< Joshua 21 >

1 And the heads of the fathers of the Levites draw near to Eleazar the priest, and to Joshua son of Nun, and to the heads of the fathers of the tribes of the sons of Israel,
To, a lokacin, sai shugabannin iyalan Lawiyawa suka je wurin Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin sauran iyalan kabilu na Isra’ila a
2 and they speak to them in Shiloh, in the land of Canaan, saying, “YHWH commanded by the hand of Moses to give to us cities to dwell in, and their outskirts for our livestock.”
Shilo cikin Kan’ana, suka ce musu, “Ubangiji ya yi umarni ta wurin Musa cewa a ba mu garuruwan da za mu zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau don dabbobinmu.”
3 And the sons of Israel give to the Levites, out of their inheritance, at the command of YHWH, these cities and their outskirts:
Saboda haka kamar yadda Ubangiji ya umarta, sai Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo daga cikin gādonsu.
4 and the lot goes out for the families of the Kohathite, and there are for the sons of Aaron the priest (of the Levites), out of the tribe of Judah, and out of the tribe of Simeon, and out of the tribe of Benjamin, thirteen cities by lot,
Ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kan Kohatawa bisa ga iyalansu. Sai aka ba wa Lawiyawa waɗanda suke’yan zuriyar Haruna, firist, garuruwa goma sha uku daga kabilan Yahuda, Simeyon da Benyamin.
5 and for the sons of Kohath who are left, out of the families of the tribe of Ephraim, and out of the tribe of Dan, and out of the half-tribe of Manasseh, ten cities by lot.
Sauran Kohatawan kuma aka ba su garuruwa goma daga iyalan kabilar Efraim, Dan da kuma rabi kabilar Manasse.
6 And for the sons of Gershon, out of the families of the tribe of Issachar, and out of the tribe of Asher, and out of the tribe of Naphtali, and out of the half-tribe of Manasseh in Bashan, [are] thirteen cities by lot.
Aka kuma ba wa zuriyar Gershon garuruwa goma sha uku daga iyalan kabilan Issakar, Asher, Naftali, da kuma rabin kabilar Manasse a Bashan.
7 For the sons of Merari, for their families, out of the tribe of Reuben, and out of the tribe of Gad, and out of the tribe of Zebulun, [are] twelve cities.
Aka ba wa zuriyar Merari bisa ga iyalansu, garuruwa goma sha biyu daga kabilan Ruben, Gad da Zebulun.
8 And the sons of Israel give these cities and their outskirts to the Levites, as YHWH commanded by the hand of Moses, by lot.
Haka Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo masu kyau, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
9 And they give out of the tribe of the sons of Judah, and out of the tribe of the sons of Simeon, these cities which are called by name;
Daga kabilan Yahuda da Simeyon ne aka ba su waɗannan garuruwan da aka ambata,
10 and they are for the sons of Aaron, of the families of the Kohathite, of the sons of Levi, for the first lot has been theirs;
(ga garuruwan da aka ba wa zuriyar Haruna waɗanda suke daga iyalan Kohatawa na Lawiyawa, domin ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kansu),
11 and they give to them the city of Arba father of Anak (it [is] Hebron), in the hill-country of Judah, and its outskirts around it;
an ba su, Kiriyat Arba (wato, Hebron), da wurin kiwon da yake kewaye da ƙasar kan tudu ta Yahuda. (Arba shi ne kakan Anak.)
12 and they have given the field of the city and its villages to Caleb son of Jephunneh for his possession.
Amma sai aka ba Kaleb ɗan Yefunne filayen da kuma ƙauyukan da suke kewaye da birnin, su zama nasa.
13 And to the sons of Aaron the priest they have given the city of refuge [for] the manslayer, Hebron and its outskirts, and Libnah and its outskirts,
Sai aka ba zuriyar Haruna firist, ƙasar Hebron (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Libna,
14 and Jattir and its outskirts, and Eshtemoa and its outskirts,
da Yattir, da Eshtemowa,
15 and Holon and its outskirts, and Debir and its outskirts,
da Holon, da Debir,
16 and Ain and its outskirts, and Juttah and its outskirts, Beth-Shemesh and its outskirts; nine cities out of these two tribes.
da Ayin, da Yutta, da kuma Bet-Shemesh, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa tara ke nan daga kabilun nan biyu, Yahuda da Simeyon.
17 And out of the tribe of Benjamin, Gibeon and its outskirts, Geba and its outskirts,
Daga kabilar Benyamin kuwa aka ba su, Gibeyon, Geba,
18 Anathoth and its outskirts, and Almon and its outskirts—four cities;
Anatot da Almon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
19 all the cities of the sons of Aaron the priests, [are] thirteen cities and their outskirts.
Duka-duka garuruwan firistoci, zuriyar Haruna, su goma sha uku ne tare da wuraren kiwonsu.
20 And for the families of the sons of Kohath, the Levites, who are left of the sons of Kohath, even the cities of their lot are of the tribe of Ephraim;
Aka kuma ba wa sauran Kohatawa, iyalan Lawiyawa, garuruwa daga kabilar Efraim.
