< Luke 6 >

1 And it came to pass, on a Sabbath, as He is going through the grainfields, that His disciples were plucking the ears, and were eating, rubbing with the hands,
A wata ranar Asabbaci, Yesu yana bi ta gonakin hatsi, sai almajiran suka fara kakkarya kan hatsi suna murjewa a hannuwansu suna ci.
2 and certain of the Pharisees said to them, “Why do you do that which is not lawful to do on the Sabbaths?”
Sai waɗansu Farisiyawa suka ce, “Me ya sa kuke yin abin da doka ta hana yi a ranar Asabbaci?”
3 And Jesus answering said to them, “Did you not read even this that David did when he hungered, himself and those who are with him,
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi, sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa ba?
4 how he went into the house of God, and took the Bread of the Presentation, and ate, and gave also to those with him, which it is not lawful to eat, except only to the priests?”
Ya shiga gidan Allah, ya ɗauki keɓaɓɓen burodi, sa’an nan ya ci abin da firistoci kaɗai sukan ci bisa ga doka. Ya kuma ba wa abokan tafiyarsa?”
5 And He said to them, “The Son of Man is Lord also of the Sabbath.”
Sai Yesu ya ce musu, “Ai, Ɗan Mutum ne Ubangijin Asabbaci.”
6 And it came to pass also, on another Sabbath, that He goes into the synagogue, and teaches, and there was there a man, and his right hand was withered,
A wata ranar Asabbaci kuma, Yesu ya shiga majami’a yana koyarwa. To, a nan kuwa akwai wani mutumin da hannun damansa ya shanye.
7 and the scribes and the Pharisees were watching Him, if on the Sabbath He will heal, that they might find an accusation against Him.
Farisiyawa da malaman dokoki suka zuba wa Yesu ido, su ga ko zai warkar a ranar Asabbaci, don su sami dalilin zarginsa.
8 And He Himself had known their reasonings and said to the man having the withered hand, “Rise, and stand in the midst”; and he having risen, stood.
Amma Yesu ya san abin da suke tunani. Sai ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.” Sai ya tashi ya tsaya.
9 Then Jesus said to them, “I will question you something: is it lawful on the Sabbaths to do good, or to do evil? To save life or to kill?”
Yesu ya ce musu, “Ina tambayarku, me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a hallaka shi?”
10 And having looked around on them all, He said to the man, “Stretch forth your hand”; and he did so, and his hand was restored whole as the other;
Sai ya kalle su duka, sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙe, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
11 and they were filled with madness, and were speaking with one another what they might do to Jesus.
Amma Farisiyawa da malaman Doka suka fusata, suka fara tattauna da junansu a kan abin da za su yi wa Yesu.
12 And it came to pass in those days, He went forth to the mountain to pray, and was passing the night in the prayer of God,
Wata rana, a cikin kwanakin nan, Yesu ya je wani dutse domin yă yi addu’a, ya kuma kwana yana addu’a ga Allah.
13 and when it became day, He called near His disciples, also having chosen twelve from them, whom He also named apostles:
Da gari ya waye, sai ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya zaɓi guda goma sha biyu daga cikinsu, waɗanda ya kira su, Manzanni.
14 Simon, whom He also named Peter, and his brother Andrew, James and John, Philip and Bartholomew,
Siman (wanda ya kira Bitrus), ɗan’uwansa Andarawus, Yaƙub, Yohanna, Filibus, Bartolomeyu,
15 Matthew and Thomas, James of Alphaeus, and Simon called Zealot,
Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Siman wanda ake kira Zilot,
16 Judas of James, and Judas Iscariot, who also became betrayer.
Yahuda ɗan Yaƙub, da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
17 And having come down with them, He stood on a level spot; and a crowd of His disciples, and a great multitude of the people from all Judea, and Jerusalem, and the seacoast of Tyre and Sidon,
Sai ya sauko tare da su, ya tsaya a wani fili. A can, akwai taro mai yawa na almajiransa, da kuma mutane masu yawan gaske daga ko’ina a Yahudiya, Urushalima da kuma Taya da Sidon da suke bakin teku,
18 who came to hear Him and to be healed of their diseases, [gathered]. And those harassed by unclean spirits [also gathered] and were healed.
waɗanda suka zo domin su ji shi, a kuma warkar da cututtukansu. Waɗanda suke fama da mugayen ruhohi kuwa aka warkar da su.
