< Jonah 3 >

1 And there is a word of YHWH to Jonah a second time, saying,
Sa’an nan sai maganar Ubangiji ta zo wa Yunana sau na biyu.
2 “Rise, go to Nineveh, the great city, and proclaim to it the proclamation that I am speaking to you”;
“Tafi babban birnin nan Ninebe, ka yi masa shelar saƙon da na ba ka.”
3 and Jonah rises, and he goes to Nineveh, according to the word of YHWH. And Nineveh has been a great city before God, a journey of three days.
Sai Yunana ya yi biyayya da maganar Ubangiji, ya tafi Ninebe. Ninebe birni ne da yake da muhimmanci, wanda sai an ɗauki kwana uku kafin a iya zaga shi.
4 And Jonah begins to go into the city—a journey of one day—and proclaims and says, “Yet forty days and Nineveh is overturned!”
A rana ta fari, Yunana ya kama tafiya yana ratsa birnin. Sai ya yi shela cewa, “Nan da kwana arba’in za a hallaka Ninebe?”
5 And the men of Nineveh believe in God, and proclaim a fast, and put on sackcloth, from their greatest even to their least,
Mutanen Ninebe kuwa suka gaskata Allah. Aka yi shela a yi azumi, sai dukansu daga babba har zuwa ƙaraminsu, suka sa tufafin makoki.
6 seeing the word comes to the king of Nineveh, and he rises from his throne, and removes his honorable robe from off him, and spreads out sackcloth, and sits on the ashes,
Da saƙon Yunana ya kai kunnen sarkin Ninebe, sai ya tashi daga kujerar mulkinsa, ya tuɓe alkyabbarsa, ya sa rigar makoki, ya zauna cikin toka.
7 and he cries and says in Nineveh by a decree of the king and his great ones, saying, “Man and beast, herd and flock—do not let them taste anything, do not let them feed, do not even let them drink water;
Sai ya yi umarni a Ninebe cewa, “Bisa ga umarnin sarki da fadawansa. “Kada a bar wani mutum ko dabba, garke ko shannu, su ɗanɗana wani abu; kada a bari su ci ko su sha.
8 and let man and beast cover themselves [with] sackcloth, and let them call to God mightily, and let them each turn back from his evil way, and from the violence that [is] in their hands.
Bari kowane mutum da dabba yă yafa rigunan makoki. Kowa yă roƙi Allah da gaske, kowa kuma yă bar mugayen ayyukan da yake yi.
9 Who knows? He turns back, and God has relented, and has turned back from the heat of His anger, and we do not perish.”
Wa ya sani? Ko Allah zai ji tausayinmu da kuma juyayinmu yă janye zafin fushinsa don kada mu hallaka.”
10 And God sees their works, that they have turned back from their evil way, and God relents of the evil that He spoke of doing to them, and He has not done [it].
Da Allah ya ga abin da suka yi, da kuma yadda suka juya daga mugayen hanyoyinsu sai ya ji tausayinsu, bai kawo hallaka a kansu yadda ya yi shirin yi ba.

< Jonah 3 >