< Luke 16 >

1 And He also said to His disciples, “A certain man was rich, who had a steward, and he was accused to him as scattering his goods;
Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Akwai wani mai arziki da yake da wakili, sai aka yi karan sa da cewa wannan wakili yana fallasar masa da dukiya.
2 and having called him, he said to him, What [is] this I hear about you? Render the account of your stewardship, for you may not be steward any longer.
Sai mai arziki ya kira shi ya ce masa, 'Labarin me nake ji game da kai? Kawo lissafin wakilcin ka, don ba za ka sake zama wakili na ba.'
3 And the steward said in himself, What will I do, because my lord takes away the stewardship from me? I am not able to dig, I am ashamed to beg—
Sai wakilin ya ce a ransa, 'Kaka zan yi, da yake maigida na zai karbe wakilci daga hannuna? Gashi, ba ni da karfin noma ina kuwa jin kunya in yi roko.
4 I have known what I will do, that, when I may be removed from the stewardship, they may receive me to their houses.
Na san abin da zan yi domin idan an fitar da ni daga wakilcin, mutane su karbe ni a gidajensu.
5 And having called near each one of his lord’s debtors, he said to the first, How much do you owe to my lord?
Sai wakilin ya kira kowanne daya da maigidansa ke bi bashi, yace wa na farkon, 'Nawa maigida na yake bin ka?'
6 And he said, One hundred baths of oil; and he said to him, Take your bill, and having sat down write fifty.
Ya ce, 'Garwan mai dari.' Sai ya ce masa, 'Ga takardarka, maza ka zauna, ka rubuta hamsin.'
7 Afterward to another he said, And you, how much do you owe? And he said, One hundred cors of wheat; and he says to him, Take your bill, and write eighty.
Ya kuma ce wa wani, 'Nawa ake binka?' Ya ce, 'Buhu dari na alkama.' Ya ce masa, 'Ga tarkardarka, ka rubuta tamanin.'
8 And the lord commended the unrighteous steward that he did prudently, because the sons of this age are more prudent than the sons of the light in respect to their generation. (aiōn g165)
Sai maigida ya yaba wa wakilin nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama 'ya'yan zamanin nan a ma'ammalar su da mutanen zamaninsu sun fi 'ya'yan haske wayo. (aiōn g165)
9 And I say to you, make to yourselves friends out of the wealth of unrighteousness, that when you may fail, they may receive you into the continuous dwelling places. (aiōnios g166)
Ina gaya maku ku yi abuta ta dukiya ta rashin gaskiya, saboda idan ya kare, su karbe ku a gidaje masu dauwama. (aiōnios g166)
10 He who is faithful in the least, [is] also faithful in much; and he who in the least [is] unrighteous, is also unrighteous in much;
Wanda yake da aminci a karamin abu, mai aminci ne a babban abu, wanda yake marar gaskiya a karamin abu, marar gaskiya ne a babban abu.
11 if, then, in the unrighteous wealth you did not become faithful—who will entrust to you the true?
Idan fa ba ku yi aminci da dukiya mara adalci ba, wa zai amince maku da dukiya ta gaskiya?
12 And if in the other’s you did not become faithful—who will give to you your own?
Idan kuma ba ku yi aminci da kudin wani ba, wa zai ba ku kudin da ke naku?
13 No servant is able to serve two lords, for either he will hate the one, and he will love the other; or one he will hold to, and of the other he will be heedless; you are not able to serve God and wealth.”
Ba bawan da zai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya ko kuwa ya amince wa dayan, ya raina dayan. Ba za ku iya bauta wa Allah ku kuma bauta wa dukiya ba.”
14 And also the Pharisees, being lovers of money, were hearing all these things, and were deriding Him,
Da Farisawa da ke da kaunar kudi suka ji dukan wadannan abubuwa, suka yi masa ba'a.
15 and He said to them, “You are those declaring yourselves righteous before men, but God knows your hearts; because that which is high among men [is] abomination before God;
Sai ya ce masu, “Ku ne masu baratar da kanku a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abin da mutane suke girmamawa kwarai abin kyama ne a gun Allah.
