< Leviticus 21 >
1 And YHWH says to Moses, “Speak to the priests, sons of Aaron, and you have said to them: No one defiles himself for a [dead] person among his people,
Ubangiji ya ce wa Musa, “Yi magana da firistoci,’ya’yan Haruna maza, ka ce musu, ‘Kada firist yă ƙazantar da kansa saboda wani cikin mutanensa da suka mutu,
2 except for his relation who [is] near to him: for his mother, and for his father, and for his son, and for his daughter, and for his brother,
sai dai na danginsa na kusa, kamar mahaifiyarsa ko mahaifinsa, ɗansa ko’yarsa, ɗan’uwansa,
3 and for his sister, the virgin, who is near to him, who has not been to a man; he is defiled for her.
ko’yar’uwarsa da ba tă riga ta yi aure ba, wadda take dogara gare shi, da yake ba ta da miji, saboda ita zai iya ƙazantar da kansa.
4 A master [priest] does not defile himself among his people—to defile himself;
Kada yă ƙazantar da kansa saboda mutanen da suke da dangantakar da shi ta wurin aure, ta yin haka zai ƙazantar da kansa.
5 they do not make baldness on their head, and they do not shave the corner of their beard, and they do not make a cutting in their flesh;
“‘Kada firistoci su aske kansu ƙwal ko su kwakkwafe gemunsu, ko su tsattsage jikunansu.
6 they are holy to their God, and they do not defile the Name of their God, for the fire-offerings of YHWH, bread of their God, they are bringing near, and have been holy.
Dole su kasance masu tsarki ga Allahnsu, kada kuma su ɓata sunan Allahnsu. Domin sukan miƙa hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta, abincin Allahnsu, saboda haka sai su kasance da tsarki.
7 They do not take a woman of harlotry, or defiled, and they do not take a woman cast out from her husband, for he [is] holy to his God;
“‘Ba za su auri matan da karuwanci ya ɓata su, ko waɗanda mazansu suka sake su ba, gama firistoci masu tsarki ne ga Allahnsu.
8 and you have sanctified him, for he is bringing the bread of your God near. He is holy to you, for I, YHWH, sanctifying you, [am] holy.
An ɗauke su da tsarki, domin suna miƙa abincin Allahnku. An ɗauka su masu tsarki gama Ni Ubangiji, mai tsarki ne, Ni wanda ya mai da ku masu tsarki.
9 And when a daughter of any priest defiles herself by going whoring—she is defiling her father; she is burned with fire.
“‘In’yar firist ta ɓata kanta ta wurin zama karuwa, ta kunyatar da mahaifinta ke nan; dole a ƙone ta da wuta.
10 And the high priest of his brothers, on whose head the anointing oil is poured, and who has consecrated his hand to put on the garments, does not uncover his head, nor tear his garments,
“‘Babban firist, wanda yake ɗaya cikin’yan’uwansa wanda aka shafe da mai a kansa, wanda kuma aka naɗa don yă sa rigunan firistoci, kada yă bar gashin kansa buzu-buzu, ko ya kyakketa rigunansa.
11 nor does he come beside any dead person; he does not defile himself for his father and for his mother;
Ba zai shiga inda akwai gawa ba. Kada yă ƙazantar da kansa, ko ma ta mahaifinsa ce ko ta mahaifiyarsa.
12 nor does he go out from the sanctuary, nor does he defile the sanctuary of his God, for the separation of the anointing oil of his God [is] on him; I [am] YHWH.
An keɓe shi domina, kada yă ƙazantar da kansa, kada kuwa yă ɓata Tentin Sujada ta wurin shiga gidan da gawa take, ko ta mahaifinsa, ko ta mahaifiyarsa ce. Ni ne Ubangiji.
13 And he takes a wife in her virginity;
“‘Dole macen da zai aura ta kasance budurwa.
14 a widow, or cast out, or defiled, [or] a harlot—these he does not take, but he takes a virgin of his own people [for] a wife,
Ba zai auri matan da mijinta ya mutu, ko macen da mijinta ya rabu da ita, ko macen da ta ɓata kanta ta wurin karuwanci ba, sai dai yă auri budurwa daga cikin mutanensa,
15 and he does not defile his seed among his people; for I [am] YHWH, sanctifying him.”
don kada yă ƙazantar da’ya’yansa a cikin mutanensa. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da shi mai tsarki.’”
16 And YHWH speaks to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 “Speak to Aaron, saying, No man of your seed throughout their generations in whom there is blemish draws near to bring the bread of his God near,
“Faɗa wa Haruna cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, kada ko ɗaya daga cikin zuriyarka, da yake da lahani yă zo kusa domin yă miƙa hadaya ta ci gare ni.
18 for no man in whom [is] a blemish draws near: a man blind, or lame, or disfigured, or deformed,
Duk mai lahani, ko makaho, ko gurgu, ko mai naƙasa, ko mai wani lahani a jiki;
19 or a man in whom there is a breach in the foot, or a breach in the hand,
ko mai karyayyen ƙafa, ko mai karyayyen hannu,
20 or hunchbacked, or a dwarf, or [with] a defect in his eye, or [with] an itch, or [with] a scab, or [with] a broken testicle.
ko mai ƙusumbi, ko wada, ko wanda yake da lahani a ido, ko mai cuta mai sa ƙaiƙayi, ko mai kirci, ko wanda aka daƙe, ba zai yi kusa domin yă miƙa hadaya ba.
21 No man in whom is blemish (of the seed of Aaron the priest) comes near to bring the fire-offerings of YHWH near; blemish [is] in him; he does not come near to bring the bread of his God near.
Ba zuriyar Haruna firist, mai lahanin da zai zo kusa don yă miƙa hadayun da aka yi ga Ubangiji da wuta. Da yake yana da lahani, ba zai zo kusa don yă miƙa abincin Allahnsa ba.
22 Bread of his God—from the most holy things and from the holy things—he eats;
Zai iya cin abinci mafi tsarki na Allahnsa, haka ma abinci mai tsarki;
23 only, he does not come toward the veil, and he does not draw near to the altar; for blemish [is] in him; and he does not defile My sanctuaries; for I [am] YHWH, sanctifying them.”
duk da haka saboda lahaninsa, ba zai yi kusa da labule, ko yă yi kusa da bagade don kada yă ƙazantar da wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji wanda yake mai da su masu tsarki.’”
24 And Moses speaks to Aaron, and to his sons, and to all the sons of Israel.
Sai Musa ya faɗa wannan wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa.