< Mark 9 >

1 And He said to them, “Truly I say to you that there are certain of those standing here, who may not taste of death until they see the Kingdom of God having come in power.”
Ya kuma ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, waɗansu da suke tsattsaye a nan ba za su mutu ba, sai sun ga mulkin Allah ya bayyana da iko.”
2 And after six days Jesus takes Peter, and James, and John, and brings them up to a high mountain by themselves, alone, and He was transfigured before them,
Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna tare da shi, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, suka kasance su kaɗai a wurin. A can aka sāke kamanninsa a gabansu.
3 and His garments became glittering, exceedingly white, as snow, so as a launderer on the earth is not able to whiten [them].
Tufafinsa suka zama fari suna ƙyalli, fiye da yadda wani a duniya zai iya yi su.
4 And there appeared to them Elijah with Moses, and they were talking with Jesus.
Iliya da Musa suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
5 And Peter answering says to Jesus, “Rabbi, it is good to us to be here; and we may make three shelters, for You one, and for Moses one, and for Elijah one”:
Bitrus ya ce wa Yesu, “Rabbi, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
6 for he was not knowing what he might say, for they were greatly afraid.
(Bai san abin da zai faɗa ba ne, gama sun tsorata ƙwarai.)
7 And there came a cloud overshadowing them, and there came a voice out of the cloud, saying, “This is My Son, the Beloved, hear Him”;
Sai wani girgije ya bayyana, ya rufe su, wata murya kuma ta fito daga girgijen, ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna, ku saurare shi!”
8 and suddenly, having looked around, they saw no one anymore, but Jesus only with themselves.
Farat ɗaya, da suka waiwaya, ba su ƙara ganin kowa tare da su ba, sai dai Yesu.
9 And as they are coming down from the mountain, He charged them that they may declare to no one the things that they saw, except when the Son of Man may rise out of the dead;
Da suna saukowa daga dutsen, Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa abin da suka gani, sai bayan Ɗan Mutum ya tashi daga matattu.
10 and the thing they kept to themselves, questioning together what the rising out of the dead is.
Suka riƙe wannan zance a ɓoye tsakaninsu, suna tattaunawa ko mece ce ma’anar “tashi daga matattu.”
11 And they were questioning Him, saying that the scribes say that Elijah must come first.
Suka tambaye shi, suka ce, “Don me malaman dokoki suke cewa, sai Iliya ya fara zuwa?”
12 And He answering said to them, “Elijah indeed, having come first, restores all things; and how has it been written concerning the Son of Man, that He may suffer many things, and be set at nothing?
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya ne, Iliya zai zo da fari, yă kuma mayar da dukan abubuwa. Don me kuma aka rubuta cewa, dole Ɗan Mutum yă sha wahala sosai, kuma a ƙi shi?
13 But I say to you that also Elijah has come, and they did to him what they willed, as it has been written of him.”
Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, kuma suka yi duk abin da suka ga dama da shi, kamar yadda aka rubuta game da shi.”
14 And having come to the disciples, He saw a great multitude around them, and scribes questioning with them,
Da suka dawo wurin sauran almajiran, sai suka ga babban taro kewaye da su, malaman dokoki suna gardama da su.
15 and immediately, all the multitude having seen Him, were amazed, and running near, were greeting Him.
Nan take da dukan mutanen suka ga Yesu, sai suka cika da mamaki, suka ruga da gudu don su gai da shi.
16 And He questioned the scribes, “What do you dispute with them?”
Ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi da su?”
17 And one out of the multitude answering said, “Teacher, I brought my son to You, having a mute spirit;
Wani mutum a cikin taron ya amsa ya ce, “Malam, na kawo maka ɗana mai wani ruhun da yake hana shi magana.
18 and wherever it seizes him, it tears him, and he foams, and gnashes his teeth, and pines away; and I spoke to Your disciples that they may cast it out, and they were not able.”
Duk lokacin da mugun ruhun ya kama shi, yakan jefa shi a ƙasa. Bakinsa yakan yi kumfa, yă cije haƙorarsa, yakan sa jikinsa ya sandare, yă zama da ƙarfi. Na roƙi almajiranka su fitar da ruhun, amma ba su iya ba.”
