< Luke 4 >

1 And Jesus, full of the Holy Spirit, turned back from the Jordan, and was brought in the Spirit into the wilderness,
Yesu kuwa cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga Urdun, Ruhu kuma ya kai shi cikin hamada,
2 being tempted by the Devil forty days, and He did not eat anything in those days, and they having been ended, He afterward hungered,
inda kwana arba’in, Iblis ya gwada shi. Bai ci kome ba a cikin kwanakin nan, a ƙarshensu kuwa ya ji yunwa.
3 and the Devil said to Him, “If You are [the] Son of God, speak to this stone that it may become bread.”
Iblis ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, ka faɗa wa wannan dutse yă zama burodi.”
4 And Jesus answered him, saying, “It has been written, that, Not on bread only will man live, but on every saying of God.”
Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba.’”
5 And the Devil having brought Him up to a high mountain, showed to Him all the kingdoms of the world in a moment of time,
Iblis ya kai shi can kan wani wuri mai tsawo, ya nunnuna masa a ƙyiftawar ido dukan mulkokin duniya.
6 and the Devil said to Him, “To You I will give all this authority, and their glory, because to me it has been delivered, and to whomsoever I will, I give it;
Ya ce masa, “Zan ba ka dukan ikonsu da darajarsu, gama ni aka danƙa wa, kuma zan bai wa duk wanda na ga dama.
7 You, then, if You may worship me—all will be Yours.”
Saboda haka in ka yi mini sujada, dukan wannan zai zama naka.”
8 And Jesus answering him said, “[[Get behind Me, Satan, for]] it has been written: You will worship the LORD your God, and Him only you will serve.”
Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, kuma shi kaɗai za ka bauta wa.’”
9 And he brought Him to Jerusalem, and set Him on the pinnacle of the temple, and said to Him, “If You are the Son of God, cast Yourself down from here,
Sai Iblis, ya kai shi Urushalima ya sa ya tsaya a kan wuri mafi tsayi na haikali ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka yi tsalle daga nan zuwa ƙasa.
10 for it has been written: To His messengers He will give charge concerning you, to guard over you;
Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, su kiyaye ka da kyau;
11 and: On hands they will bear you up, lest at any time you may dash your foot against a stone.”
za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
12 And Jesus answering said to him, “It has been said, You will not tempt the LORD your God.”
Yesu ya amsa ya ce, “An ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
13 And having ended all temptation, the Devil departed from Him until a convenient season.
Da Iblis ya gama dukan wannan gwajin, ya bar shi sai lokacin da wata dama ta samu.
14 And Jesus turned back in the power of the Spirit to Galilee, and a fame went forth through all the surrounding region concerning Him,
Yesu ya koma Galili cikin ikon Ruhu. Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a ƙauyuka.
15 and He was teaching in their synagogues, being glorified by all.
Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, kowa kuwa ya yabe shi.
16 And He came to Nazareth, where He has been brought up, and He went in, according to His custom, on the day of the Sabbaths, into the synagogue, and stood up to read;
Ya tafi Nazaret, inda aka yi renonsa. A ranar Asabbaci kuma, ya shiga majami’a kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe don yă yi karatu.
17 and there was given over to Him a scroll of Isaiah the prophet, and having unfolded the scroll, He found the place where it has been written:
Aka kuwa ba shi naɗaɗɗen littafin annabi Ishaya. Da ya buɗe, sai ya sami wurin da aka rubuta,
18 “The Spirit of the LORD [is] on Me, Because He anointed Me To proclaim good news to the poor, Sent Me to heal the broken of heart, To proclaim to captives deliverance, And to blind receiving of sight, To send the bruised away with deliverance,
“Ruhun Ubangiji yana kaina, domin ya shafe ni, in yi wa matalauta wa’azin bishara. Ya aiko ni in yi shelar’yanci ga’yan kurkuku, in kuma buɗe idanun makafi, in ba da’yanci ga waɗanda aka danne.
19 To proclaim the acceptable year of the LORD.”
In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”
20 And having folded the scroll, having given [it] back to the officer, He sat down, and the eyes of all in the synagogue were gazing on Him.
Sai ya naɗe naɗaɗɗen littafin ya mayar wa mai hidimar, ya kuma zauna. Dukan idanun waɗanda suke a majami’ar, suka koma a kansa.
21 And He began to say to them, “Today this writing has been fulfilled in your ears”;
Sai ya fara ce musu, “A yau, Nassin nan, ya cika a kunnenku.”
22 and all were bearing testimony to Him, and were wondering at the gracious words that are coming forth out of His mouth, and they said, “Is this not the Son of Joseph?”
Duk suka yabe shi, suka yi mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suka yi tambaya, suna cewa, “Anya, wannan ba ɗan Yusuf ba ne?”
23 And He said to them, “Certainly you will say to Me this allegory, Physician, heal yourself; as great things as we heard done in Capernaum, do also here in Your country”;
Yesu ya ce musu, “Tabbatacce, na san za ku faɗa mini karin maganan nan, ‘Likita, warkar da kanka! Ka kuma yi abin da muka ji ka yi a Kafarnahum, a nan garinka.’”
24 and He said, “Truly I say to you, no prophet is accepted in his own country;
Ya ci gaba, da ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, babu annabin da ake yarda da shi a garinsa.
