< Joshua 7 >
1 And the sons of Israel commit a trespass in the devoted thing, and Achan, son of Carmi, son of Zabdi, son of Zerah, of the tribe of Judah, takes from the devoted thing, and the anger of YHWH burns against the sons of Israel.
Amma Isra’ilawa ba su yi aminci game da kayan da aka hallaka ba; Akan ɗan Karmi, ɗan Zabdi, ɗan Zera, na kabilan Yahuda ya kwashi waɗansu abubuwa, saboda haka fushin Ubangiji ya sauka a kan Isra’ilawa.
2 And Joshua sends men from Jericho to Ai, which [is] near Beth-Aven, on the east of Bethel, and speaks to them, saying, “Go up and spy out the land”; and the men go up and spy Ai,
Sai Yoshuwa ya aika mutane daga Yeriko zuwa Ai kusa da Bet-Awen gabas da Betel, ya ce musu, “Ku je ku leƙo ku ga yadda yankin yake.” Sai mutanen suka je suka leƙo asirin ƙasar Ai.
3 and they return to Joshua, and say to him, “Do not let all the people go up; let about two thousand men, or about three thousand men, go up, and they strike Ai; do not cause all the people to labor there; for they [are] few.”
Da suka dawo wurin Yoshuwa suka ce, “Ba lalle dukan jama’a su je yaƙi da Ai ba, ka aika mutum dubu biyu ko dubu uku su je su ciwo ƙasar da yaƙi, ba sai ka dami mutane duka ba, gama mutanen wurin kaɗan ne.”
4 So about three thousand men of the people go up from there, and they flee before the men of Ai,
Saboda haka sai kimanin mutum duba uku suka haura; amma mutanen Ai suka fatattake su,
5 and the men of Ai strike about thirty-six men from them, and pursue them before the gate to Shebarim, and they strike them in Morad; and the heart of the people is melted, and becomes water.
suka kashe Isra’ilawa wajen mutum talatin da shida, suka fafari Isra’ilawa tun daga bakin ƙofar birnin har zuwa wurin da ake fasa duwatsu. Suka karkashe su a gangare. Wannan ya sa zuciyar Isra’ilawa ta narke suka zama kamar ruwa.
6 And Joshua tears his garments, and falls on his face to the earth before the Ark of YHWH until the evening, he and [the] elderly of Israel, and they cause dust to go up on their head.
Sai Yoshuwa ya yaga tufafinsa ya fāɗi rubda ciki a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, yana can har yamma. Dattawan Isra’ila ma suka yi haka, suka zuba toka a kawunansu.
7 And Joshua says, “Aah! Lord YHWH, why have You caused this people to pass over the Jordan at all, to give us into the hand of the Amorite to destroy us? And oh that we had been willing—and we dwell beyond the Jordan!
Yoshuwa kuma ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, me ya sa ka sa mutanen nan suka ƙetare Urdun don ka bari mu shiga hannun Amoriyawa su hallaka mu? Kila da mun haƙura mun zauna a ɗaya gefen Urdun da ya fi mana!
8 Oh, Lord, what do I say, after that Israel has turned the neck before its enemies?
Ya Ubangiji me zan ce, yanzu da abokan gāban Isra’ilawa suka ci ƙarfinsu?
9 And the Canaanite and all the inhabitants of the land hear, and have come around against us, and cut off our name from the earth; and what do You do for Your great Name?”
Yanzu Kan’aniyawa da sauran jama’a za su ji, za su zo su kewaye mu su share sunanmu daga duniya. To, yanzu me za ka yi don girman sunanka?”
10 And YHWH says to Joshua, “Rise, for you—why this—[that] you [are] falling on your face?
Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka tashi! Me kake yi kwance rubda ciki?
11 Israel has sinned, and they have also transgressed My covenant which I commanded them, and also taken of the devoted thing, and also stolen, and also deceived, and also put [it] among their vessels,
Isra’ilawa sun yi zunubi, sun karya sharaɗin da na yi musu. Sun ɗauki waɗansu abubuwan da aka keɓe; sun yi sata, sun yi ƙarya, sun ɓoye su cikin kayansu.
12 and the sons of Israel have not been able to stand before their enemies; they turn the neck before their enemies, for they have become a devoted thing; I do not add to be with you—if you do not destroy the devoted thing from your midst.
Shi ne ya sa Isra’ilawa suka kāsa yin tsayayya da abokan gābansu; suka juya suka gudu domin za a hallaka su. Ba zan sāke kasancewa tare da ku ba sai in kun hallaka duk abin da aka keɓe don hallaka.
13 Rise, sanctify the people, and you have said, Sanctify yourselves for tomorrow; for thus said YHWH, God of Israel: A devoted thing [is] in your midst, O Israel, you are not able to stand before your enemies until your turning aside the devoted thing from your midst;
“Tashi, ka je ka tsarkake mutane. Ka ce musu su tsarkake kansu, su yi shiri domin gobe; gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, a cikinku akwai abubuwan da aka keɓe, ya Isra’ilawa. Ba za ku iya yin tsayayya da abokan gābanku ba sai in kun rabu da abubuwan nan da aka haramta.
