< Luke 13 >
1 And there were some present at that time, telling Him about the Galileans, whose blood Pilate mingled with their sacrifices;
A lokacin, wadansu mutane suka gaya masa game da galilawa wadanda Bilatus ya gauraye jininsu da hadayunsu.
2 and Jesus answering said to them, “Do you think that these Galileans became sinners beyond all the Galileans, because they have suffered such things?
Sai Yesu ya amsa masu yace “Kuna tsammani wadannan Galilawa sun fi duk sauran Galilawan zunubi ne, da suka sha azaba haka?
3 No—I say to you, but if you may not convert, even so will all you perish.
A'a, ina gaya maku. In ba ku tuba ba, dukanku za ku halaka kamarsu.
4 Or those eighteen on whom the tower in Siloam fell, and killed them, do you think that these became debtors beyond all men who are dwelling in Jerusalem?
Ko kuwa mutane goma sha takwas din nan da suna Siluwam wadanda hasumiya ta fado a kansu ta kashe su, kuna tsamani sun fi duk sauran mutanen Urushalima laifi ne?
5 No—I say to you, but if you may not convert, all you will perish in like manner.”
Ina gaya maku ba haka bane. Amma duk wanda ya ki tuba, dukanku za su hallaka”
6 And He spoke this allegory: “A certain one had a fig tree planted in his vineyard, and he came seeking fruit in it, and he did not find;
Yesu ya fada wannan misali, “Wani mutum yana da baure wanda ya shuka a garkar inabinsa sai ya zo neman 'ya'yan itacen amma bai samu ba.
7 and he said to the vinedresser, Behold, three years I come seeking fruit in this fig tree, and do not find [it], cut it off, why does it also render the ground useless?
Sai mutumin ya ce wa mai kula da garkar, “ka ga, shekara uku kenan nake zuwa neman 'ya'yan wannan baure, amma ban samu ba. A sare shi. Yaya za a bar shi ya tsare wurin a banza?
8 And he answering says to him, Lord, permit it also this year, until I may dig around it, and cast in dung;
Sai mai lura da garkar ya amsa yace, 'Ka dan ba shi lokaci kadan in yi masa kaftu in zuba masa taki.
9 and if indeed it may bear fruit—and if not so, thereafter you will cut it off.”
In yayi 'ya'ya shekara mai zuwa to, amma in bai yi 'ya'ya ba sai a sare shi!”'
10 And He was teaching in one of the synagogues on the Sabbath,
Wata rana Yesu yana koyarwa a wata majami' a ran Asabaci.
11 and behold, there was a woman having a spirit of disability [for] eighteen years, and she was bent together, and not able to bend back at all,
Sai, ga wata mace a wurin shekarunta goma sha takwas tana da mugun ruhu, duk ta tankware, ba ta iya mikewa.
12 and Jesus having seen her, called [her] near and said to her, “Woman, you have been loosed from your disability”;
Da Yesu ya gan ta, sai ya kira ta ya ce mata, an warkar da ke daga wannan cuta.”
13 and He laid on her [His] hands, and immediately she was set upright, and was glorifying God.
Sai Yesu ya dora hannunsa a kanta, nan da nan sai ta mike a tsaye ta fara daukaka Allah.
14 And the chief of the synagogue answering—much displeased that on the Sabbath Jesus healed—said to the multitude, “Six days there are in which it is necessary to be working; in these, then, coming, be healed, and not on the day of the Sabbath.”
Amma shugaban majami'a yayi fushi domin Yesu yayi warkarwa a ranar Asabaci. Sai shugaban ya amsa yace wa jama'a, “Akwai ranaku shida da ya kamata a yi aiki. Ku zo domin a warkar da ku amma ba ranar Asabaci ba.”
15 Then the LORD answered him and said, “Hypocrite, do not each of you loose his ox or donkey from the stall on the Sabbath, and having led [it] away, water [it]?
Amma Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Munafukai! Ashe kowannenku ba ya kwance Jakinsa ko Sa daga turkensa ya kai shi banruwa ran Asabaci?
16 And this one, being a daughter of Abraham, whom Satan bound eighteen years, behold, did [she] not ought to be loosed from this bond on the day of the Sabbath?”
Ashe wannan 'yar gidan Ibrahim, wanda shaidan ya daure ta shekara goma sha takwas, wato ba za a iya kwance ta a ranar Asabaci kenan ba?
17 And He saying these things, all who were opposed to Him were being ashamed, and all the multitude were rejoicing over all the glorious things that are being done by Him.
Da ya fada wadannan abubuwa, dukansu da suka yi adawa da shi suka kunyata, duk taron kuwa suka yi ta farin ciki da abubuwa masu daraja da yayi.
18 And He said, “To what is the Kingdom of God like? And to what will I liken it?
Sai Yesu ya ce, “Yaya za a misalta mulkin Allah, kuma da me zan kwatanta shi?
