< Job 9 >

1 And Job answers and says:
Sai Ayuba ya amsa,
2 “Truly I have known that [it is] so, But how is man righteous with God?
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 If he delights to strive with Him—He does not answer him one of a thousand.
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 Wise in heart and strong in power—Who has hardened toward Him and is at peace?
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
5 Who is removing mountains, And they have not known, Who has overturned them in His anger.
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
6 Who is shaking earth from its place, And its pillars move themselves.
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
7 Who is commanding to the sun, and it does not rise, And the stars He seals up.
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
8 Stretching out the heavens by Himself, And treading on the heights of the sea,
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
9 Making the Great Bear, Orion, and the Pleiades, And the inner chambers of the south.
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
10 Doing great things until there is no searching, And wonderful, until there is no numbering.
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
11 Behold, He goes over by me, and I do not see, And He passes on, and I do not attend to it.
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
12 Behold, He snatches away, who brings it back? Who says to Him, What [are] You doing?
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
13 God does not turn back His anger, Proud helpers have bowed under Him.
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
14 How much less do I answer Him? Choose out my words with Him?
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15 Whom, though I were righteous, I do not answer, For my judgment I make supplication.
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16 Though I had called and He answers me, I do not believe that He gives ear [to] my voice.
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17 Because He bruises me with a storm, And has multiplied my wounds for nothing.
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18 He does not permit me to refresh my spirit, But fills me with bitter things.
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19 If of power, behold, the Strong One; And if of judgment—who convenes me?
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20 If I am righteous, my mouth declares me wicked; [If] I am perfect, it declares me perverse.
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21 I am perfect; I do not know my soul, I despise my life.
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
22 It is the same thing, therefore I said, He is consuming the perfect and the wicked.
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
23 If a scourge puts to death suddenly, He laughs at the trial of the innocent.
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
24 Earth has been given Into the hand of the wicked. He covers the faces of her judges, If not—where, who [is] he?
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
25 My days have been swifter than a runner, They have fled, they have not seen good,
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
26 They have passed on with ships of reed, As an eagle darts on food.
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
27 Though I say, I forget my talking, I forsake my corner, and I brighten up!
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
28 I have been afraid of all my griefs, I have known that You do not acquit me.
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
29 I become wicked; why [is] this? I labor [in] vain.
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
30 If I have washed myself with snow-water, And purified my hands with soap,
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
31 Then You dip me in corruption, And my garments have detested me.
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
32 But if a man like myself—I answer Him, We come together into judgment.
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
33 If there were a mediator between us, He places his hand on us both.
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
34 He turns aside His rod from off me, And His terror does not make me afraid,
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
35 I speak, and do not fear Him, but I am not right with myself.”
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.

< Job 9 >