< Joshua 1 >

1 And it comes to pass after the death of Moses, servant of YHWH, that YHWH speaks to Joshua son of Nun, minister of Moses, saying,
Bayan mutuwar Musa bawan Ubangiji, sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa ɗan Nun, mataimakin Musa,
2 “My servant Moses is dead, and now, rise, pass over this Jordan, you and all this people, to the land which I am giving to them, to the sons of Israel.
“Bawana Musa ya mutu. Yanzu sai ka tashi tare da mutanen nan duka, ku yi shirin ƙetare kogin Urdun zuwa cikin ƙasar da zan ba su Isra’ilawa.
3 Every place on which the sole of your foot treads, I have given it to you, as I have spoken to Moses.
Zan ba ku duk ƙasar da za ku taka, kamar yadda na yi wa Musa alkawari.
4 From this wilderness and Lebanon, and to the great river, the Euphrates River, all the land of the Hittites, and to the Great Sea—the going in of the sun—is your border.
Ƙasar da ta kama daga hamada zuwa Lebanon, zuwa babban Kogin, wato, Kogin Yuferites, da dukan ƙasar Hittiyawa zuwa Bahar Rum, wajen yamma.
5 No man stations himself before you all [the] days of your life; as I have been with Moses, I am with you, I do not fail you, nor forsake you;
Ba wanda zai yi tsayayya da kai dukan kwanakin ranka. Yadda na kasance tare da Musa, haka zan kasance tare da kai; ba zan taɓa rabuwa da kai ba; ba zan yashe ka ba.
6 be strong and courageous, for you cause this people to inherit the land which I have sworn to their fathers to give to them.
“Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, gama kai za ka bi da mutanen nan har su karɓi ƙasar da na yi wa kakanninsu alkawari zan ba su.
7 Only, be strong and very courageous, to observe to do according to all the Law which Moses My servant commanded you; you do not turn aside from it right or left, so that you act wisely in every [place] to where you go;
Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, ka yi lura fa, ka yi biyayya da dokokin da bawana Musa ya ba ka; kada ka kauce ga bin dokokin ko hagu ko dama, domin ka yi nasara a duk, inda za ka je.
8 the scroll of this Law does not depart out of your mouth, and you have meditated in it by day and by night, so that you observe to do according to all that is written in it, for then you cause your way to prosper, and then you act wisely.
Kada ka bar Littafin Dokokin nan yă rabu da bakinka, sai dai ka yi ta tunani game da shi dare da rana, don ka lura, ka yi duk abin da aka rubuta a ciki, ta haka ne za ka yi nasara cikin duk abin da za ka yi.
9 Have I not commanded you? Be strong and courageous; do not be terrified nor frightened, for your God YHWH [is] with you in every [place] to where you go.”
Ba ni na umarce ka ba? Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro. Kada ka ji tsoro; kada ka karaya, gama Ubangiji Allahnka zai kasance tare da kai duk inda za ka je.”
10 And Joshua commands the authorities of the people, saying,
Saboda haka sai Yoshuwa ya umarci shugabannin mutane,
11 “Pass over into the midst of the camp, and command the people, saying, Prepare provision for yourselves, for within three days you are passing over this Jordan, to go in to possess the land which your God YHWH is giving to you to possess it.”
“Ku ratsa cikin sansani, ku gaya wa mutane, ‘Ku shirya guzurinku. Nan da kwana uku za ku ƙetare Urdun a nan, don ku je ka mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ta zama taku.’”
12 And to the Reubenite, and to the Gadite, and to the half of the tribe of Manasseh, Joshua has spoken, saying,
Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse,
13 “Remember the word which Moses, servant of YHWH, commanded you, saying, Your God YHWH is giving rest to you, and He has given this land to you;
“Ku tuna da umarnin da Musa bawan Ubangiji ya yi muku. ‘Ubangiji Allahnku ya ba ku hutawa, ya kuma ba ku wannan ƙasa.’
14 your wives, your infants, and your substance, abide in the land which Moses has given to you beyond the Jordan, and you pass over by fifties, before your brothers, all the mighty men of valor, and have helped them,
Matanku, da yaranku, da kuma dabbobinku za su kasance a ƙasar da Musa ya ba ku a gabashin Urdun, amma dole mayaƙanku, su yi shirin yaƙi su haye, su yi gaba tare da’yan’uwanku, za ku taimaki’yan’uwanku
15 until YHWH gives rest to your brothers as to yourselves, and they have possessed, even they, the land which your God YHWH is giving to them; then you have turned back to the land of your possession, and have possessed it, which Moses, servant of YHWH, has given to you beyond the Jordan, [at] the sun-rising.”
har sai lokacin da Ubangiji ya ba su hutawa, kamar yadda ya yi muku, kuma har sai su ma sun ƙwace ƙasar da Ubangiji Allahnku ya yi alkawari zai ba su. Bayan haka ne za ku koma ku mallaki ƙasarku, wadda Musa bawan Ubangiji ya ba ku a gabashin Urdun.”
16 And they answer Joshua, saying, “All that you have commanded us we do; and to every [place] to where you send us, we go;
Sai suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “Duk abin da ka ce mu yi, za mu yi. Duk inda kuma ka aike mu, za mu je.
17 according to all that we listened to [from] Moses, so we listen to you; surely your God YHWH is with you as He has been with Moses.
Kamar yadda muka yi wa Musa biyayya, haka za mu yi maka biyayya. Ubangiji Allahnka ya kasance tare da Musa.
18 Any man who provokes your mouth, and does not hear your words, in all that you command him, is put to death; only, be strong and courageous.”
Duk wanda ya yi wa maganarka tawaye, ya ƙi yă yi biyayya da maganarka, ko da umarnin da ka ba shi, za a kashe shi. Ka dai ƙarfafa ka kuma yi ƙarfi hali!”

< Joshua 1 >