< John 7 >

1 And Jesus was walking after these things in Galilee, for He did not wish to walk in Judea, because the Jews were seeking to kill Him,
Bayan wadannan abubuwa Yesu ya zagaya cikin Gallili, saboda baya so ya shiga cikin Yahudiya domin Yahudawa suna shirin su kashe shi.
2 and the celebration of the Jews was near—that of Shelters—
To Idin Bukkoki na Yahudawa ya kusa.
3 His brothers, therefore, said to Him, “Depart from here, and go away to Judea, that Your disciples may also behold Your works that You do;
Sai 'yan'uwansa suka ce da shi, “ka tashi ka tafi Yahudiya, domin almajiranka su ga ayyukan da kake yi su ma.
4 for no one does anything in secret, and himself seeks to be in public; if you do these things—reveal Yourself to the world”;
Ba wanda ya ke yin wani abu a boye idan dai yana so kowa da kowa ya san shi. Da yake ka na yin wadannan abubuwa sai ka nuna kan ka a fili ga duniya.
5 for not even His brothers were believing in Him.
Domin ko 'yan'uwansa ma basu bada gaskiya gare shi ba.
6 Jesus, therefore, says to them, “My time is not yet present, but your time is always ready;
Yesu ya ce dasu, “lokaci na bai yi ba tukuna, amma ku koyaushe lokacin ku ne.
7 the world is not able to hate you, but it hates Me, because I testify concerning it that its works are evil.
Duniya baza ta iya kin ku ba, amma ta ki ni saboda ina fadin cewa ayyukanta ba su da kyau.
8 You—go up to this celebration; I do not yet go up to this celebration, because My time has not yet been fulfilled”;
Ku ku je wurin idin, ni ba zan je wurin idin ba domin lokacina bai yi ba tukuna.
9 and saying these things to them, He remained in Galilee.
Bayan da ya gaya masu wadannan abubuwa, ya tsaya a cikin Gallili.
10 And when His brothers went up, then also He Himself went up to the celebration, not openly, but as in secret;
Amma bayan da 'yan'uwansa su ka tafi wurin idin shi ma ya tafi, amma a asirce ba a fili ba.
11 the Jews, therefore, were seeking Him in the celebration, and said, “Where is that One?”
Saboda Yahudawa suna neman sa a wurin idin, su na cewa “Ina yake?”
12 And there was much murmuring about Him among the multitudes, some indeed said, “He is good”; and others said, “No, but He leads the multitude astray”;
Akwai maganganu dayawa a kansa cikin taron. Wadansu suna cewa, “shi mutumin kirki ne.” Wadansu kuma suna cewa,”A'a yana karkatar da hankalin jama'a.”
13 no one, however, was speaking freely about Him, through fear of the Jews.
Amma duk da haka ba wanda ya yi magana a fili a kansa saboda suna jin tsoron Yahudawa.
14 And it being now the middle of the celebration, Jesus went up to the temple, and He was teaching,
Sa'anda aka kai rabin idin, sai Yesu ya shiga cikin haikali ya fara koyarwa.
15 and the Jews were wondering, saying, “How has this One known letters—having not learned?”
Yahudawa suna mamaki suna cewa,”Yaya aka yi wannan mutum ya sami ilimi dayawa haka? Shi kuwa bai je makaranta ba.”
16 Jesus answered them and said, “My teaching is not Mine, but His who sent Me;
Yesu ya ba su amsa ya ce,”Koyarwata ba tawa ba ce, amma ta wanda ya aiko ni ce.”
17 if anyone may will to do His will, he will know concerning the teaching, whether it is of God, or—[if] I speak from Myself.
Idan wani yana so ya yi nufinsa, za ya gane koyarwannan ko daga wurin Allah ta zo, ko ko tawa ce ta kaina.
18 He who is speaking from himself seeks his own glory, but he who is seeking the glory of him who sent him, this one is true, and unrighteousness is not in him;
Ko wanene yake maganar kansa, yana neman darajar kansa kenan, amma ko wanene ya nemi darajar wanda ya aiko ni, wannan mutum mai gaskiya ne, babu rashin adalci a cikin sa.
