< John 11 >

1 And there was a certain one ailing, Lazarus, from Bethany, of the village of Mary and Martha her sister—
To wani mutum mai suna Li'azaru, yayi rashin lafiya. Shi mutumin Baitanya ne, wato kauyen su Maryamu da 'yar'uwarta Matta.
2 and it was Mary who anointed the LORD with ointment, and wiped His feet with her hair, whose brother Lazarus was ailing—
Wato wannan Maryamu da ta shafe Ubangiji da mur ta kuma share masa kafafunsa da gashin kanta, wadda dan'uwanta Li'azaru ke rashin lafiya.
3 therefore the sisters sent to Him, saying, “Lord, behold, he whom You cherish is ailing”;
'Yan'uwannan mata suka aika sako wurin yesu, cewa, “Ubangiji, duba, shi wanda kake kauna yana rashin lafiya”.
4 and Jesus having heard, said, “This ailment is not to death, but for the glory of God, that the Son of God may be glorified through it.”
Da Yesu ya ji, sai ya ce “Wannan ciwo ba zai kai ga mutuwa ba, amma domin daukakar Allah ne, domin Dan Allah ya sami daukaka tawurin ta”.
5 And Jesus was loving Martha, and her sister, and Lazarus,
Yesu yana kaunar Matta, da 'yar'uwarta da Li'azaru.
6 when, therefore, He heard that he is ailing, then indeed He remained in the place in which He was two days,
Da yaji cewa Li'azaru na rashin lafiya, sai ya tsaya kwana biyu a inda ya ke.
7 then after this, He says to the disciples, “We may go to Judea again”;
Bayan haka, sai ya ce wa almajiransa, “Bari mu je Yahudiya kuma.”
8 the disciples say to Him, “Rabbi, the Jews were just seeking to stone You, and again You go there?”
Sai almajiransa suka ce masa, “Mallam, harwayau Yahudaya na neman ka domin su jefe ka da duwatsu, kuma kana son komawa can?”
9 Jesus answered, “Are there not twelve hours in the day? If anyone may walk in the day, he does not stumble, because he sees the light of this world;
Yesu ya amsa, “Ba sa'a goma sha biyu ce ta haske a rana guda ba? Idan mutum ya yi tafiya da rana, ba za ya yi tuntube ba, domin yana gani ta wurin hasken wannan duniya.
10 and if anyone may walk in the night, he stumbles, because the light is not in him.”
Amma idan mutum ya yi tafiya chikin dare, za ya yi tuntube domin haske ba ya tare da shi.
11 He said these things, and after this He says to them, “Our friend Lazarus has fallen asleep, but I go on that I may awake him”;
Ya fadi wadannan al'amura, kuma bayan wadannan abubuwa, sai ya ce masu, “Abokinmu Li'azaru ya yi barci, amma zan je don In tashe shi daga barci”.
12 therefore His disciples said, “Lord, if he has fallen asleep, he will be saved”;
Sai almajirai suka ce masa, “Ubangiji, idan barci yake yi, ai za ya farka.”
13 but Jesus had spoken about his death, but they thought that He speaks about the repose of sleep.
Yesu kuwa ya yi maganar mutuwar Li'azaru ne, amma su suna tsammani yana magana akan barci ne na hutu.
14 Then, therefore, Jesus said to them freely, “Lazarus has died;
Sai Yesu ya yi masu bayani cewa, “Li'azaru ya mutu.
15 and I rejoice, for your sake (that you may believe), that I was not there; but we may go to him”;
Ina farinchiki domin ku, da bani a wurin domin ku gaskata. Bari mu je wurinsa.”
16 therefore Thomas, who is called Didymus, said to the fellow-disciples, “We may go—we also, that we may die with Him,”
Toma wanda ake kira Dan tagwaye, ya ce wa sauran almajirai, “Bari mu tafi domin mu mutu tare da Yesu.”
17 Jesus, therefore, having come, found him having already been four days in the tomb.
Da Yesu ya iso, sai ya tarar cewa Li'azaru ya rigaya ya yi kwana hudu a kabari.
18 And Bethany was near to Jerusalem, about fifteen stadia off,
Baitanya kuma tana kusa da Urushalima, 'yar tafiya marar nisa ce a tsakanin su.
19 and many of the Jews had come to Martha and Mary, that they might comfort them concerning their brother;
Yahudawa dayawa sun zo wurin Maryamu da Matta domin su yi masu ta'aziyar mutuwar dan'uwansu.
