< Job 34 >

1 And Elihu answers and says:
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 “Hear, O wise men, my words, And, O knowing ones, give ear to me.
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 For the ear tries words, And the palate tastes to eat.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Let us choose judgment for ourselves, Let us know among ourselves what [is] good.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 For Job has said, I have been righteous, And God has turned aside my right,
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 Against my right do I lie? My arrow [is] mortal—without transgression.
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 Who [is] a man like Job? He drinks scoffing like water,
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 And he has traveled for company With workers of iniquity, So as to go with men of wickedness.
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 For he has said, It does not profit a man When he delights himself with God.
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 Therefore, O men of heart, listen to me; Far be it from God to do wickedness, And [from] the Mighty to do perverseness,
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 For He repays the work of man to him, And according to the path of each He causes him to find.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 Indeed, truly, God does not do wickedly, And the Mighty does not pervert judgment.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 Who has inspected for Himself the earth? And who has placed all the habitable world?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 If He sets His heart on him, [If] He gathers His Spirit and His breath to Himself,
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 All flesh expires together, And man returns to dust.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 And if [there is] understanding, hear this, Give ear to the voice of my words.
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 Indeed, does one hating justice govern? Or do you condemn the Most Just?
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 Who has said to a king, Worthless, To princes, Wicked?
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 That has not accepted the person of princes, Nor has known the rich before the poor, For all of them [are] a work of His hands.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 [In] a moment they die, And at midnight people shake, And they pass away, And they remove the mighty without hand.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 For His eyes [are] on the ways of each, And He sees all his steps.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 There is no darkness nor death-shade, For workers of iniquity to be hidden there;
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 For He does not permit man anymore, To go to God in judgment,
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 He breaks the mighty—no searching! And He appoints others in their stead.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 Therefore He knows their works, And He has overturned by night, And they are bruised.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 As wicked He has struck them, In the place of beholders.
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 Because that against right They have turned aside from after Him, And have considered none of His ways,
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 To cause to come to Him The cry of the poor, And He hears the cry of the afflicted.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 And He gives rest, and who makes wrong? And hides the face, and who beholds it? And in reference to a nation and to a man, [It is] the same.
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 From the reigning of a profane man, From the snares of a people;
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 For has any said to God: I have taken away, I do not do corruptly,
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 Besides [that which] I see, You show me, If I have done iniquity—I do not add?
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 Does He repay by you, that you have refused—That you choose, and not I? And what you have known, speak.
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 Let men of heart say to me, And a wise man is listening to me:
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 Job—he does not speak with knowledge, And his words [are] not with wisdom.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 My Father! Let Job be tried—to victory, Because of answers for men of iniquity,
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 For he adds to his sin, He vomits transgression among us, And multiplies his sayings to God.”
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Job 34 >