19 has not Moses given you the Law? And none of you does the Law; why do you seek to kill Me?”
Ba Musa ya baku dokoki ba? Amma duk da haka ba mai aikata dokokin. Me yasa ku ke so ku kashe ni?
20 The multitude answered and said, “You have a demon, who seeks to kill You?”
Taron suka ba shi amsa, “Ka na da aljani. Wanene yake so ya kashe ka?”
21 Jesus answered and said to them, “I did one work, and you all wonder,
Yesu ya amsa ya ce masu, “Nayi aiki daya, dukan ku kuna mamaki da shi.
22 because of this, Moses has given you the circumcision—not that it is of Moses, but of the fathers—and on a Sabbath you circumcise a man;
Musa ya baku kaciya, (ba kuwa daga Musa take ba, amma daga kakannin kakanni ta ke), kuma a ranar Asabar kukan yi wa mutum kaciya.
23 if a man receives circumcision on a Sabbath that the Law of Moses may not be broken, are you angry with Me that I made a man all whole on a Sabbath?
Idan mutum ya karbi kaciya ranar Asabar, domin kada a karya dokar Musa, don me kuka ji haushi na saboda na mai da mutum lafiyayye sarai ranar Asabar?
24 Do not judge according to appearance, but the righteous judgment judge.”
Kada ku yi shari'a ta ganin ido, amma ku yi shari'a mai adalci.”
25 Certain, therefore, of the Jerusalemites said, “Is this not He whom they are seeking to kill?
Wadansun su daga Urushalima suka ce, “wannan ba shine wannan da suke nema su kashe ba?”
26 And behold, He speaks freely, and they say nothing to Him; did the rulers truly know that this is the Christ?
Kuma duba, yana magana a fili, sannan ba wanda ya ce da shi komai. Ba zai yiwu ba mahukunta su sani cewa wannan Kristi ne, ko ba haka ba?
27 But this One—we have known where He is from; and the Christ, when He comes, no one knows where He is from.”
da haka, mun san inda wannan mutum ya fito. Amma sa'anda Kristi za ya zo, ba wanda zai san inda ya fito.”
28 Jesus cried, therefore, in the temple, teaching and saying, “You have both known Me, and you have known from where I am; and I have not come of Myself, but He who sent Me is true, whom you have not known;
Yesu yayi magana da karfi a haikali, yana koyarwa ya na cewa, “Kun san ni kuma kun san inda na fito. Ban zo domin kaina ba, amma wanda ya aiko ni mai gaskiya ne, ku kuwa baku san shi ba.
29 and I have known Him, because I am from Him, and He sent Me.”
Ni na san shi domin daga wurinsa na fito, kuma shine ya aiko ni.”
30 They were seeking, therefore, to seize Him, and no one laid the hand on Him, because His hour had not yet come,
Suna kokari su kama shi, amma ba wanda ya iya sa masa hannu domin sa'arsa ba ta yi ba tukuna.
31 and many out of the multitude believed in Him and said, “The Christ—when He may come—will He do more signs than these that this One did?”
Duk da haka wadansu dayawa a cikin taron suka bada gaskiya gare shi suka ce,”Sa'anda Kristi ya zo, zai yi alamu fiye da wadanda wannan mutum ya yi?”
32 The Pharisees heard the multitude murmuring these things concerning Him, and the Pharisees and the chief priests sent officers that they may take Him;
Farisawa suka ji tattarmukan suna yin rada a kan wadannan abubuwa game da Yesu, Sai manyan malamai da Farisawa su ka aika jami'ai su kama shi.
33 Jesus, therefore, said to them, “Yet a short time I am with you, and I go away to Him who sent Me;
Sa'annan Yesu yace ma su,” jimawa kadan ina tare ku, sa'annan in tafi wurin wanda ya aiko ni.
34 you will seek Me, and you will not find; and where I am, you are not able to come.”
Za ku neme ni ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba.”
35 The Jews, therefore, said among themselves, “To where is this One about to go that we will not find Him? Is He about to go to the dispersion of the Greeks, and to teach the Greeks?
