< Malachi 3 >

1 “Behold, I am sending My messenger, And he has prepared a way before Me, And suddenly the Lord whom you are seeking comes into His temple, Even the Messenger of the Covenant, Whom you are desiring, Behold, He is coming,” said YHWH of Hosts.
“Duba, zan aika manzona, wanda zai shirya hanya a gabana. Sa’an nan a farat ɗaya Ubangiji wanda kuke nema zai zo haikalinsa. Manzon alkawari, wanda kuke sa zuciya kuwa zai zo,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
2 “And who is bearing the day of His coming? And who is standing in His appearing? For He [is] as fire of a refiner, And as soap of a fuller.
Amma wa zai jure wa ranar zuwansa? Wa zai iya tsaya sa’ad da ya bayyana? Gama zai zama kamar wuta mai tace ƙarfe, ko sabulu mai wanki.
3 And He has sat, a refiner and purifier of silver, And He has purified the sons of Levi, And has refined them as gold and as silver, And they have been bringing a present near to YHWH in righteousness.
Zai zama kamar mai tace azurfa da mai tsarkaketa; zai tsabtacce Lawiyawa, yă kuma tace su kamar zinariya da azurfa. Sa’an nan Ubangiji zai sami mutanen da za su kawo hadayu a cikin adalci.
4 And the present of Judah and Jerusalem has been sweet to YHWH, As in days of old, and as in former years.
Hadayun Yahuda da na Urushalima za su zama yardajje ga Ubangiji, za su zama kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a shekarun baya.
5 And I have drawn near to you for judgment, And I have been a witness, Making haste against sorcerers, and against adulterers, And against swearers to a falsehood, And against oppressors of the hire of a hired worker, Of a widow, and of a fatherless one, And those turning aside a sojourner, And who do not fear Me,” said YHWH of Hosts.
“Ta haka zan zo kusa da ku don in yi hukunci. Zan hanzarta ba da shaida a kan masu yin sihiri, da mazinata da masu shaidar zur. Zan ba da shaida a kan waɗanda suke zaluntar ma’aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye da marayu, suna kuma hana baƙi samun adalci, ba sa ma tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
6 “For I, YHWH, have not changed, And you, the sons of Jacob, You have not been consumed.
“Ni Ubangiji ba na canjawa. Shi ya sa ku zuriyar Yaƙub, ba a hallaka ku ƙaƙaf ba.
7 Even from the days of your fathers You have turned aside from My statutes, And you have not taken heed. Return to Me, and I return to you,” said YHWH of Hosts. “And you have said, In what do we turn back?
Tun zamanin kakanninku, kun juye wa ƙa’idodina baya, ba ku kuma kiyaye su ba. Ku komo gare ni, ni kuma zan koma gare ku,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya za mu koma gare ka?’
8 Does man deceive God? But you are deceiving Me, And you have said, In what have we deceived You? The tithe and the raised-offering!
“Mutum zai iya yi wa Allah fashi ne? Duk da haka kun yi mini fashi. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka yi maka fashi?’ “A wajen zakka da hadayu.
9 You are cursed with a curse! And you are deceiving Me—this nation—all of it.
Kuna ƙarƙashin la’ana, dukan al’ummarku, domin kuna yin mini fashi.
10 Bring in all the tithe to the treasure-house, And there is food in My house; When you have tried Me, now, with this,” said YHWH of Hosts, “Do I not open the windows of the heavens to you? Indeed, I have emptied on you a blessing until there is no space.
Ku kawo dukan zakka cikin gidan ajiya, don a kasance da abinci a gidana. Ku gwada ni a wannan ku ga, ko ba zan buɗe taskokin sama in zubo muku albarka mai yawa, wadda har ba za ku rasa wurin sa ta ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
11 And I have pushed against the consumer for you, And He does not destroy the fruit of your ground, Nor does the vine in the field miscarry to you,” said YHWH of Hosts.
Zan hana ƙwari su cinye hatsinku. Kuringar inabi a gonakinku kuma ba za su zubar da’ya’yansu kafin su nuna ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 “And all the nations have declared you blessed, For you are a delightful land,” said YHWH of Hosts.
“Sa’an nan dukan al’ummai za su ce da ku masu albarka, gama ƙasarku za tă yi daɗin zama,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
13 “Your words have been hard against Me,” said YHWH, “And you have said, What have we spoken against You?
“Kun faɗi mugayen abubuwa a kaina,” in ji Ubangiji. “Duk da haka kuka ce, ‘Me muka faɗa a kanka?’
14 You have said, A vain thing to serve God! And what gain when we kept His charge? And when we have gone in black, Because of YHWH of Hosts?
“Kun ce, ‘Ba amfani a bauta wa Allah. Wanda amfani muka samu ta wurin kiyaye umarnansa muna yawo kamar masu makoki a gaban Ubangiji Maɗaukaki?
15 And now, we are declaring the proud blessed, Indeed, those doing wickedness have been built up, Indeed, they have tempted God, and escape.
A ganinmu, masu girman kai suna jin daɗi. Masu aikata mugunta kuwa ba arziki kaɗai suka yi ba, amma sukan gwada Allah da mugayen ayyukansu, su kuwa zauna lafiya.’”
16 Then have those fearing YHWH spoken to one another, And YHWH attends and hears, And a scroll of memorial is written before Him Of those fearing YHWH, And of those esteeming His Name.
Sa’an nan waɗanda suke tsoron Ubangiji suka yi magana da juna, Ubangiji kuwa ya kasa kunne ya kuma ji. A gabansa aka rubuta a littafin tarihi waɗanda suke tsoron Ubangiji, suna kuma girmama sunansa.
17 And they have been to Me,” said YHWH of Hosts, “In the day that I am appointing—a peculiar treasure, And I have had pity on them, As one has pity on his son who is serving him.
“A ranar da na shirya ajiyayyen mallakata, za su zama nawa,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ji kansu kamar yadda mahaifi cikin tausayi yakan ji kan ɗansa wanda yake masa hidima.
18 And you have turned back and considered, Between the righteous and the wicked, Between the servant of God and him who is not His servant.”
Za ku kuma ga bambanci tsakanin masu adalci da mugaye, tsakanin waɗanda suke wa Allah hidima da kuma waɗanda ba sa yi.

< Malachi 3 >