19 And all the multitude were seeking to touch Him, because power was going forth from Him, and He was healing all.
Kuma dukan mutane suka yi ƙoƙari su taɓa shi, domin iko yana fitowa daga gare shi, ya kuwa warkar da su duka.
20 And He, having lifted up His eyes to His disciples, said: “Blessed the poor—because yours is the Kingdom of God.
Da ya dubi almajiransa, sai ya ce, “Masu albarka ne ku da kuke matalauta, gama mulkin Allah naku ne.
21 Blessed those hungering now—because you will be filled. Blessed those weeping now—because you will laugh.
Masu albarka ne ku da kuke jin yunwa yanzu, gama za ku ƙoshi. Masu albarka ne ku da kuke kuka yanzu, gama za ku yi dariya.
22 Blessed are you when men will hate you, and when they will separate you, and will reproach, and will cast forth your name as evil, for the Son of Man’s sake—
Masu albarka ne sa’ad da mutane suka ƙi ku, suka ware ku, suka zage ku, suna ce da ku mugaye, saboda Ɗan Mutum.
23 rejoice in that day, and leap, for behold, your reward [is] great in Heaven, for according to these things were their fathers doing to the prophets.
“Ku yi farin ciki a wannan rana, ku kuma yi tsalle don murna, saboda ladarku yana da yawa a sama. Gama haka kakanninsu suka yi wa annabawa.
24 But woe to you—the rich, because you have gotten your comfort.
“Amma kaitonku da kuke da arziki, gama kun riga kun sami ta’aziyyarku.
25 Woe to you who have been filled—because you will hunger. Woe to you who are laughing now—because you will mourn and weep.
Kaitonku da kuke ƙosassu yanzu, gama za ku zauna da yunwa. Kaitonku da kuke dariya yanzu, gama za ku yi makoki da kuka.
26 Woe to you when all men will speak well of you—for according to these things were their fathers doing to false prophets.
Kaitonku sa’ad da dukan mutane suna magana mai kyau a kanku, gama haka kakanninsu suka yi da annabawan ƙarya.
27 But I say to you who are hearing, love your enemies, do good to those hating you,
“Amma ina faɗa muku, ku da kuke ji na, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku yi wa masu ƙinku alheri.
28 bless those cursing you, pray for those maligning you;
Ku albarkaci waɗanda suke la’anta ku, ku kuma yi wa waɗanda suke wulaƙanta ku addu’a.
29 and to him striking you on the cheek, give also the other, and from him taking away from you the mantle, also the coat you may not keep back.
In wani ya mare ka a wannan kumatu, juya masa ɗayan ma, in wani ya ƙwace maka babban riga, kada ma ka hana masa’yar cikin ma.
30 And to everyone who is asking of you, be giving; and from him who is taking away your goods, do not be asking again;
Duk wanda ya roƙe ka abu, ka ba shi. In kuma wani ya yi maka ƙwace, kada ka nema yă mayar maka.
31 and as you wish that men may do to you, do also to them in like manner;
Ka yi wa waɗansu abin da kai kake so su yi maka.
32 and—if you love those loving you, what grace is it to you? For also the sinful love those loving them;
“In kana ƙaunar masu ƙaunarka ne kawai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma suna ƙaunar waɗanda suke ƙaunarsu.
33 and if you do good to those doing good to you, what grace is it to you? For also the sinful do the same;
In kuma kana yin alheri ga masu yi maka ne kaɗai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma suna yin haka.
34 and if you lend [to those] of whom you hope to receive back, what grace is it to you? For also the sinful lend to sinners—that they may receive again as much.
In kana ba da bashi ga mutanen da za su iya biyan ka ne kawai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma, suna ba da bashi ga masu zunubi, da fata za a biya su tsab.
35 But love your enemies, and do good, and lend, hoping for nothing again, and your reward will be great, and you will be sons of the Highest, because He is kind to the ungracious and evil;
Amma, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku kuma yi musu alheri, ku ba su bashi, ba da sa zuciya sai an biya ku ba. Ta yin haka ne kawai, za ku sami lada mai yawa, ku kuma zama’ya’yan Mafi Ɗaukaka, gama shi mai alheri ne ga marasa godiya da mugaye.
36 be therefore merciful, as also your Father is merciful.
Ku zama masu jinƙai, kamar yadda Ubanku mai jinƙai ne.
37 And do not judge, and you may not be judged; do not condemn, and you may not be condemned; release, and you will be released.