20 Martha, therefore, when she heard that Jesus comes, met Him, and Mary kept sitting in the house.
Da Matta ta ji cewa Yesu na zuwa, sai ta tafi domin ta same shi, amma Maryamu na zamne a cikin gida.
21 Martha, therefore, said to Jesus, “Lord, if You had been here, my brother had not died;
Matta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan tare da mu, da dan'uwana baya mutu ba”.
22 but even now, I have known that whatever You may ask of God, God will give to You”;
Ko yanzu na san cewa duk abinda ka roka a wurin Allah, za ya ba ka.
23 Jesus says to her, “Your brother will rise again.”
Yesu ya ce mata, “Dan'uwanki za ya rayu kuma.
24 Martha says to Him, “I have known that he will rise again in the resurrection in the last day”;
Sai Matta ta ce masa, “Na san zaya rayu kuma a tashin mattatu na ranar karshe.”
25 Jesus said to her, “I AM the resurrection, and the life; he who is believing in Me, even if he may die, will live;
Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu, ni ne kuma rai; wanda ya bada gaskiya gare ni, ko ya mutu, za ya rayu;
26 and everyone who is living and believing in Me will not die—throughout the age; (aiōn g165)
Kuma duk wanda yake raye, ya kuma bada gaskiya gare ni, ba zai mutu ba dadai. Kin gaskata da wannan?” (aiōn g165)
27 do you believe this?” She says to Him, “Yes, Lord, I have believed that You are the Christ, the Son of God, who is coming into the world.”
Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, Na gaskata cewa kaine Almasihu, Dan Allah, wanda ke zuwa duniya.
28 And having said these things, she went away, and called Mary her sister privately, saying, “The Teacher is present, and calls you”;
Sa'adda ta fadi haka, sai ta koma ta kira yar'uwarta Maryamu gefe guda. Ta ce, “mallam ya iso, kuma yana kiran ki.”
29 she, when she heard, rises up quickly, and comes to Him;
Da ta ji haka, sai ta tashi da sauri ta tafi wurin sa.
30 and Jesus had not yet come into the village, but was in the place where Martha met Him;
Yesu bai rigaya ya shiga kauyen ba, yana nan inda Matta ta zo ta same shi.
31 the Jews, therefore, who were with her in the house, and were comforting her, having seen Mary that she rose up quickly and went forth, followed her, saying, “She goes away to the tomb, that she may weep there.”
Da Yahudawan nan dake tare da Maryamu, wato wadannan da suka zo mata ta'aziya, suka ga ta fita daga chikin gida da sauri, sai suka bi ta, suna tsammanin cewa ta tafi ta yi kuka ne a kabari.
32 Mary, therefore, when she came where Jesus was, having seen Him, fell at His feet, saying to Him, “Lord, if You had been here, my brother had not died”;
Da Maryamu ta kai inda Yesu ya ke, sai ta fadi gaban sawayensa, ta ce, “Ubangiji, inda kana tare da mu, da dan'uwana bai mutu ba”.
33 Jesus, therefore, when He saw her weeping, and the Jews who came with her weeping, groaned in the spirit, and troubled Himself, and He said,
Da Yesu ya gan ta tana kuka, da wadannan Yahudawa da suka bi ta, sai ya yi juyayi a ruhu ya damu kuma;
34 “Where have you laid him?” They say to Him, “Lord, come and see”;
sai ya ce, “A ina kuka kwantar da shi?” Sai suka ce masa, “Ubangiji, zo ka gani.”
35 Jesus wept.
Yesu ya yi kuka.
36 The Jews, therefore, said, “Behold, how He was cherishing him!”
Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake kaunar Li'azaru!”
37 And certain of them said, “Was not this One, who opened the eyes of the blind man, also able to cause that this one might not have died?”
Amma wadansun su suka ce, “Shi wannan mutum da ya iya ba makaho ganin gari, da bai iya hana wannan mutum mutuwa ba?
38 Jesus, therefore, again groaning in Himself, comes to the tomb, and it was a cave, and a stone was lying on it,
Yesu yana cikin juyayi kuma a cikin kansa, sai ya tafi kabarin. Kabarin a kogo ne an kuma rufe bakinsa da dutse.
39 Jesus says, “Take away the stone”; the sister of him who has died—Martha—says to Him, “Lord, he already stinks, for he is four days dead”;
Sai Yesu ya ce, “A kawar da dutsen.” Matta yar'uwar Li'azaru wanda ya mutu, ta ce wa Yesu, “Ubangiji, Yanzu jikin ya ruba domin ya kai kwana hudu da mutuwa”.
