< John 1 >

1 In the beginning was the Word, and the Word was with God, and the Word was God;
A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne.
2 this One was in the beginning with God;
Shi kuwa tare da Allah yake tun farko.
3 all things happened through Him, and without Him not even one thing happened that has happened.
Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.
4 In Him was life, and the life was the light of men,
A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane.
5 and the light shined in the darkness, and the darkness did not perceive it.
Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
6 There came a man—having been sent from God—whose name [is] John,
Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
7 this one came for testimony, that he might testify about the Light, that all might believe through him;
Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa.
8 that one was not the Light, but—that he might testify about the Light.
Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
9 He was the true Light, which enlightens every man, coming into the world;
Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
10 He was in the world, and the world was made through Him, and the world did not know Him:
Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba.
11 He came to [His] own, and [His] own did not receive Him;
Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
12 but as many as received Him, to them He gave authority to become sons of God—to those believing in His Name,
Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah.
13 who were begotten, not of blood, nor of will of flesh, nor of will of man, but of God.
Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
14 And the Word became flesh, and dwelt among us, and we beheld His glory, glory as of [the] only begotten of [the] Father, full of grace and truth.
Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya.
15 John testifies concerning Him, and has cried, saying, “This was He of whom I said, He who is coming after me has come before me, for He was before me.”
Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, “Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'”
16 And we all received out of His fullness, and grace for grace;
Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri.
17 for the Law was given through Moses, the grace and the truth came through Jesus Christ.
Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu.
18 No one has ever seen God; the only begotten God who is on the bosom of the Father—He has expounded [Him].
Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
19 And this is the testimony of John when the Jews sent priests and Levites out of Jerusalem, that they might question him, “Who are you?”
Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, “Wanene kai?”
20 And he confessed and did not deny, and confessed, “I am not the Christ.”
Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, “ba nine Almasihu ba.”
21 And they questioned him, “What then? Are you Elijah?” And he says, “I am not.” “Are you the prophet?” And he answered, “No.”
Sai suka tambaye shi, “To kai wanene? Kai Iliya ne?” Yace, “Ba ni ba ne.” Suka ce, “Kai ne anabin?” Ya amsa, “A'a”.
22 Then they said to him, “Who are you, that we may give an answer to those sending us? What do you say concerning yourself?”
Sai suka ce masa, “Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?”
23 He said, “I [am] a voice of one crying in the wilderness: Make straight the way of the LORD, as Isaiah the prophet said.”
Yace, “Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada.”
24 And those sent were of the Pharisees,
Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa,
25 and they questioned him and said to him, “Why, then, do you immerse, if you are not the Christ, nor Elijah, nor the prophet?”
“To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?”.
26 John answered them, saying, “I immerse in water, but in the midst of you has stood He whom you have not known, it is this One who is coming after me, who has been before me,
Yahaya ya amsa masu, cewa, “Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba,
27 of whom I am not worthy that I may loose the strap of His sandal.”
shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba.”
28 These things came to pass in Bethabara, beyond the Jordan, where John was immersing.
Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
29 On the next day John sees Jesus coming to him and says, “Behold, the Lamb of God, who is taking away the sin of the world;
Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, “Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya!
30 this is He concerning whom I said, After me comes a Man who has come before me, because He was before me:
Wannan shine wanda na fada maku cewa, “Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'
31 and I did not know Him, but that He might be revealed to Israel, because of this I came immersing in water.”
Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa. “
32 And John testified, saying, “I have seen the Spirit coming down out of Heaven as a dove, and [that] One remained on Him;
Yahaya ya shaida, cewa, “Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa.
33 and I did not know Him, but He who sent me to immerse in water, He said to me, On whomsoever you may see the Spirit coming down, and remaining on Him, this is He who is immersing in the Holy Spirit;
Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.'
34 and I have seen, and have testified, that this is the Son of God.”
Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah.”
35 On the next day, again, John was standing, and two of his disciples,
Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa,
36 and having looked on Jesus walking, he says, “Behold, the Lamb of God”;
suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, “Duba, ga Dan rago na Allah!”
37 and the two disciples heard him speaking, and they followed Jesus.
Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu.
38 And Jesus having turned, and having beheld them following, says to them, “What do you seek?” And they said to Him, “Rabbi” (which is, being interpreted, Teacher), “where do You remain?”
Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, “Me kuke so?” Suka amsa, “Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?”
39 He says to them, “Come and see”; they came and saw where He remains, and they remained with Him that day and the hour was about the tenth.
Yace masu, “Zo ku gani.” Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
40 Andrew, the brother of Simon Peter, was one of the two who heard from John, and followed Him;
Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus.
41 this one first finds his own brother Simon and says to him, “We have found the Messiah,” (which is, being interpreted, Anointed One),
Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, “Mun sami Almasihu” (wanda ake kira 'Kristi').
42 and he brought him to Jesus: and having looked on him, Jesus says, “You are Simon, the son of Jonas, you will be called Cephas,” (which is interpreted, A rock).
Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, “Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas,” (ma'ana, 'Bitrus').
43 On the next day He willed to go forth to Galilee, and He finds Philip and says to him, “Follow Me.”
Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, “ka biyo ni.”
44 And Philip was from Bethsaida, of the city of Andrew and Peter;
Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus.
45 Philip finds Nathanael and says to him, “Him of whom Moses wrote in the Law, and the Prophets, we have found, Jesus the Son of Joseph, who [is] from Nazareth!”
Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, “Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat.”
46 And Nathanael said to him, “Is any good thing able to be out of Nazareth?” Philip said to him, “Come and see.”
Natana'ilu ya ce masa, “za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?” Filibus yace masa, “Zo ka gani.”
47 Jesus saw Nathanael coming to Him, and He says concerning him, “Behold, truly an Israelite, in whom is no guile”;
Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, “Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa.”
48 Nathanael says to Him, “From where do You know me?” Jesus answered and said to him, “Before Philip’s calling you, being under the fig tree, I saw you.”
Natana'ilu yace masa, “Ta yaya ka san ni?” Sai Yesu ya amsa masa yace, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka.”
49 Nathanael answered and says to Him, “Rabbi, You are the Son of God, You are the King of Israel.”
Natana'ilu ya amsa, “Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!”
50 Jesus answered and said to him, “Because I said to you, I saw you under the fig tree, you believe; you will see greater things than these”;
Yesu ya amsa masa yace, “Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma.”
51 and He says to him, “Truly, truly, I say to you, from now on you will see Heaven opened, and the messengers of God going up and coming down on the Son of Man.”
Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum.”

< John 1 >