19 And He answering him, said, “O generation unbelieving, until when will I be with you? Until when will I suffer you? Bring him to Me”;
Yesu ya ce, “Ya ku zamani marar bangaskiya, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron.”
20 and they brought him to Him, and he having seen Him, immediately the spirit convulsed him, and he, having fallen on the earth, was wallowing—foaming.
Sai suka kawo shi. Da ruhun ya ga Yesu, nan da nan sai ya buge yaron da farfaɗiya. Ya fāɗi a ƙasa, yana birgima, bakinsa yana kumfa.
21 And He questioned his father, “How much time is it since this came to him?” And he said, “From childhood,
Yesu ya tambayi mahaifin yaron ya ce, “Tun yaushe yake haka?” Ya ce, “Tun yana ƙarami.
22 and many times it also cast him into fire, and into water, that it might destroy him; but if You are able to do anything, help us, having compassion on us.”
Ya sha jefa shi cikin wuta, ko ruwa don yă kashe shi. Amma in za ka iya yin wani abu, ka ji tausayinmu ka taimake mu.”
23 And Jesus said to him, “If you are able to believe! All things are possible to the one that is believing”;
Yesu ya ce, “‘In za ka iya’? Ai, kome mai yiwuwa ne ga wanda ya gaskata.”
24 and immediately the father of the child, having cried out with tears, said, “I believe, Lord; be helping my unbelief.”
Nan da nan mahaifin yaron ya faɗa da ƙarfi ya ce, “Na gaskata, ka taimake ni in sha kan rashin bangaskiyata!”
25 Jesus having seen that a multitude runs together, rebuked the unclean spirit, saying to it, “Spirit—mute and deaf—I charge you, come forth out of him, and you may no longer enter into him”;
Da Yesu ya ga taron suna zuwa can a guje, sai ya tsawata wa mugun ruhun ya ce, “Kai ruhun kurma, da na bebe, na umarce ka, ka fita daga cikinsa, kada kuma ka ƙara shigarsa.”
26 and having cried, and convulsed him much, it came forth, and he became as dead, so that many said that he was dead,
Sai ruhun ya yi ihu, ya buge shi da ƙarfi da farfaɗiya, ya fita. Yaron ya kwanta kamar matacce, har mutane da yawa suka ce, “Ai, ya mutu.”
27 but Jesus, having taken him by the hand, lifted him up, and he arose.
Amma Yesu ya kama shi a hannu ya ɗaga, ya kuwa tashi tsaye.
28 And He having come into the house, His disciples were questioning Him by Himself, “Why were we not able to cast it forth?”
Da Yesu ya shiga gida, almajiransa suka tambaye shi a ɓoye, suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da shi ba?”
29 And He said to them, “This kind is able to come forth with nothing except with prayer and fasting.”
Ya amsa ya ce, “Sai da addu’akaɗai irin wannan yakan fita.”
30 And having gone forth there, they were passing through Galilee, and He did not wish that any may know,
Suka bar wurin suka bi ta Galili. Yesu bai so wani yă san inda suke ba,
31 for He was teaching His disciples, and He said to them, “The Son of Man is being delivered into the hands of men, and they will kill Him, and having been killed, the third day He will rise,”
gama yana koya wa almajiransa. Ya ce musu, “Za a ci amanar Ɗan Mutum, a ba da shi ga hannun mutane. Za su kashe shi, bayan kwana uku kuma zai tashi.”
32 but they were not understanding the saying, and they were afraid to question Him.
Amma ba su fahimci abin da yake nufi ba, suka kuma ji tsoro su tambaye shi game da wannan.
33 And He came to Capernaum, and being in the house, He was questioning them, “What were you reasoning in the way among yourselves?”
Suka iso Kafarnahum. Da yana cikin gida, sai ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi a hanya?”
34 And they were silent, for they reasoned with one another in the way who is greater;
Amma suka yi shiru, don a hanya suna gardama ne, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma?
35 and having sat down He called the Twelve, and He says to them, “If any wills to be first, he will be last of all, and minister of all.”