16 the Law and the Prophets [are] until John; since then the good news of the Kingdom of God is proclaimed, and everyone presses into it;
Attaura da litattafan annabawa suna nan har zuwan Yahaya. Tun daga lokacin nan ake yin bisharar mulkin Allah, kowa kuma yana kokarin kutsawa zuwa cikinta.
17 and it is easier for the heaven and the earth to pass away, than one tittle to fall of the Law.
Duk da haka, zai fi sauki sama da kasa su shude, da ko digo daya na attaura ya shude.
18 Everyone who is sending his wife away, and marrying another, commits adultery; and everyone who is marrying her sent away from a husband commits adultery.
Duk wanda ya saki matansa ya auri wata ya aikata zina, kuma wanda ma ya auri sakakkiya ya aikata zina.
19 And—a certain man was rich, and was clothed in purple and fine linen, making merry sumptuously every day,
Akwai wani mai arziki, mai sa tufafi na alfarma masu tsada yana shagalin sa kowace rana.
20 and there was a certain poor man, by name Lazarus, who was laid at his porch, full of sores,
Aka ajiye wani gajiyayye a kofarsa, mai suna liazaru wanda duk jikinsa miki ne,
21 and desiring to be filled from the crumbs that are falling from the table of the rich man; indeed, also the dogs, coming, were licking his sores.
Shi kuwa yana marmarin ya koshi da barbashin da ke fadowa daga teburin mai arzikin nan har ma karnuka sukan zo suna lasar mikinsa.
22 And it came to pass, that the poor man died, and that he was carried away by the messengers into the bosom of Abraham—and the rich man also died, and was buried;
Ana nan sai gajiyayyen nan ya mutu, malaiku kuma suka dauke shi suka kai shi wurin Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi,
23 and having lifted up his eyes in Hades, being in torments, he sees Abraham far off, and Lazarus in his bosom, (Hadēs g86)
yana cikin hades yana shan azaba, sai ya daga kai ya hangi Ibrahim daga nesa, da Li'azaru a kirjinsa. (Hadēs g86)
24 and having cried, he said, Father Abraham, deal kindly with me, and send Lazarus, that he may dip the tip of his finger in water, and may cool my tongue, because I am distressed in this flame.
Sai ya yi kira ya ce, 'Baba Ibrahim, ka ji tausayi na, ka aiko Li'azaru ya tsoma dan yatsansa a ruwa ya sanyaya harshena, don azaba nake sha a cikin wannan wuta.'
25 And Abraham said, Child, remember that you received your good things in your life, and Lazarus in like manner the evil things, and now he is comforted, and you are distressed;
Amma Ibrahim ya ce, 'Yaro, ka tuna fa a zamanka na duniya ka sha duniyarka, ka kuma karba abubuwa masu kyau, amma Li'azaru kuma sai wahala. Amma yanzu dadi ake bashi a nan, kai kuwa kana shan azaba.
26 and besides all these things, between us and you a great chasm is fixed, so that they who are willing to go over from here to you are not able, nor do they pass through from there to us.
Banda haka ma, akwai rami mai zurfi, domin wadanda suke son ketarewa zuwa wurinku kada su iya, kada kuma kowa ya ketaro zuwa wurinmu daga can.'
27 And he said, I ask, then, father, that you may send him to the house of my father,
Sai mai arziki ya ce, 'To ina rokonka, Baba Ibrahim, ka aike shi zuwa gidan mahaifina -
28 for I have five brothers, so that he may thoroughly testify to them, that they also may not come to this place of torment.
domin ina da 'yan'uwa maza biyar, ya je ya yi masu gargadi kada su ma su zo wurin azaban nan.'
29 Abraham says to him, They have Moses and the prophets, let them hear them;
Amma Ibrahim ya ce, 'Suna da Musa da annabawa; bari su saurare su.'
30 and he said, No, father Abraham, but if anyone from the dead may go to them, they will convert.
Sai mai arziki ya amsa, 'A'a, Baba Ibrahim, idan wani daga cikin matattu ya je wurinsu, zasu tuba.'
31 And he said to him, If they do not hear Moses and the prophets, neither will they be persuaded if one may rise out of the dead.”
Amma Ibrahim ya ce masa, 'In dai har basu saurari Musa da na annabawa ba, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su rinjayu ba.'”

< Luke 16 >