< Matthew 18 >

1 At that hour the disciples came near to Jesus, saying, “Who, now, is greater in the kingdom of the heavens?”
Daidai wannan lokacin, almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, ''Wanene mafi girma a mulkin sama?''
2 And Jesus having called near a child, set him in the midst of them,
Sai Yesu ya kira karamin yaro gunsa, ya sa shi a tsakaninsu,
3 and said, “Truly I say to you, if you may not be turned and become as the children, you may not enter into the kingdom of the heavens;
ya ce, ''Hakika ina gaya maku, idan baku juya kun zama kamar kananan yara ba, babu yadda zaku shiga mulkin sama.
4 whoever then may humble himself as this child, he is the greater in the kingdom of the heavens.
Saboda haka, duk wanda ya kaskantar da kansa kamar karamin yaron nan, shi ne mafi girma a mulkin sama.
5 And he who may receive one such child in My Name, receives Me,
Duk wanda ya karbi karamin yaro a suna na, ya karbe ni.
6 and whoever may cause to stumble one of those little ones who are believing in Me, it is better for him that a weighty millstone may be hanged on his neck, and he may be sunk in the depth of the sea.
Amma duk wanda ya sa daya daga cikin 'yan yaran nan da suka gaskanta da ni zunubi, gwamma a rataya dutsen nika a wuyansa a jefa shi cikin zurfin teku.
7 Woe to the world from the stumbling-blocks! For there is necessity for the stumbling-blocks to come, but woe to that man through whom the stumbling-block comes!
Kaiton duniya saboda lokacin tuntube! Lallai ne wadannan lokuta su zo, amma kaiton mutumin da ta wurinsa ne wadannan lokutan za su zo!
8 And if your hand or your foot causes you to stumble, cut them off and cast [them] from you; it is good for you to enter into life lame or maimed, rather than having two hands or two feet, to be cast into the continuous fire. (aiōnios g166)
Idan hannunka ko kafarka ce za ta sa ka tuntube, ka yanke ta, ka yar daga gare ka. Zai fi maka kyau ka shiga rai da nakasa ko gurguntaka, da a jefa ka cikin madawwamiyar wuta tare da hannayenka ko kafafunka. (aiōnios g166)
9 And if your eye causes you to stumble, pluck it out and cast from you; it is good for you to enter into life one-eyed, rather than having two eyes to be cast into the Gehenna of fire. (Geenna g1067)
Idan idonka zai sa ka tuntube, ka kwakule shi, ka yar. Zai fi maka kyau ka shiga rai da ido daya, da a jefa ka cikin madawwamiyar wuta da idanu biyu. (Geenna g1067)
10 Beware! You may not despise one of these little ones, for I say to you that their messengers in the heavens always behold the face of My Father who is in the heavens,
Ku kula fa kada ku rena kananan nan. Domin koyaushe a sama, mala'ikunsu na duban fuskar Ubana da ke sama.
11 [[for the Son of Man came to save the lost.]]
[Dan Mutum ya zo ya ceci abinda ya bata].
12 What do you think? If a man may have one hundred sheep, and there may go astray one of them, does he not—having left the ninety-nine, having gone on the mountains—seek that which is gone astray?
Menene tunaninku? Idan mutum na da tumaki dari, sa'annan daya ta bata, ashe ba zai bar tassa'in da tara a gefen tudu ya tafi neman wadda ta bata ba?
13 And if it may come to pass that he finds it, truly I say to you that he rejoices over it more than over the ninety-nine that have not gone astray;
In ya same ta, hakika ina gaya maku, farin cikinsa na samun dayan nan da ta bace, zai fi na tassa'in da taran nan da basu bata ba.
14 so it is not [the] will in [the] presence of your Father who is in the heavens that one of these little ones may perish.
Hakanan fa, ba nufin Ubanku dake sama ba ne da ya daga cikin wadannan kananan ya hallaka.
15 And if your brother may sin against you, go and show him his fault between you and him alone, if he may hear you, you gained your brother;
Idan dan'uwanka yayi maka laifi, fada masa tsakaninku, kai da shi kadai. Idan ya saurare ka, ka maido da dan'uwanka kenan.
16 and if he may not hear, take with you yet one or two, that by the mouth of two witnesses or three every word may stand.
Amma in ya ki ya saurare ka, ka je da 'yan'uwa biyu ko uku su zama shaidu, don ta wurin shaidu biyu ko uku ake tabbatar da kowacce kalma.
17 And if he may not hear them, say [it] to the assembly, and if also the assembly he may not hear, let him be to you as the heathen man and the tax collector.
In kuma ya ki ya saurare su, ka kai lamarin ga ikklisiya. Idan ya ki ya saurari ikklisiya, ka maishe shi ba'al'umme da mai karbar haraji.