14 and you have been brought near in the morning by your tribes, and it has been [that] the tribe which YHWH captures draws near by families, and the family which YHWH captures draws near by households, and the household which YHWH captures draws near by men;
“‘Da safe ku zo kabila-kabila. Kabilar da Ubangiji ya ware, za tă zo gaba gida-gida; gidan da Ubangiji ya ware, za su zo gaba iyali-iyali. Iyalin kuma da Ubangiji ya ware, za su zo gaba mutum bayan mutum.
15 and it has been, he who is captured with the devoted thing is burned with fire, he and all that he has, because he has transgressed the covenant of YHWH, and because he has done folly in Israel.”
Mutumin da aka same shi da haramtattun abubuwan kuwa za a ƙone shi, duk da mallakarsa domin ya karya sharaɗin da Ubangiji ya yi muku, ya yi abin kunya a Isra’ila!’”
16 And Joshua rises early in the morning, and brings Israel near by its tribes, and the tribe of Judah is captured;
Kashegari da sassafe Yoshuwa ya sa Isra’ilawa suka fito kabila-kabila, aka ware kabilar Yahuda.
17 and he brings the family of Judah near, and he captures the family of the Zerahite; and he brings the family of the Zerahite near by men, and Zabdi is captured;
Gidan Yahuda suka zo gaba, sai aka ware gidan Zera, aka sa suka fito iyali-iyali, sai aka ware Zabdi.
18 and he brings his household near by men, and Achan—son of Carmi, son of Zabdi, son of Zerah, of the tribe of Judah—is captured.
Yoshuwa kuwa ya sa iyalin Zabdi suka fito mutum-mutum, sai kuwa aka ware Akan ɗan Karmi, ɗan Zimri, ɗan Zera na kabilar Yahuda.
19 And Joshua says to Achan, “My son, please give glory to YHWH, God of Israel, and give thanks to Him, and now declare to me what you have done—do not hide [it] from me.”
Sai Yoshuwa ya ce wa Akan, “Ɗana, sai ka ba Ubangiji, Allah na Isra’ila ɗaukaka, ka yi masa yabo. Ka gaya mini abin da ka yi; kada ka ɓoye mini.”
20 And Achan answers Joshua and says, “Truly I have sinned against YHWH, God of Israel, and I have done thus and thus;
Akan kuwa ya amsa ya ce, “Gaskiya ne! Na yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila zunubi. Ga abin da na yi.
21 and I see among the spoil a good robe of Shinar, and two hundred shekels of silver, and one wedge of gold, whose weight [is] fifty shekels, and I desire them, and take them; and behold, they [are] hid in the earth, in the midst of my tent, and the silver [is] under it.”
A cikin ganimar, na ga doguwar riga mai kyau irin ta Babilon, da shekel ɗari biyu na azurfa, da kuma sandan zinariya mai nauyin shekel hamsin, sai raina ya so su, na kuwa kwashe su. Na tona rami a cikin ƙasa a tentina; na ɓoye.”
22 And Joshua sends messengers, and they run to the tent, and behold, it is hidden in his tent, and the silver [is] under it;
Sai Yoshuwa ya aiki’yan aika suka tafi da gudu zuwa tenti ɗin, haka kuwa suka same su a ɓoye a tentinsa, da azurfa a ƙarƙashi.
23 and they take them out of the midst of the tent, and bring them to Joshua, and to all the sons of Israel, and pour them out before YHWH.
Suka kwashe kayan daga tenti ɗin suka kawo wa Yoshuwa da sauran Isra’ilawa, suka baza su a gaban Ubangiji.
24 And Joshua takes Achan son of Zerah, and the silver, and the robe, and the wedge of gold, and his sons, and his daughters, and his ox, and his donkey, and his flock, and his tent, and all that he has, and all Israel with him, and they brought them up [to] the Valley of Achor.
Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ɗauki Akan ɗan Zera, da azurfar, doguwar rigar, sandan zinariya,’ya’yansa maza da mata, shanunsa, jakuna da tumaki, tentinsa da duk abin da yake da shi, suka kai su Kwarin Akor.
25 And Joshua says, “Why have you troubled us? YHWH troubles you this day!” And all Israel cast stone at him, and they burn them with fire, and they stone them with stones,
Yoshuwa ya ce, “Me ya sa ka jawo mana wahala haka? Ubangiji zai kawo maka wahala kai ma a yau.” Sai dukan Isra’ilawa suka jajjefe shi, bayan da suka gama jifarsa sai suka ƙone sauran.
26 and they raise up a great heap of stones over him to this day, and YHWH turns back from the heat of His anger, therefore [one] has called the name of that place “Valley of Achor” until this day.
Suka tara manyan duwatsu a kan Akan, tarin duwatsun na nan a can har wa yau. Sa’an nan Ubangiji ya huce daga fushinsa mai zafi. Saboda haka ake kiran wurin Kwarin Akor.