Da Yesu ya zauna, sai ya kira Sha Biyun ya ce, “In wani yana so yă zama na fari, dole yă zama na ƙarshe duka, da kuma bawan kowa.”
36 And having taken a child, He set him in the midst of them, and having taken him in His arms, said to them,
Ya ɗauki wani ƙaramin yaro ya sa yă tsaya a tsakiyarsu. Ya ɗauke shi a hannunsa, ya ce musu,
37 “Whoever may receive one of such children in My Name, receives Me, and whoever may receive Me, does not receive Me, but Him who sent Me.”
“Duk wanda ya karɓi ɗaya daga cikin waɗannan ƙananan yara a cikin sunana, ni ya karɓa. Duk wanda kuma ya karɓe ni, ba ni ya karɓa ba, amma wanda ya aiko ni ne ya karɓa.”
38 And John answered Him, saying, “Teacher, we saw a certain one casting out demons in Your Name, who does not follow us, and we forbade him, because he does not follow us.”
Yohanna ya ce, “Malam mun ga wani mutum yana fitar da aljanu a cikin sunanka, sai muka ce yă daina, domin shi ba ɗaya daga cikinmu ba ne.”
39 And Jesus said, “Do not forbid him, for there is no one who will do a mighty work in My Name, and will be readily able to speak evil of Me:
Yesu ya ce, “Kada ku hana shi. Ba wanda yake yin ayyukan banmamaki a cikin sunana, nan take yă faɗi wani abu mummuna game da ni.
40 for he who is not against us is for us;
Gama duk wanda ba ya gāba da mu, namu ne.
41 for whoever may give you to drink a cup of water in My Name, because you are Christ’s, truly I say to you, he may not lose his reward;
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ba ku ruwan sha a sunana, saboda ku na Kiristi ne, lalle, ba zai rasa ladarsa ba.
42 and whoever may cause to stumble one of the little ones believing in Me, better is it for him if a millstone is hanged around his neck, and he has been cast into the sea.
“Idan kuma wani yă sa ɗaya daga cikin waɗannan’yan yara masu gaskatawa da ni yă yi laifi, zai fiye masa a rataya wani babban dutsen niƙa a wuyarsa, a jefa shi cikin teku.
43 And if your hand may cause you to stumble, cut it off; it is better for you to enter into life maimed, than having the two hands, to go away into Gehenna, into the fire—the unquenchable— (Geenna g1067)
In hannunka yana sa ka yin zunubi, yanke shi. Ai, gwamma ka shiga rai da hannu ɗaya, da ka shiga jahannama ta wuta, inda ba a iya kashe wutar ba, da hannuwanka biyu. (Geenna g1067)
44 [[where their worm is not dying, and the fire is not being quenched.]]
45 And if your foot may cause you to stumble, cut it off; it is better for you to enter into life lame, than having the two feet to be cast into Gehenna, into the fire—the unquenchable— (Geenna g1067)
In kuma ƙafarka tana sa ka yin zunubi, yanke ta. Ai, gwamma ka shiga rai da ƙafa ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da ƙafafunka biyu. (Geenna g1067)
46 [[where their worm is not dying, and the fire is not being quenched.]]
47 And if your eye may cause you to stumble, cast it out; it is better for you to enter into the Kingdom of God one-eyed, than having two eyes, to be cast into the Gehenna of fire— (Geenna g1067)
In kuma idonka yana sa ka zunubi, ƙwaƙule shi. Ai, gwamma ka shiga mulkin Allah da ido ɗaya, da a jefa ka cikin jahannama ta wuta, da idanu biyu, (Geenna g1067)
48 where their worm is not dying, and the fire is not being quenched;
inda “‘tsutsotsinsu ba sa mutuwa, wutar kuma ba a iya kashewa.’
49 for everyone will be salted with fire, and every sacrifice will be salted with salt.
Za a tsarkake kowa da wuta.
50 The salt [is] good, but if the salt may become saltless, in what will you season [it]? Have in yourselves salt, and have peace in one another.”
“Gishiri yana da daɗi, amma in ya rabu da ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da ɗanɗanonsa? Ku kasance da gishiri a cikinku, ku kuma yi zauna lafiya da juna.”

< Mark 9 >