25 and of a truth I say to you, many widows were in the days of Elijah, in Israel, when the sky was shut for three years and six months, when great famine came on all the land,
Ina tabbatar muku a zamanin Iliya, akwai gwauraye da yawa a Isra’ila, sa’ad da aka rufe sararin sama har shekara uku da rabi, aka kuma yi yunwa mai tsanani ko’ina a ƙasar.
26 and to none of them was Elijah sent, but—to Sarepta of Sidon, to a woman, a widow;
Duk da haka, ba a aiki Iliya ga ko ɗaya a cikinsu ba. Sai dai zuwa ga wata gwauruwa da take a Zarefat, a yankin Sidon.
27 and many lepers were in the time of Elisha the prophet, in Israel, and none of them was cleansed, but—Naaman the Syrian.”
Akwai kuma mutane da yawa a Isra’ila masu kuturta a zamanin annabi Elisha, amma ba ko ɗayansu da aka tsarkake sai Na’aman mutumin Suriyan nan kaɗai.”
28 And all in the synagogue were filled with wrath, hearing these things,
Dukan mutanen da suke cikin majami’a suka fusata ƙwarai da jin wannan.
29 and having risen, they put Him forth outside the city, and brought Him to the brow of the hill on which their city had been built—to cast Him down headlong,
Suka tashi, suka fitar da Yesu bayan gari, suka kai shi goshin tudun da aka gina garin, don su ture shi ƙasa,
30 and He, having gone through the midst of them, went away.
amma sai ya bi ta tsakiyar taron ya yi tafiyarsa.
31 And He came down to Capernaum, a city of Galilee, and was teaching them on the Sabbaths,
Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a Galili, a ranar Asabbaci kuma, ya fara koya wa mutane.
32 and they were astonished at His teaching, because His word was with authority.
Suka yi ta mamakin koyarwarsa, domin saƙonsa yana da iko.
33 And in the synagogue was a man having a spirit of an unclean demon, and he cried out with a great voice,
A cikin majami’ar, akwai wani mutum mai aljani, wani mugun ruhu. Mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce,
34 “Aah! What [regards] us and You, Jesus, O Nazarene? You came to destroy us; I have known who You are—the Holy One of God!”
“Wayyo! Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki na Allah!”
35 And Jesus rebuked him, saying, “Be silenced, and come forth out of him”; and the demon having cast him into the midst, came forth from him, having hurt him nothing;
Yesu ya tsawata masa da ƙarfin cewa, “Yi shiru! Ka fita daga cikinsa!” Sai aljanin ya fyaɗa mutumin da ƙasa a gabansu duka, sa’an nan ya fita, ya bar shi ba wani rauni.
36 and amazement came on all, and they were speaking together with one another, saying, “What [is] this word, that with authority and power He commands the unclean spirits, and they come forth?”
Dukan mutanen suka yi mamaki, suka ce wa junansu, “Wace irin koyarwa ce haka? Da ƙarfi da iko, yana ba wa mugayen ruhohin umarni suna kuma fita!”
37 And there was going forth a fame concerning Him to every place of the surrounding region.
Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a cikin ƙasar.
38 And having risen out of the synagogue, He entered into the house of Simon, and the mother-in-law of Simon was pressed with a great fever, and they asked Him about her,
Yesu ya fita daga majami’ar, ya tafi gidan Siman. Surukar Siman kuwa tana fama da zazzaɓi mai tsanani, sai suka roƙi Yesu yă taimake ta.
39 and having stood over her, He rebuked the fever, and it left her, and immediately, having risen, she was ministering to them.
Sai ya sunkuya kusa da ita, ya kuma tsawata wa zazzaɓin, sai zazzaɓin ya sāke ta. Nan take ta tashi, ta yi musu hidima.
40 And at the setting of the sun, all, as many as had any ailing with manifold diseases, brought them to Him, and He, having put hands on each one of them, healed them.
Rana tana fāɗuwa, sai mutane suka yi ta kawo wa Yesu dukan waɗanda suke da cuta iri-iri, sai ya ɗibiya wa kowannensu hannuwansa, ya warkar da su.
41 And demons were also coming forth from many, crying out and saying, “You are the Christ, the Son of God”; and rebuking, He did not permit them to speak, because they knew Him to be the Christ.
Bugu da ƙari, aljanu suka fiffita daga cikin mutane da yawa suna ihu suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne!” Amma ya kwaɓe su, ya hana su magana, don sun san cewa shi ne Kiristi.
42 And day having come, having gone forth, He went on to a desolate place, and the multitudes were seeking Him, and they came to Him, and were restraining Him—not to go on from them,
Da gari yana wayewa, sai Yesu ya je inda ba kowa. Mutane suka yi ta nemansa, da suka zo inda yake, sai suka yi ƙoƙari su hana shi barinsu.
43 and He said to them, “Also to the other cities it is necessary for Me to proclaim good news of the Kingdom of God, because for this I have been sent”;
Amma ya ce, “Dole in yi wa’azin bisharar mulkin Allah ga sauran garuruwa, saboda wannan ne aka aiko ni.”
44 and He was preaching in the synagogues of Galilee.
Sai ya dinga yin wa’azi a majami’un Yahudiya.

< Luke 4 >