< Lamentations 3 >
1 [ALEPH-BET] I [am] the man [who] has seen affliction By the rod of His wrath.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 He has led me, and causes to go [in] darkness, and without light.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Surely against me He turns back, He turns His hand all the day.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 He has worn out my flesh and my skin. He has broken my bones.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 He has built up against me, And sets around poverty and weariness.
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 In dark places He has caused me to dwell, As the dead of old.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 He has hedged me in, and I do not go out, He has made heavy my chain.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Also when I call and cry out, He has shut out my prayer.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 He has hedged my ways with hewn work, My paths He has made crooked.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 A bear lying in wait He [is] to me, A lion in secret hiding places.
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 My ways He is turning aside, and He pulls me in pieces, He has made me a desolation.
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 He has bent His bow, And sets me up as a mark for an arrow.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 He has caused to enter into my reins The sons of His quiver.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 I have been a derision to all my people, Their song all the day.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 He has filled me with bitter things, He has filled me [with] wormwood.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 And He breaks with gravel my teeth, He has covered me with ashes.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 And You cast off my soul from peace, I have forgotten prosperity.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 And I say, My strength and my hope have perished from YHWH.
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Remember my affliction and my mourning, Wormwood and gall!
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 Remember well, and my soul bows down in me.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 This I turn to my heart—therefore I hope.
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 The kindnesses of YHWH! For we have not been consumed, For His mercies have not ended.
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 New every morning, abundant [is] Your faithfulness.
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 My portion [is] YHWH, my soul has said, Therefore I hope for Him.
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 YHWH [is] good to those waiting for Him, To the soul [that] seeks Him.
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 [It is] good when one stays and stands still For the salvation of YHWH.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 [It is] good for a man that he bears a yoke in his youth.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 He sits alone, and is silent, For He has laid [it] on him.
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 He puts his mouth in the dust, if so be, there is hope.
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 He gives to his striker the cheek, He is filled with reproach.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 For the Lord does not cast off for all time.
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 For though He afflicted, yet He has pitied, According to the abundance of His kindness.
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 For He has not afflicted with His heart, Nor does He grieve the sons of men.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 To bruise under one’s feet any bound ones of earth,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 To turn aside the judgment of a man, Before the face of the Most High,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 To subvert a man in his cause, the Lord has not approved.
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Who [is] this—he has spoken, and it is, [And] the Lord has not commanded [it]?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 From the mouth of the Most High does not go forth the evils and the good.
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Why does a living man sigh habitually, A man for his sin?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 We search our ways, and investigate, And turn back to YHWH.
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 We lift up our heart on the hands to God in the heavens.
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 We have transgressed and been rebellious, You have not forgiven.
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 You have covered Yourself with anger, And pursue us; You have slain—You have not pitied.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 You have covered Yourself with a cloud, So that prayer does not pass through.
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 Outcast and refuse You make us In the midst of the peoples.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 Opened against us their mouth have all our enemies.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Fear and a snare has been for us, Desolation and destruction.
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Streams of water go down my eye, For the destruction of the daughter of my people.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 My eye is poured out, And does not cease without intermission,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 Until YHWH looks and sees from the heavens,
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 My eye affects my soul, Because of all the daughters of my city.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Hunting—my enemies have hunted me without cause like the bird.
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 They have cut off my life in a pit, And they cast a stone against me.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 Waters have flowed over my head, I have said, I have been cut off.
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 I called Your Name, O YHWH, from the lower pit.
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 You have heard my voice, do not hide Your ear at my breathing—at my cry.
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 You have drawn near in the day I call You, You have said, Do not fear.
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 You have pleaded, O Lord, the pleadings of my soul, You have redeemed my life.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 You have seen, O YHWH, my overthrow, Judge my cause.
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 You have seen all their vengeance, All their thoughts of me.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 You have heard their reproach, O YHWH, All their thoughts against me,
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 The lips of my withstanders, Even their meditation against me all the day.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Their sitting down, and their rising up, Behold attentively, I [am] their song.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 You return to them the deed, O YHWH, According to the work of their hands.
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 You give to them a covered heart, Your curse to them.
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 You pursue in anger, and destroy them, From under the heavens of YHWH!
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.