“Kada ku ɗora wa wani, ku ma ba za a ɗora muku ba. Kada ku yanke wa wani hukunci, ku ma ba za a yanke muku ba. Ku gafarta, ku ma za a gafarta muku.
38 Give, and it will be given to you; good measure, pressed, and shaken, and running over, they will give into your bosom; for with that measure with which you measure, it will be measured to you again.”
Ku bayar, ku ma sai a ba ku mudu a cike, a danƙare, har yă yi tozo, yana zuba, za a juye muku a hannun riga. Mudun da kuka auna da shi, da shi za a auna muku.”
39 And He spoke an allegory to them, “Is blind able to lead blind? Will they not both fall into a pit?
Ya kuma faɗa musu wannan misali cewa, “Makaho yana iya jagoran makaho ne? Ba sai dukansu biyu su fāɗa a rami ba?
40 A disciple is not above his teacher, but everyone perfected will be as his teacher.
Ɗalibi bai fi malaminsa ba, sai dai kowane ɗalibi wanda ya sami cikakkiyar koyarwa, zai zama kamar malaminsa.
41 And why do you behold the speck that is in your brother’s eye, and do not consider the beam that [is] in your own eye?
“Don me kake duban ɗan tsinke da yake idon ɗan’uwanka, amma ba ka kula da gungumen da yake a naka ido ba?
42 Or how are you able to say to your brother, Brother, permit, I may take out the speck that [is] in your eye—yourself not beholding the beam in your own eye? Hypocrite, first take the beam out of your own eye, and then you will see clearly to take out the speck that [is] in your brother’s eye.
Yaya za ka ce wa ɗan’uwanka, ‘Ɗan’uwa, bari in cire maka ɗan tsinke da yake idonka,’ alhali kuwa, kai kanka ka kāsa ganin gungumen da yake a naka ido? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen daga idonka, sa’an nan za ka iya gani sosai, ka kuma cire ɗan tsinken da yake a idon ɗan’uwanka.”
43 For there is not a good tree making bad fruit, nor a bad tree making good fruit;
“Ba itace mai kyau da yake ba da munanan’ya’ya. Mummunan itace kuma ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
44 for each tree is known from its own fruit, for they do not gather figs from thorns, nor do they crop a grape from a bramble.
Kowane itace da irin’ya’yansa ne ake saninsa. Mutane ba sa tsinke’ya’yan ɓaure daga ƙaya, ko kuwa’ya’yan inabi daga sarƙaƙƙiya.
45 The good man out of the good treasure of his heart brings forth that which [is] good; and the evil man out of the evil treasure of his heart brings forth that which [is] evil; for out of the abounding of the heart his mouth speaks.
Mutumin nagari yakan nuna abubuwa nagari daga cikin nagarta da yake a ɓoye a zuciyarsa, mugun mutum kuwa yakan nuna mugayen abubuwa daga muguntar da take a ɓoye a zuciyarsa. Gama baki yakan faɗa abin da ya cika zuciya ne.”
46 And why do you call Me, Lord, Lord, and do not do what I say?
“Don me kuke ce da ni, ‘Ubangiji, Ubangiji,’ amma ba kwa yin abin da na faɗa?
47 Everyone who is coming to Me, and is hearing My words, and is doing them, I will show you to whom he is like:
Zan nuna muku kwatancin mutumin da yakan zo wurina, yă ji kalmomina, yă kuma aikata.
48 he is like to a man building a house, who dug and deepened, and laid a foundation on the rock, and a flood having come, the stream broke forth on that house, and was not able to shake it, for it had been founded on the rock.
Yana kama da mutumin da ya gina gida, wanda ya haƙa ƙasa da zurfi, sa’an nan ya kafa tushen ginin a kan dutse. Da ambaliyar ruwa ta taso, ƙarfin ruwa kuwa ya buga gidan, wannan bai jijjiga shi ba, domin an yi masa tushen gini na ainihi.
49 And he who heard and did not, is like to a man having built a house on the earth, without a foundation, against which the stream broke forth, and immediately it fell, and the ruin of that house became great.”
Amma wanda yakan ji kalmomina, ba ya kuma aikata su, yana kama da mutumin da ya gina gida a ƙasa, ba tare da ya kafa tushen gini ba. A sa’ad da ƙarfin ruwa ya buga gidan, sai gidan yă rushe, mummunar rushewa kuwa.”

< Luke 6 >