19 It is like to a grain of mustard, which a man having taken, cast into his garden, and it increased, and came to a great tree, and the birds of the heavens rested in its branches.”
Yananan kamar kwayar mastad, wanda wani mutum ya dauka ya jefa ta a lambunsa, ta kuma yi girma ta zama gagarumin itace, har tsuntsaye suka yi shekarsu a rassanta.”
20 And again He said, “To what will I liken the Kingdom of God?
Ya sake cewa, “Da me zan kwatanta mulkin Allah?
21 It is like leaven, which a woman, having taken, hid in three measures of meal, until all was leavened.”
Yana kamar yisti wanda wata mace ta dauka ta cuda da mudu uku na garin alkama don ya kumburar da shi.”
22 And He was going through cities and villages, teaching, and making progress toward Jerusalem;
Yesu ya ziyarci kowanne birni da kauye, a hanyar sa ta zuwa Urushalima yana koyar da su.
23 and a certain one said to Him, “Lord, are those saved few?” And He said to them,
Sai wani ya ce masa, “Ubangiji, wadanda za su sami ceto kadan ne?” Sai ya ce masu,
24 “Be striving to go in through the straight gate, because many, I say to you, will seek to go in, and will not be able;
“Ku yi kokari ku shiga ta matsatsiyar kofa, domin na ce maku, mutane dayawa za su nemi shiga amma ba za su iya shiga ba.
25 from the time the Master of the house may have risen up, and may have shut the door, and you may begin to stand outside, and to knock at the door, saying, Lord, Lord, open to us, and He answering will say to you, I have not known you from where you are,
In dai maigida ya riga ya tashi ya rufe kofa, sannan za ku tsaya a waje kuna kwankwasa kofar kuna cewa, 'Ubangiji, Ubangiji, bari mu shiga ciki'. Sai ya amsa yace maku, 'Ni ban san ku ba ko daga ina ku ka fito.'
26 then you may begin to say, We ate before You, and drank, and You taught in our broad places;
Sannan za ku ce, 'Mun ci mun sha a gabanka, ka kuma yi koyarwa a kan titunanmu.'
27 and He will say, I say to you, I have not known you from where you are; depart from Me, all you workers of the unrighteousness.
Amma zai amsa ya ce, “Ina gaya maku, ban san ko daga ina ku ka fito ba, ku tafi daga wurina, dukanku masu aikata mugunta!'
28 There will be there the weeping and the gnashing of the teeth when you may see Abraham, and Isaac, and Jacob, and all the prophets, in the Kingdom of God, and yourselves being cast outside;
Za a yi kuka da cizon hakora a lokacin da kun ga Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu da dukan annabawa a mulkin Allah amma ku-za a jefar da ku waje.
29 and they will come from east and west, and from north and south, and will recline in the Kingdom of God,
Za su zo daga gabas, yamma, kudu, da arewa, za su ci a teburin abinci a mulkin Allah.
30 and behold, there are last who will be first, and there are first who will be last.”
Ku san da wannan, na karshe za su zama na farko, na farko kuma za su zama na karshe.”
31 On that day there came near certain Pharisees, saying to Him, “Go forth, and be going on from here, for Herod wishes to kill You”;
Nan take, wadansu farisiyawa suka zo suka ce masa, “Ka tafi daga nan domin Hirudus yana so ya kashe ka.”
32 and He said to them, “Having gone, say to that fox, Behold, I cast forth demons, and perfect cures today and tomorrow, and the third [day] I am being perfected;
Yesu ya ce, “Ku tafi ku gaya wa dilan nan cewa, 'Duba, na fitar da aljanu, ina warkarwa yau da gobe, kuma a rana ta uku kuwa zan gama aiki na.'
33 but it is necessary for Me today, and tomorrow, and the [day] following, to go on, because it is not possible for a prophet to perish out of Jerusalem.
Ko da kaka, dole ne in ci gaba da tafiyata yau, da gobe, da kuma jibi, don bai dace a kashe annabi nesa da Urushalima ba.
34 Jerusalem, Jerusalem, that is killing the prophets, and stoning those sent to her, how often I willed to gather together your children, as a hen [gathers] her brood under the wings, and you did not will.
Urushalima, Urushalima masu kisan annabawa, masu jifan wadanda aka aiko gare ku. Sau nawa ne ina so in tattara 'ya'yanki kamar yadda kaza take tattara 'ya'yanta a cikin fukafukanta, amma ba ki so wannan ba.
35 Behold, your house is being left to you desolate, and truly I say to you, you may not see Me, until it may come when you may say, Blessed [is] He who is coming in the Name of the LORD.”
Duba, an yashe gidanki. Ina kwa gaya maku ba za ku kara ganina ba sai ran da kuka ce, 'Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji.'”