Yahudawa fa su ka cewa junan su, “Ina wannan mutum zai je inda ba za mu iya samun sa ba? Ko za ya tafi wurin Helinawa na warwatsuwa ya koyawa Helinawa?
36 What is this word that He said, You will seek Me, and you will not find? And, Where I am, you are not able to come?”
Wace kalma ya ke fadi haka, 'za ku neme ni amma ba za ku same ni ba; inda na tafi, ba za ku iya zuwa ba'?”
37 And in the last, the great day of the celebration, Jesus stood and cried, saying, “If anyone thirsts, let him come to Me and drink;
To a rana ta karshe, babbar rana ta idin, Yesu ya mike ya yi magana da karfi cewa, “Idan kowa yana jin kishi, ya zo wuri na ya sha.
38 he who is believing in Me, according as the Writing said, Rivers of living water will flow out of his belly”;
Shi wanda ya bada gaskiya gare ni kamar yadda nassi ya fadi, daga cikin sa rafukan ruwa na rai za su bulbulo.”
39 and this He said of the Spirit, which those believing in Him were about to receive; for not yet was the Holy Spirit, because Jesus was not yet glorified.
Amma ya fadi haka a kan Ruhu, wanda wadanda suka bada gaskiya gare shi za su karba; ba a ba da Ruhun ba tukuna, saboda ba a rigaya an daukaka Yesu ba.
40 Many, therefore, out of the multitude, having heard the word, said, “This is truly the Prophet”;
Wadansu a cikin taron, sa'anda suka ji wadannan kalmomi, suka ce, “Wannan lallai annabi ne.”
41 others said, “This is the Christ”; and others said, “Why, does the Christ come out of Galilee?
Wadansu suka ce, “Wannan Almasihu ne.” Amma wadansu suka ce, “Almasihu zai fito daga Gallili ne?
42 Did the Writing not say that out of the seed of David, and from Beth-Lehem—the village where David was—the Christ comes?”
Ba nassi ya ce Almasihu zai fito daga cikin dangin Dauda daga Baitalami ba, daga kauyen da Dauda ya fito?”
43 A division, therefore, arose among the multitude because of Him.
Sai aka sami rabuwa a cikin taron saboda shi.
44 And certain of them were willing to seize Him, but no one laid hands on Him;
Da wadansun su sun kama shi, amma ba wanda ya sa masa hannu.
45 the officers came, therefore, to the chief priests and Pharisees, and they said to them, “Why did you not bring Him?”
Sa'annan jami'an suka dawo wurin manyan Fristoci da Farisawa, wadanda suka ce,” me yasa ba ku kawo shi ba?”
46 The officers answered, “Never so spoke man—as this Man.”
Jami'an su ka amsa, “Ba mutumin da ya taba yin magana kamar haka.”
47 The Pharisees, therefore, answered them, “Have you also been led astray?
Farisawa suka amsa masu, “kuma an karkatar da ku?
48 Did anyone out of the rulers believe in Him? Or out of the Pharisees?
Ko wani daga cikin mahukunta ya bada gaskiya gare shi, ko kuwa daga cikin Farisawa?
49 But this multitude, that is not knowing the Law, is accursed.”
Amma wannan taro da basu san shari'a ba, la'anannu ne.”
50 Nicodemus says to them—he who came by night to Him—being one of them,
Nikodimus ya ce masu, (shi wanda ya zo wurin Yesu da, daya daga cikin Farisawa),
51 “Does our law judge the Man, if it may not hear from Him first, and know what He does?”
“Ko shari'armu bata hana hukunta mutum ba, sai ta ji daga gare shi ta kuma san abin da ya aikata ba?”
52 They answered and said to him, “Are you also out of Galilee? Search and see that a prophet has not risen out of Galilee”; [[
Suka amsa masa suka ce,”kai ma daga Galili ka fito? Ka yi bincike ka gani ba annanbin da zai fito daga Galili.”
53 and each one went on to his house, but Jesus went on to the Mount of Olives.
Daga nan sai kowa ya tafi gidansa.

< John 7 >