< Mark 2 >

1 And again He entered into Capernaum, after [some] days, and it was heard that He is in the house,
Bayan’yan kwanaki, da Yesu ya sāke shiga Kafarnahum, sai mutane suka ji labarin zuwansa gida.
2 and immediately many were gathered together, so that there was no more room, not even at the door, and He was speaking to them the word.
Mutane suka taru da yawa har ma babu wuri, ko a bakin ƙofa ma, sai ya yi musu wa’azin bishara.
3 And they come to Him, bringing a paralytic, carried by four,
Waɗansu mutum huɗu suka zo wajensa ɗauke da wani shanyayye.
4 and not being able to come near to Him because of the multitude, they uncovered the roof where He was, and having broken [it] up, they let down the pallet on which the paralytic was lying,
Da ba su iya kai shi wurin Yesu ba, saboda taron, sai suka buɗe rufin gidan saman, bisa daidai inda Yesu yake. Bayan da suka huda rami, sai suka saukar da shanyayyen, kwance a kan tabarmarsa.
5 and Jesus having seen their faith, says to the paralytic, “Child, your sins have been forgiven you.”
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, “Saurayi, an gafarta zunubanka.”
6 And there were certain of the scribes sitting there, and reasoning in their hearts,
To, waɗansu malaman dokoki da suke zaune a wurin, suka yi tunani a zuciyarsu, suna cewa,
7 “Why does this One thus speak evil words? Who is able to forgive sins except one—God?”
“Me ya sa mutumin nan yake magana haka? Yana saɓo! Wane ne zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
8 And immediately Jesus, having known in His spirit that they thus reason in themselves, said to them, “Why do you reason these things in your hearts?
Nan da nan, Yesu ya gane a ruhunsa abin da suke tunani a zuciyarsu, sai ya ce musu, “Me ya sa kuke tunanin waɗannan abubuwa?
9 Which is easier? To say to the paralytic, Your sins are forgiven; or to say, Rise, and take up your pallet, and walk?
Wanne ya fi sauƙi, a ce wa shanyayyen, ‘An gafarta zunubanka,’ ko a ce, ‘Tashi, ɗauki tabarmarka ka yi tafiya’?
10 And that you may know that the Son of Man has authority on the earth to forgive sins—(He says to the paralytic)—
Amma don ku san cewa, Ɗan Mutum yana da iko a duniya yă gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen,
11 I say to you, rise, and take up your pallet, and go away to your house”;
“Ina ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka, ka tafi gida.”
12 and he rose immediately, and having taken up the pallet, he went forth before all, so that all were astonished, and glorify God, saying, “Never thus did we see.”
Sai ya tashi, ya ɗauki tabarmarsa, ya yi tafiyarsa a gabansu duka. Wannan ya ba wa kowa mamaki, suka kuma ɗaukaka Allah suna cewa, “Ba mu taɓa ganin abu haka ba!”
13 And He went forth again by the sea, and all the multitude was coming to Him, and He was teaching them,
Yesu ya sāke tafiya bakin tafkin. Taro mai yawa ya zo wurinsa, sai ya fara koya musu.
14 and passing by, He saw Levi of Alpheus sitting at the tax office, and says to him, “Follow Me,” and he, having risen, followed Him.
Yana cikin tafiya, sai ya ga Lawi, ɗan Alfayus zaune a inda ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.” Sai Lawi ya tashi, ya bi shi.
15 And it came to pass, in His reclining in his house, that many tax collectors and sinners were dining with Jesus and His disciples, for there were many, and they followed Him.
Yayinda Yesu yake cin abinci a gidan Lawi, sai masu karɓar haraji da “masu zunubi” da yawa, suka zo suka ci tare da shi da almajiransa, gama akwai mutane da yawa da suka bi shi.
16 And the scribes and the Pharisees, having seen Him eating with the tax collectors and sinners, said to His disciples, “Why—that with the tax collectors and sinners He eats and drinks?”
Da malaman dokoki, waɗanda su ma Farisiyawa ne, suka ga yana ci tare da masu “zunubi” da masu karɓar haraji, sai suka tambayi almajiransa, suka ce, “Me ya sa yake ci tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
17 And Jesus, having heard, says to them, “They who are strong have no need of a physician, but they who are ill; I did not come to call righteous men, but sinners.”
Da jin wannan, Yesu ya ce musu, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya. Ban zo domin in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi.”
18 And the disciples of John and those of the Pharisees were fasting, and they come and say to Him, “Why do the disciples of John and those of the Pharisees fast, and Your disciples do not fast?”
To, almajiran Yohanna da na Farisiyawa suna azumi, sai waɗansu mutane suka zo suka tambayi Yesu, suka ce, “Yaya almajiran Yohanna da na Farisiyawa suna azumi, amma almajiranka ba sa yi?”
19 And Jesus said to them, “Are the sons of the bride-chamber able, while the bridegroom is with them, to fast? As long a time [as] they have the bridegroom with them they are not able to fast;
Yesu ya amsa ya ce, “Yaya abokan ango za su yi azumi, sa’ad da yana tare da su? Ai, ba za su yi ba, muddin yana tare da su.
20 but days will come when the bridegroom may be taken from them, and then they will fast—in those days.
Ai, lokaci yana zuwa da za a ɗauke musu angon. A sa’an nan ne fa za su yi azumi.
21 And no one sews a patch of undressed cloth on an old garment, and if not—the new, filling it up, takes from the old and the split becomes worse;
“Ba mai facin sabon ƙyalle a tsohuwar riga. In ya yi haka, sabon ƙyallen zai yage daga tsohuwar, yagewar kuwa za tă zama da muni.
22 and no one puts new wine into old skins, and if not—the new wine bursts the skins, and the wine is poured out, and the skins will be destroyed; but new wine is to be put into new skins.”
Ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a tsofaffin salkuna. In ya yi haka, ruwan inabin zai farfashe salkunan, yă yi hasarar ruwan inabin, salkunan kuma su lalace. A’a, yakan zuba sabon ruwan inabin a sababbin salkuna.”
23 And it came to pass—He is going along on the Sabbaths through the grainfields—and His disciples began to make a way, plucking the ears,
Wata ranar Asabbaci, Yesu yana ratsa gonakin hatsi, sai almajiransa da suke tafiya tare da shi, suka fara kakkarya waɗansu kan hatsi.
24 and the Pharisees said to Him, “Behold, why do they do on the Sabbaths that which is not lawful?”
Farisiyawa suka ce masa, “Duba, me ya sa suke yin abin da doka ta hana a yi, a ranar Asabbaci?”
25 And He said to them, “Did you never read what David did when he had need and was hungry, he and those with him?
Ya amsa ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi ba, sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa, suna kuma cikin bukata?
26 How he went into the house of God, in [the days of] Abiathar the chief priest, and ate the Bread of the Presentation, which it is not lawful to eat, except to the priests, and he also gave to those who were with him?”
Ya shiga gidan Allah a zamanin Abiyatar babban firist, ya ci keɓaɓɓen burodin nan, ya kuma ba wa abokan tafiyarsa abin da firistoci kaɗai sukan ci bisa ga doka?”
27 And He said to them, “The Sabbath was made for man, not man for the Sabbath,
Sai ya ce musu, “An yi Asabbaci saboda mutum ne, ba mutum saboda Asabbaci ba.
28 so that the Son of Man is also Lord of the Sabbath.”
Don haka, Ɗan Mutum Ubangiji ne, har ma da na Asabbaci.”

< Mark 2 >