18 Truly I say to you, whatever things you may bind on the earth will be having been bound in the heavens, and whatever things you may loose on the earth will be having been loosed in the heavens.
Hakika ina gaya maku, duk abin da kuka daure a duniya, a daure yake a sama. Abin da kuka kwance kuma, a kwance yake a sama.
19 Again, I say to you that if two of you may agree on the earth concerning anything, whatever they may ask—it will be done to them from My Father who is in the heavens,
Kuma ina gaya maku, idan mutum ku biyu zaku yarda akan duk abin da zaku roka, Ubana wanda ke a sama zai yi maku shi.
20 for where there are two or three gathered together—to My Name, there am I in the midst of them.”
Wurin da mutum biyu ko uku suka taru a cikin sunana, zan kasance tare da su.''
21 Then Peter having come near to Him, said, “Lord, how often will my brother sin against me, and I forgive him—until seven times?”
Bitrus ya zo ya ce wa Yesu, ''Ubangiji, sau nawa ne dan'uwana zai yi mani laifi in gafarta masa? Har sai ya kai sau bakwai?''
22 Jesus says to him, “I do not say to you until seven times, but until seventy times seven.
Yesu ya amsa ya ce masa, ''Ban gaya maka sau bakwai ba, amma bakwai din ma har sau saba'in.
23 Because of this was the kingdom of the heavens likened to a man, a king, who willed to take reckoning with his servants,
Saboda haka, za a kwatanta mulkin sama da wani sarki da yake so ya lisafta dukiyarsa dake a hannun barorinsa.
24 and he having begun to take account, there was brought near to him one debtor of a myriad of talents,
Da ya fara yin haka, sai aka kawo masa daya daga cikin barorinsa da yake binsa talanti dubu goma.
25 and he having nothing to pay, his lord commanded him to be sold, and his wife, and the children, and all, whatever he had, and payment to be made.
Amma tunda ba shi da abin biya, ubangidansa ya bada umurni a sayar da shi, tare da matarsa da 'ya'yansa da duk mallakarsa, domin a biya.
26 The servant then, having fallen down, was prostrating to him, saying, Lord, have patience with me, and I will pay you all;
Sai baran ya fadi kasa, ya rusuna a gaban ubangidansa ya ce, “Maigida, kayi mani hakuri, zan biya duk abin da na karba.”
27 and the lord of that servant having been moved with compassion released him, and the debt he forgave him.
Don haka ubangidansa yayi juyayi, sai ya ce, ya yafe bashin, a saki baran.
28 And that servant having come forth, found one of his fellow-servants who was owing him one hundred denarii, and having laid hold, he took him by the throat, saying, Pay me that which you owe.
Amma bayan an saki wannan baran, ya je ya sami wani baran kamar sa da yake bi bashin dinari dari. Ya cafke shi, ya shake shi a wuya, ya ce, 'Ka biya bashin da nake bin ka.'
29 His fellow-servant then, having fallen down at his feet, was calling on him, saying, Have patience with me, and I will pay you all;
Amma dan'uwansa bara ya roke shi ya ce, kayi mani hakuri, zan biya ka duk abinda na karba.'
30 and he would not, but having gone away, he cast him into prison, until he might pay that which was owing.
Amma baran nan na farko ya ki. A maimakon haka, ya sa aka jefa dan'uwansa bara a kurkuku sai ya biya bashin nan.
31 And his fellow-servants having seen the things that were done, were grieved exceedingly, and having come, showed fully to their lord all the things that were done;
Da sauran barori suka ga abin da ya faru, suka damu kwarai. Sai suka je suka fada wa ubangidansu yadda abin ya faru duka.
32 then having called him, his lord says to him, Evil servant! All that debt I forgave you, seeing you called on me;
Sai ubangidansa ya kirawo shi, ya ce masa, ''Kai mugun bawa, na gafarta maka bashin nan duka, domin ka roke ni.
33 did it not seem necessary to you to have dealt kindly with your fellow servant, as I also dealt kindly with you?
Ashe, bai kamata kaima ka nuna jinkai ga dan'uwanka bara kamar yadda na nuna maka jinkai ba?'
34 And having been angry, his lord delivered him to the inquisitors, until he might pay all that was owing to him;
Ubangidansa yayi fushi, ya danka shi ga masu azabtarwa, har sai ya gama biyan dukan bashin da ake binsa.
35 so also My heavenly Father will do to you, if you may not forgive each one his brother from your hearts their trespasses.”
Hakanan Ubana dake a sama zai yi maku, idan kowannenku bai gafarta wa dan'uwansa daga zuciya ba.''

< Matthew 18 >