40 Jesus says to her, “Did I not say to you that if you may believe, you will see the glory of God?”
Yesu ya ce mata, “Ba na ce maki idan kin gaskata za ki ga daukakar Allah ba?”
41 Therefore they took away the stone where the dead was laid, and Jesus lifted His eyes upwards, and said, “Father, I thank You that You heard Me;
Sai suka kawar da dutsen. Yesu ya daga idanunsa ya ce, “Uba, na gode maka domin kana ji na.”
42 and I knew that You always hear Me, but because of the multitude that is standing by, I said [it], that they may believe that You sent Me.”
Na san kana ji na a kowane lokaci, amma domin wannan taro da ke tsaye kewaye da ni nike wannan magana, domin su bada gaskiya cewa kaine ka aiko ni.”
43 And saying these things, He cried out with a loud voice, “Lazarus, come forth!”
Bayan ya yi wannan magana, sai ya daga murya ya ce, “Li'azaru, ka fito!”
44 And he who died came forth, feet and hands being bound with grave-clothes, and his face was bound around with a napkin; Jesus says to them, “Loose him, and permit to go.”
Sai mataccen ya fito; kafafunsa da hannayensa na daure da likkafani, fuskarsa kuma na lullube da tsumma. Yesu ya ce masu, “Ku kwance shi, ya tafi”.
45 Many, therefore, of the Jews who came to Mary, and beheld what Jesus did, believed in Him;
To dayawa daga cikin yahudawan da suka zo wurin Maryamu suka kuma ga abinda Yesu ya yi, suka gaskata da shi;
46 but certain of them went away to the Pharisees, and told them what Jesus did;
amma wadansu suka koma wurin farisawa suka fada masu abubuwan da Yesu ya yi.
47 the chief priests, therefore, and the Pharisees, gathered together [the] Sanhedrin and said, “What may we do? Because this Man does many signs?
Sai manyan firistoci da farisawa suka tara majalisa wuri guda, suka ce, “menene za mu yi?” Mutumin nan yana alamu masu yawa.
48 If we may leave Him alone thus, all will believe in Him; and the Romans will come, and will take away both our place and nation.”
Idan mun kyale shi haka, duka za su gaskata da shi; Romawa za su zo su kwace wurinmu da al'ummar mu.
49 And a certain one of them, Caiaphas, being chief priest of that year, said to them, “You have not known anything,
Duk da haka, wani daga cikin su wato, Kayafas wanda shine babban firist a wannan shekara, ya ce da su, “baku san komai ba”.
50 nor reason that it is good for us that one man may die for the people, and not the whole nation perish.”
Ba ku lura cewa ya fi maku kyau mutum daya ya mutu domin mutane, a maimakon dukan al'umma ta hallaka.”
51 And he did not say this of himself, but being chief priest of that year, he prophesied that Jesus was about to die for the nation,
Ya fadi wannan ne ba don kansa ba, amma sabo da shine babban firist, ya yi anabci ne cewa ya kamata Yesu ya mutu domin al'ummar;
52 and not for the nation only, but that also the children of God, who have been scattered abroad, He may gather together into one.
kuma ba don alummar kawai ba, amma domin a tattara 'ya'yan Allah da suke warwatse ko'ina wuri daya.
53 From that day, therefore, they took counsel together that they may kill Him;
Tun daga wannan rana suka fara neman hanyar da za su kashe Yesu.
54 Jesus, therefore, was no longer freely walking among the Jews, but went away from there into the region near the wilderness, to a city called Ephraim, and there He tarried with His disciples.
Tun daga nan Yesu ya dena tafiya a sarari chikin Yahudawa, amma sai ya koma wani yanki kusa da jeji a wani gari da ake kira Ifraimu. A can kuma ya zamna da almajiransa.
55 And the Passover of the Jews was near, and many went up to Jerusalem out of the country before the Passover, that they might purify themselves;
Idin ketarewa na Yahudawa ya yi kusa, da yawa sun tafi Urushalima daga yankin kasar kamin ranar idi domin su tsarkake kan su.
56 therefore they were seeking Jesus and said with one another, standing in the temple, “What appears to you—that He may not come to the celebration?”
Suka shiga neman Yesu, suna magana da junan su yayin da suke tsaitsaye a haikali, cewa “me kuke tunani? Ba za ya zo idin bane?”
57 And both the chief priests and the Pharisees had given a command, that if anyone may know where He is, he may show [it], so that they may seize Him.
Babban firist da farisawa sun rigaya sun ba da umurni cewa duk inda aka ga Yesu a zo a shaida domin su kama shi.

< John 11 >