< Mark 16 >

1 And the Sabbath having past, Mary the Magdalene, and Mary of James, and Salome, bought spices, that having come, they may anoint Him,
Da Asabbaci ya wuce, sai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub, da kuma Salome suka sayi kayan ƙanshi domin su je su shafa wa jikin Yesu.
2 and early in the morning of the first [day] of the weeks, they come to the tomb, at the rising of the sun,
A ranar farko ta mako, da sassafe, bayan fitowar rana, suna kan hanyarsu zuwa kabarin ke nan,
3 and they said among themselves, “Who will roll away the stone out of the door of the tomb for us?”
sai suka tambaye juna suka ce, “Wane ne zai gungura mana dutsen daga bakin kabarin?”
4 And having looked, they see that the stone has been rolled away—for it was very great,
Amma da suka ɗaga kai, sai suka ga cewa, an riga an gungura dutsen. Dutsen kuwa babba ne.
5 and having entered into the tomb, they saw a young man sitting on the right hand, clothed in a long white robe, and they were amazed.
Da suna shiga cikin kabarin, sai suka ga wani saurayi sanye da farar riga, yana zaune a hannun dama, sai suka firgita.
6 And he says to them, “Do not be amazed, you seek Jesus the Nazarene, the crucified [One]: He rose—He is not here; behold the place where they laid Him!
Ya ce, “Kada ku firgita. Kuna neman Yesu Banazare wanda aka gicciye ne. Ya tashi! Ba ya nan. Ku dubi inda aka kwantar da shi.
7 And go, say to His disciples and Peter that He goes before you to Galilee; there you will see Him, as He said to you.”
Amma ku tafi ku gaya wa almajiransa da kuma Bitrus cewa, ‘Ya sha gabanku zuwa Galili. Can za ku gan shi, kamar yadda ya faɗa muku.’”
8 And having come forth quickly, they fled from the tomb, and trembling and amazement had seized them, and they said to no one anything, for they were afraid. [[
Da rawan jiki da kuma ruɗewa, matan suka fita a guje daga kabarin. Ba su kuwa gaya wa kowa ba, don suna tsoro.
9 (note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) And He, having risen in the morning of the first of the week, appeared first to Mary the Magdalene, out of whom He had cast seven demons;
(note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Da Yesu ya tashi daga matattu da safe, a ranar farko ta mako, ya fara bayyana ga Maryamu Magdalin, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta.
10 she having gone, told those who had been with Him, mourning and weeping;
Ta je ta gaya wa waɗanda dā suke tare da shi, waɗanda kuma suke makoki da kuka.
11 and they, having heard that He is alive, and was seen by her, did not believe.
Da suka ji cewa Yesu yana da rai, har ma ta gan shi, ba su gaskata ba.
12 And after these things, to two of them, as they are going into a field, walking, He appeared in another form,
Daga baya Yesu ya bayyana a wani kamanni dabam ga biyunsu, yayinda suke tafiya ƙauye.
13 and they having gone, told [it] to the rest; not even them did they believe.
Waɗannan kuwa suka koma suka shaida wa sauran, amma su ma ba su gaskata ba.
14 Afterward, as they are reclining, He appeared to the Eleven, and reproached their unbelief and stiffness of heart, because they did not believe those having seen Him being raised;
Bayan haka, Yesu ya bayyana ga Sha Ɗayan, yayinda suke cin abinci. Ya tsawata musu a kan rashin bangaskiyarsu, da yadda suka ƙi gaskata waɗanda suka gan shi bayan ya tashi.
15 and He said to them, “Having gone into all the world, proclaim the good news to all the creation;
Ya ce, musu, “Ku tafi cikin dukan duniya, ku yi wa’azin bishara ga dukan halitta.
16 he who has believed and has been immersed will be saved; and he who has not believed will be condemned.
Duk wanda ya gaskata, aka kuma yi masa baftisma, zai sami ceto. Amma duk wanda bai gaskata ba kuwa, zai hallaka.
17 And signs will accompany those believing these things: they will cast out demons in My Name; they will speak with new tongues;
Waɗannan alamu za su kasance tare da waɗanda suka gaskata. A cikin sunana za su fitar da aljanu, za su yi magana da sababbin harsuna.
18 they will take up serpents; and if they may drink any deadly thing, it will not hurt them; they will lay hands on the ailing, and they will be well.”
Za su ɗauki macizai da hannuwansu. In kuwa suka sha mugun dafi, ba zai cuce su ba ko kaɗan. Za su ɗibiya hannuwansu a kan marasa lafiya, su kuwa warke.”
19 The LORD, then, indeed, after speaking to them, was received up to Heaven, and sat on the right hand of God;
Bayan Ubangiji Yesu ya yi musu magana, sai aka ɗauke shi zuwa sama, ya kuma zauna a hannun dama na Allah.
20 and they, having gone forth, preached everywhere, the LORD working with [them], and confirming the word, through the signs following. Amen.]]
Sai almajiran suka fita, suka yi wa’azi ko’ina. Ubangiji kuwa ya yi aiki tare da su, ya tabbatar da maganarsa ta wurin alamu da suke biye da maganar.

< Mark 16 >