< Matthew 16 >
1 And the Pharisees and Sadducees having come, tempting, questioned Him, to show to them a sign from Heaven,
Sai Farisawa da Sadukiyawa suka zo su gwada shi suka roke shi ya nuna masu alama daga sama.
2 and He answering said to them, “Evening having come, you say, Fair weather, for the sky is red,
Amma ya amsa ya ce masu, “Lokacin da yamma ta yi, sai ku ce, 'Za a yi yanayi mai kyau, domin sama ta yi ja,'
3 and at morning, Foul weather today, for the sky is red—gloomy; hypocrites, you indeed know to discern the face of the sky, but the signs of the times you are not able!
Kuma da safe ku ce, 'Zai zama yanayi mara kyau a yau, domin sama ta yi ja ta kuma gama gari, kun san yadda za ku bayyana kammanin sararin sama, amma ba ku iya bayyana alamun lokaci ba.
4 An evil and adulterous generation seeks a sign, and a sign will not be given to it, except the sign of Jonah the prophet”; and having left them He went away.
Mugun zamani, maciya amana suna neman alama, amma babu wata alama da za a nuna sai ta Yunusa.” Daga nan sai Yesu ya tafi.
5 And His disciples having come to the other side, forgot to take loaves,
Almajiran suka zo daga wancan gefe, amma sun manta su dauki gurasa,
6 and Jesus said to them, “Beware, and take heed of the leaven of the Pharisees and Sadducees”;
Yesu ya ce masu, “Ku kula ku kuma mai da hankali da yisti na Farisawa da Sadukiyawa.”
7 and they were reasoning in themselves, saying, “Because we took no loaves.”
Sai almajiran suka fara magana da junansu suka ce, “Ko saboda bamu kawo gurasa bane.”
8 And Jesus having known, said to them, “Why reason you in yourselves, you of little faith, because you took no loaves?
Yesu yana sane da wannan sai ya ce, “Ku masu karancin bangaskiya, don me ku ke magana a tsakaninku cewa ko don bamu kawo gurasa bane?
9 Do you not yet understand, nor remember the five loaves of the five thousand, and how many hand-baskets you took up?
Ba ku gane ko tuna da gurasa guda biyar da aka ciyar da mutum dubu biyar, kuma kwando nawa kuka tara ba?
10 Nor the seven loaves of the four thousand, and how many baskets you took up?
Ko gurasa bakwai ga mutum dubu hudu, da kuma kwanduna nawa kuka dauka ba?
11 How do you not understand that I did not speak to you of bread—to take heed of the leaven of the Pharisees and Sadducees?”
Yaya kuka kasa fahimta cewa ba game da gurasa nake yi maku magana ba? Ku yi hankali ku kuma lura da yistin Farisawa da Sadukiyawa.”
12 Then they understood that He did not say to take heed of the leaven of the bread, but of the teaching of the Pharisees and Sadducees.
Sa'annan suka fahimta cewa ba yana gaya masu su yi hankali da yistin da ke cikin gurasa ba ne, amma sai dai su yi lura da koyarwar Farisawa da Sadukiyawa.
13 And Jesus, having come to the parts of Caesarea Philippi, was asking His disciples, saying, “Who do men say I am—the Son of Man?”
A lokacin da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, ya tambayi almajiransa, cewa, “Wa mutane ke cewa Dan Mutum yake?
14 And they said, “Some, John the Immerser, and others, Elijah, and others, Jeremiah, or one of the prophets.”
Suka ce, “Wadansu suna cewa Yahaya mai baftisma; wadansu Iliya, saura suna cewa Irmiya, ko daya daga cikin annabawa.”
15 He says to them, “And you—who do you say I am?”
Ya ce masu, “Amma ku wa kuke ce da ni?”
16 And Simon Peter answering said, “You are the Christ, the Son of the living God.”
Sai Saminu Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Almasihu, Dan Allah mai rai.”
17 And Jesus answering said to him, “Blessed are you, Simon Bar-Jona, because flesh and blood did not reveal [it] to you, but My Father who is in the heavens.
Yesu ya amsa ya ce masa, “Mai albarka ne kai, Saminu dan Yunusa, don ba nama da jini ba ne ya bayyana maka wannan, amma Ubana wanda ke cikin sama.
18 And I also say to you that you are Peter, and on this rock I will build My Assembly, and [the] gates of Hades will not prevail against it; (Hadēs )
Ina kuma gaya maka cewa kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikilisiya ta. Kofofin hades ba za su yi nasara da ita ba. (Hadēs )
19 and I will give to you the keys of the kingdom of the heavens, and whatever you may bind on the earth will be having been bound in the heavens, and whatever you may loose on the earth will be having been loosed in the heavens.”
Zan ba ka mabudan mulkin sama. Duk abin da ka kulla a duniya zai zama abin da an kulla a cikin sama, kuma duk abinda ka warware a duniya a warware yake cikin sama,”
20 Then He charged His disciples that they may say to no one that He is Jesus the Christ.
Sai Yesu ya umarci almajiransa kada su gaya wa kowa cewa shi ne Almasihu.
21 From that time Jesus began to show to His disciples that it is necessary for Him to go away to Jerusalem, and to suffer many things from the elders, and chief priests, and scribes, and to be put to death, and the third day to rise.
Daga lokacin nan Yesu ya fara gaya wa almajiransa cewa dole ne ya tafi Urushalima, ya sha wahala mai yawa a hannun dattawa, da manyan firistoci da malaman attaura, a kashe shi, a tashe shi zuwa rai a rana ta uku.
22 And having taken Him aside, Peter began to rebuke Him, saying, “Be kind to Yourself, Lord; this will not be to You”;
Sai Bitrus ya kai shi a gefe ya tsauta masa, cewa, “Wannan ya yi nesa da kai, Ubangiji; wannan ba zai taba faruwa da kai ba.”
23 and He having turned, said to Peter, “Get behind Me, Satan! You are a stumbling-block to Me, for you do not mind the things of God, but the things of men.”
Amma Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Ka koma bayana, Shaidan! Kai sanadin tuntube ne gare ni, domin ba ka damuwa da abubuwan da suke na Allah, amma sai abubuwan mutane.”
24 Then Jesus said to His disciples, “If anyone wills to come after Me, let him disown himself, and take up his cross, and follow Me,
Sa'annan Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk wanda yake so ya bi ni, lallai ne ya ki kansa, ya dauki gicciyensa, ya bi ni.
25 for whoever may will to save his life will lose it, and whoever may lose his life for My sake will find it;
Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi. Duk wanda ya rasa ransa domina zai same shi.
26 for what is a man profited if he may gain the whole world, but of his life suffer loss? Or what will a man give as an exchange for his life?
Domin wace riba mutum zai samu in ya sami dukan duniya ya rasa ransa? Me mutum zai iya bayarwa a maimakon ransa?
27 For the Son of Man is about to come in the glory of His Father, with His messengers, and then He will reward each according to his work.
Domin Dan Mutum zai zo ne cikin daukakar Ubansa tare da mala'ikunsa. Sa'annan ne zaya biya kowane mutum bisa ga ayyukansa.
28 Truly I say to you, there are certain of those standing here who will not taste of death until they may see the Son of Man coming in His kingdom.”
Gaskiya ina gaya maku, akwai wadansun ku da ke tsaye a nan, da ba za su dandana mutuwa ba sai sun ga Dan Mutum na zuwa cikin mulkinsa.”