< Job 4 >
1 And Eliphaz the Temanite answers and says:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 “Has one tried a word with you? You are weary! And who is able to keep in words?
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
3 Behold, you have instructed many, And feeble hands you make strong.
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
4 Your words raise up the stumbling one, And you strengthen bowing knees.
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5 But now, it comes to you, And you are weary; It strikes to you, and you are troubled.
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6 Is your reverence not your confidence? Your hope—the perfection of your ways?
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
7 Now remember, Who, being innocent, has perished? And where have the upright been cut off?
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8 As I have seen—plowers of iniquity, And sowers of misery, reap it!
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9 From the breath of God they perish, And from the spirit of His anger [are] consumed.
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
10 The roaring of a lion, And the voice of a fierce lion, And teeth of young lions have been broken.
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
11 An old lion is perishing without prey, And the whelps of the lioness separate.
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
12 And a thing is secretly brought to me, And my ear receives a little of it.
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
13 In thoughts from visions of the night, In the falling of deep sleep on men,
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
14 Fear has met me, and trembling, And the multitude of my bones caused to fear.
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
15 And a spirit passes before my face, The hair of my flesh stands up;
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16 It stands, and I do not discern its aspect, A likeness [is] before my eyes, Silence! And I hear a voice:
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17 Is mortal man more righteous than God? Is a man cleaner than his Maker?
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
18 Behold, He puts no credence in His servants, Nor sets praise in His messengers.
In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
19 Also—the inhabitants of houses of clay (Whose foundation [is] in the dust, They bruise them before a moth).
to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
20 From morning to evening are beaten down, Without any regarding, they perish forever.
Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
21 Has their excellence not been removed with them? They die, and not in wisdom!”
Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’