< Job 35 >
1 And Elihu answers and says:
Sai Elihu ya ce,
2 “Have you reckoned this for judgment [when] you have said, My righteousness [is] more than God’s?
“Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
3 For you say, What does it profit You? What do I profit from my sin?
Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
4 I return words, and your friends with you,
“Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
5 Behold attentively the heavens—and see, And behold the clouds, They have been higher than you.
Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
6 If you have sinned, what do you do against Him? And your transgressions have been multiplied, What do you do to Him?
In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
7 If you have been righteous, What do you give to Him? Or what does He receive from your hand?
In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
8 For a man like yourself [is] your wickedness, And for a son of man your righteousness.
Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
9 Because of the multitude of oppressions They cause to cry out, They cry because of the arm of the mighty.
“Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
10 And none said, Where [is] God my Maker? Giving songs in the night,
Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
11 Teaching us more than the beasts of the earth, Indeed, He makes us wiser than the bird of the heavens.
wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
12 There they cry, and He does not answer, Because of the pride of evildoers.
Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
13 Surely God does not hear vanity, And the Mighty does not behold it.
Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
14 Indeed, though you say you do not behold Him, Judgment [is] before Him, and stays for Him.
Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
15 And now, because there is not, He has appointed His anger, And He has not known in great extremity.
Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
16 And Job opens his mouth [with] vanity, He multiplies words without knowledge.”
Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”