< Matthew 19 >
1 And it came to pass, when Jesus finished these words, He removed from Galilee, and came to the borders of Judea, beyond the Jordan,
Sa’ad da Yesu ya gama faɗin waɗannan abubuwa, sai ya bar Galili, ya tafi yankin Yahudiya a ɗaya gefen Urdun.
2 and great multitudes followed Him, and He healed them there.
Taron mutane mai yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da su a can.
3 And the Pharisees came near to Him, tempting Him, and saying to Him, “Is it lawful for a man to put away his wife for every cause?”
Waɗansu Farisiyawa suka zo wurinsa don su gwada shi. Suka yi tambaya suka ce, “Daidai ne mutum yă saki matarsa saboda wani dalili da kuma a kan kowane dalili?”
4 And He answering said to them, “Did you not read that He who made [them] from the beginning, made them a male and a female,
Ya amsa ya ce, “Ba ku taɓa karantawa ba ne cewa, a farkon halitta, Mahalicci ‘ya yi su namiji da ta mace,’
5 and said, For this cause will a man leave father and mother, and cleave to his wife, and they will be—the two—for one flesh?
ya kuma ce, ‘Saboda wannan dalili, namiji zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa yă manne wa matarsa, biyun kuwa su zama jiki guda’?
6 So that they are no longer two, but one flesh; what therefore God joined together, let no man separate.”
Ta haka, ba sa ƙara zama biyu, sai dai ɗaya. Saboda haka abin da Allah ya haɗa fa, kada mutum yă raba.”
7 They say to Him, “Why then did Moses command to give a roll of divorce, and to put her away?”
Suka yi tambaya, suka ce, “To, me ya sa Musa ya umarta cewa mutum yă ba wa matarsa takardar saki, yă kuma kore ta?”
8 He says to them, “Moses for your stiffness of heart permitted you to put away your wives, but from the beginning it has not been so.
Yesu ya amsa ya ce, “Musa ya ba ku izini ku saki matanku saboda taurin zuciyarku ne. Amma ba haka yake ba daga farko.
9 And I say to you that whoever may put away his wife, if not for whoredom, and may marry another, commits adultery; and he who married her that has been put away, commits adultery.”
Ina faɗa muku cewa duk wanda ya saki matarsa, sai dai a kan rashin aminci a cikin aure, ya kuwa auri wata, ya yi zina ke nan.”
10 His disciples say to Him, “If the case of the man with the woman is so, it is not good to marry.”
Almajiran suka ce masa, “In haka yake tsakanin miji da mata, ashe, ya ma fi kyau kada a yi aure.”
11 And He said to them, “All do not receive this word, but those to whom it has been given;
Yesu ya ce, “Ba kowa ba ne zai yarda da wannan magana, sai dai waɗanda aka yarda musu.
12 for there are eunuchs who from the mother’s womb were so born; and there are eunuchs who were made eunuchs by men; and there are eunuchs who kept themselves eunuchs because of the kingdom of the heavens: he who is able to receive [it]—let him receive.”
Gama waɗansu bābānni ne domin haka aka haife su; waɗansu kuwa mutane ne suka mai da su haka; waɗansu kuma sun ƙi aure ne saboda mulkin sama. Duk mai iya ɗaukar wannan yă ɗauka.”
13 Then were brought near to Him children that He might put hands on them and pray, and the disciples rebuked them.
Sa’an nan aka kawo yara ƙanana wurin Yesu don yă ɗibiya musu hannuwansa, yă kuma yi musu addu’a. Amma almajirai suka tsawata wa waɗanda suka kawo su.
14 But Jesus said, “Permit the children, and do not forbid them to come to Me, for of such is the kingdom of the heavens”;
Yesu ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin sama na irin waɗannan ne.”
15 and having laid [His] hands on them, He departed from there.
Sa’ad da ya ɗibiya musu hannuwansa, sai ya tafi abinsa.
16 And behold, one having come near, said to Him, “Good Teacher, what good thing will I do that I may have continuous life?” (aiōnios )
To, fa, sai ga wani ya zo wurin Yesu ya tambaye shi ya ce, “Malam, wane abu mai kyau ne ya zama mini dole in yi don in sami rai madawwami?” (aiōnios )
17 And He said to him, “Why do you call Me good? No one [is] good except one—God; but if you will to enter into life, keep the commands.”
Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake tambayata game da abin da yake mai kyau? Akwai Mai kyau Ɗaya kaɗai. In kana so ka sami rai madawwami, ka kiyaye dokokin nan.”
18 He says to Him, “What kind?” And Jesus said, “You will not murder, You will not commit adultery, You will not steal, You will not bear false witness,
Mutumin ya yi tambaya ya ce, “Waɗanne?” Yesu ya amsa ya ce, “‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar ƙarya,
19 Honor your father and mother, and, You will love your neighbor as yourself.”
ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’ka kuma ‘ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
20 The young man says to Him, “All these I kept from my youth; what yet do I lack?”
Saurayin ya ce, “Duk waɗannan na kiyaye. Me kuma ya rage mini?”
21 Jesus said to him, “If you will to be perfect, go away, sell what you have, and give to the poor, and you will have treasure in Heaven, and come, follow Me.”
Yesu ya amsa ya ce, “In kana so ka zama cikakke, ka je, ka sayar da dukan dukiyarka ka kuma ba matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo, ka bi ni.”
22 And the young man, having heard the word, went away sorrowful, for he had many possessions;
Da saurayin ya ji haka, sai ya tafi rai a ɓace, don yana da arziki sosai.
23 and Jesus said to His disciples, “Truly I say to you that hardly will a rich man enter into the kingdom of the heavens;
Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Gaskiya nake gaya muku, yana da wuya mai arziki yă shiga mulkin sama.
24 and again I say to you, it is easier for a camel to go through the eye of a needle, than for a rich man to enter into the Kingdom of God.”
Har wa yau ina gaya muku, zai fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
25 And His disciples having heard, were exceedingly amazed, saying, “Who, then, is able to be saved?”
Sa’ad da almajiran suka ji wannan, sai suka yi mamaki ƙwarai. Suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
26 And Jesus having earnestly beheld, said to them, “With men this is impossible, but with God all things are possible.”
Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba ya yiwuwa, amma ga Allah kuwa, dukan abubuwa masu yiwuwa ne.”
27 Then Peter answering said to Him, “Behold, we left all, and followed You, what then will we have?”
Sai Bitrus ya amsa masa, “Ga shi mun bar kome don mu bi ka! Me za mu samu ke nan?”
28 And Jesus said to them, “Truly I say to you that you who followed Me, in the regeneration, when the Son of Man may sit on a throne of His glory, will sit—you also—on twelve thrones, judging the twelve tribes of Israel;
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, a lokacin sabunta dukan kome, sa’ad da Ɗan Mutum ya zauna a kan kursiyinsa mai daraja, ku da kuka bi ni, ku ma za ku zauna a kan kursiyoyi goma sha biyu, kuna yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.
29 and everyone who left houses, or brothers, or sisters, or father, or mother, or wife, or children, or fields, for My Name’s sake, will receive a hundredfold, and will inherit continuous life; (aiōnios )
Duk kuma wanda ya bar gidaje ko’yan’uwa maza ko’yan’uwa mata ko mahaifi ko mahaifiya ko yara ko gonaki, saboda ni, zai sami abin da ya fi haka riɓi ɗari, yă kuma gāji rai madawwami. (aiōnios )
30 and many first will be last, and last first.”
Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, da yawa kuma da suke na ƙarshe, za su zama na farko.