< Job 8 >

1 And Bildad the Shuhite answers and says:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 “Until when do you speak these things? And a strong wind—sayings of your mouth?
“Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
3 Does God pervert judgment? And does the Mighty One pervert justice?
Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
4 If your sons have sinned before Him, And He sends them away, By the hand of their transgression,
Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
5 If you seek for God early, And make supplication to the Mighty,
Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
6 If you [are] pure and upright, Surely now He wakes for you, And has completed The habitation of your righteousness.
in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
7 And your beginning has been small, And your latter end is very great.
Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
8 For inquire, please, of a former generation, And prepare for a search of their fathers,
“Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
9 For we [are] of yesterday, and we do not know, For our days [are] a shadow on earth.
gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
10 Do they not show you—speak to you, And from their heart bring forth words?
Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
11 Does a rush rise without a marsh? A reed increase without water?
Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
12 While it [is] in its budding—uncropped, Even before any herb it withers.
Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
13 So [are] the paths of all forgetting God, And the hope of the profane perishes,
Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
14 Whose confidence is loathsome, And the house of a spider his trust.
Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
15 He leans on his house—and it does not stand, He takes hold on it—and it does not abide.
Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
16 He [is] green before the sun, And over his garden his branch goes out.
Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
17 His roots are wrapped by a heap, He looks for a house of stones.
shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
18 If [one] destroys him from his place, Then it has feigned concerning him, I have not seen you!
Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
19 Behold, this [is] the joy of His way, And from the dust others spring up.
Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
20 Behold, God does not reject the perfect, Nor takes hold on the hand of evildoers.
“Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
21 While He fills your mouth with laughter, And your lips with shouting,
Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
22 Those hating you put on shame, And the tent of the wicked is not!”
Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”

< Job 8 >