21 and they give to them the city of refuge [for] the manslayer, Shechem and its outskirts, in the hill-country of Ephraim, and Gezer and its outskirts,
A ƙasar kan tudu ta Efraim, aka ba su, Shekem (garin masu neman mafaka don sun yi kisa) da Gezer,
22 and Kibzaim and its outskirts, and Beth-Horon and its outskirts—four cities.
Kibzayim da Bet-Horon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
23 And out of the tribe of Dan, Eltekeh and its outskirts, Gibbethon and its outskirts,
Haka kuma daga kabilar Dan, aka ba su, Elteke, Gibbeton,
24 Aijalon and its outskirts, Gath-Rimmon and its outskirts—four cities.
Aiyalon da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
25 And out of the half-tribe of Manasseh, Taanach and its outskirts, and Gath-Rimmon and its outskirts—two cities;
Daga rabin kabilar Manasse kuwa aka ba su, Ta’anak da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan.
26 all the cities [are] ten and their outskirts, for the families of the sons of Kohath who are left.
Dukan garuruwan nan goma tare da wuraren kiwonsu ne aka ba sauran iyalan Kohatawa.
27 And for the sons of Gershon, of the families of the Levites, out of the half-tribe of Manasseh, the city of refuge [for] the manslayer, Golan in Bashan and its outskirts, and Beeshterah and its outskirts—two cities.
Aka ba wa zuriyar Gershon, waɗanda suke Lawiyawa, rabo. Daga rabin kabilar Manasse, Golan a cikin Bashan (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Be’eshtera, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan;
28 And out of the tribe of Issachar, Kishon and its outskirts, Dabarath and its outskirts,
daga kabilar Issakar kuma aka ba su Kishiyon, Daberat,
29 Jarmuth and its outskirts, En-Gannim and its outskirts—four cities.
Yarmut da En Gannim, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
30 And out of the tribe of Asher, Mishal and its outskirts, Abdon and its outskirts,
daga kabilar Asher kuwa aka ba su, Mishal, Abdon,
31 Helkath and its outskirts, and Rehob and its outskirts—four cities.
Helkat da Rehob, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
32 And out of the tribe of Naphtali, the city of refuge [for] the manslayer, Kedesh in Galilee and its outskirts, and Hammoth-Dor and its outskirts, and Kartan and its outskirts—three cities;
daga kabilar Naftali kuma aka ba su, Kedesh a cikin Galili (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Hammon-Dor da kuma Kartan, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa uku ke nan.
33 all the cities of the Gershonite, for their families, [are] thirteen cities and their outskirts.
Duka-duka, garuruwan iyalan Gershonawa goma sha uku ne, tare da wuraren kiwonsu.
34 And for the families of the sons of Merari, the Levites, who are left, [are, ] out of the tribe of Zebulun, Jokneam and its outskirts, Kartah and its outskirts,
Aka ba wa iyalan Merari (sauran Lawiyawa) garuruwa, daga kabilar Zebulun, wato, Yokneyam, Karta,
35 Dimnah and its outskirts, Nahalal and its outskirts—four cities.
Dimna da kuma Nahalal, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
36 And out of the tribe of Reuben, Bezer and its outskirts, and Jahazah and its outskirts,
daga kabilar Ruben kuma aka ba su, Bezer, Yahza,
37 Kedemoth and its outskirts, and Mephaath and its outskirts—four cities.
Kedemot da kuma Mefa’at, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
38 And out of the tribe of Gad, the city of refuge [for] the manslayer, Ramoth in Gilead and its outskirts, and Mahanaim and its outskirts,
daga kabilar Gad kuwa aka ba su, Ramot Gileyad (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Mahanayim,
39 Heshbon and its outskirts, Jazer and its outskirts—four cities [in] all.
Heshbon da kuma Yazer, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
40 All the cities for the sons of Merari, for their families, who are left of the families of the Levites—their lot is twelve cities.
Duka-duka garuruwan da aka ba iyalan mutanen Merari, waɗanda su ne sauran Lawiyawa, garuruwa goma sha biyu ne.
41 All the cities of the Levites in the midst of the possession of the sons of Israel [are] forty-eight cities, and their outskirts.
Jimillar birane da wurarensu na kiwon da aka ba Lawiyawa daga cikin mallakar jama’ar Isra’ila guda arba’in da takwas ne.
42 These cities are each city and its outskirts around it; so to all these cities.
Dukan garuruwan nan kowannensu yana kewaye da wurin kiwo.
43 And YHWH gives to Israel the whole of the land which He has sworn to give to their fathers, and they possess it, and dwell in it;
Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa dukan ƙasar da ya yi wa kakanninsu alkawari, suka kuwa mallake ta, suka zauna a cikinta.
44 and YHWH gives rest to them all around, according to all that which He has sworn to their fathers, and there has not stood a man in their presence of all their enemies, YHWH has given the whole of their enemies into their hand;
Ubangiji ya ba su hutawa a kowane gefe kamar yadda ya yi wa kakanninsu alkawari, ba ko ɗaya daga cikin abokan gābansu da ya iya cinsu da yaƙi.
45 there has not fallen a thing of all the good thing which YHWH spoke to the house of Israel—the whole has come.
Ubangiji kuwa ya cika kowane alkawarin alherin da ya yi wa mutanen Isra’ila.

< Joshua 21 >