< Job 6 >
1 And Job answers and says:
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 “O that my provocation were thoroughly weighed, And my calamity in balances They would lift up together!
“Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
3 For now it is heavier than the sands of the sea, Therefore my words have been rash.
Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
4 For arrows of the Mighty [are] with me, Whose poison is drinking up my spirit. Terrors of God array themselves [for] me!
Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
5 Does a wild donkey bray over tender grass? Does an ox low over his provender?
Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
6 Is an insipid thing eaten without salt? Is there sense in the drivel of dreams?
Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
7 My soul is refusing to touch! They [are] as my sickening food.
Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
8 O that my request may come, That God may grant my hope!
“Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
9 That God would please—and bruise me, Loose His hand and cut me off!
wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
10 And yet it is my comfort (And I exult in pain—He does not spare), That I have not hidden The sayings of the Holy One.
Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
11 What [is] my power that I should hope? And what [is] my end that I should prolong my life?
“Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
12 Is my strength the strength of stones? Is my flesh bronze?
Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
13 Is my help not with me, And substance driven from me?
Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
14 To a despiser of his friends [is] shame, And the fear of the Mighty he forsakes.
“Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
15 My brothers have deceived as a brook, As a stream of brooks they pass away.
Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
16 That are black because of ice, By them snow hides itself.
kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
17 By the time they are warm they have been cut off, By its being hot they have been Extinguished from their place.
amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
18 The paths turn aside of their way, They ascend into emptiness, and are lost.
Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
19 Passengers of Tema looked expectingly, Travelers of Sheba hoped for them.
Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
20 They were ashamed that one has trusted, They have come to it and are confounded.
Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
21 Surely now you have become the same! You see a downfall, and are afraid.
Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
22 Is it because I said, Give to me? And, By your power bribe for me?
Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
23 And, Deliver me from the hand of an adversary? And, Ransom me from the hand of terrible ones?
ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
24 Show me, and I keep silent, And what I have erred, let me understand.
“Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
25 How powerful have been upright sayings, And what reproof from you reproves?
Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
26 For reproof—do you reckon words? And for wind—sayings of the desperate?
Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
27 You cause anger to fall on the fatherless, And are strange to your friend.
Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
28 And now, please, look on me, Even to your face do I lie?
“Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
29 Please turn back, let it not be perverseness, Indeed, turn back again—my righteousness [is] in it.
Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
30 Is there perverseness in my tongue? Does my palate not discern calamity?”
Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?