< Job 40 >
1 And YHWH answers Job and says:
Ubangiji ya ce wa Ayuba,
2 “Is the striver with the Mighty instructed? The reprover of God, let him answer it.”
“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
3 And Job answers YHWH and says:
Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
4 “Behold, I have been vile, What do I return to You? I have placed my hand on my mouth.
“Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
5 I have spoken once, and I do not answer, And twice, and I do not add.”
Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
6 And YHWH answers Job out of the whirlwind and says:
Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
7 “Now gird your loins as a man, I ask you, and you cause Me to know.
“Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
8 Do you also make My judgment void? Do you condemn Me, That you may be righteous?
“Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
9 And do you have an arm like God? And do you thunder with a voice like His?
Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
10 Now put on excellence and loftiness, Indeed, put on splendor and beauty.
Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
11 Scatter abroad the wrath of your anger, And see every proud one, and make him low.
Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
12 See every proud one—humble him, And tread down the wicked in their place.
Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
13 Hide them in the dust together, Bind their faces in secret.
Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
14 And even I praise you, For your right hand gives salvation to you.
Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
15 Now behold, behemoth, That I made with you: He eats grass as an ox.
“Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
16 Now behold, his power [is] in his loins, And his strength in the muscles of his belly.
Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
17 He bends his tail as a cedar, The sinews of his thighs are wrapped together,
Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
18 His bones [are] tubes of bronze, His bones [are] as a bar of iron.
Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
19 He [is] a beginning of the ways of God, His Maker [alone] brings His sword near;
Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
20 For mountains bear food for him, And all the beasts of the field play there.
Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
21 He lies down under shades, In a secret place of reed and marsh.
Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
22 Shades cover him, [with] their shadow, Willows of the brook cover him.
Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
23 Behold, a flood oppresses—he does not hurry, He is confident though Jordan Comes forth to his mouth.
Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
24 Does [one] take him by his eyes? Does [one] pierce the nose with snares?”
Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?