< Job 33 >
1 “And yet, please, O Job, Hear my speech and give ear [to] all my words.
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 Now behold, I have opened my mouth, My tongue has spoken in the palate.
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 Of the uprightness of my heart [are] my sayings, And my lips have clearly spoken knowledge.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 The Spirit of God has made me, And the breath of the Mighty quickens me.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 If you are able—answer me, Set in array before me—station yourself.
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 Behold, I [am], according to your word, for God, I have also been formed from the clay.
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 Behold, my terror does not frighten you, And my burden on you is not heavy.
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 Surely you have spoken in my ears, And the sounds of words I hear:
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 I [am] pure, without transgression, I [am] innocent, and I have no iniquity.
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 Behold, He develops hindrances against me, He reckons me for an enemy to Him,
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 He puts my feet in the stocks, He watches all my paths.
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 Behold, you have not been righteous [in] this, I answer you, that God is greater than man.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 Why have you striven against Him, When [for] all His matters He does not answer?
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 For once God speaks, and twice (he does not behold it),
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 In a dream—a vision of night, In the falling of deep sleep on men, In slumberings on a bed.
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 Then He uncovers the ear of men, And seals for their instruction,
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 To turn aside man [from] doing, And He conceals pride from man.
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 He keeps back his soul from corruption, And his life from passing away by a dart.
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 And he has been reproved With pain on his bed, And the strife of his bones [is] enduring.
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 And his life has nauseated bread, And his soul desirable food.
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 His flesh is consumed from being seen, And his bones are high, they were not seen!
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 And his soul draws near to the pit, And his life to those causing death.
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 If there is a messenger by him, An interpreter—one of a thousand, To declare for man his uprightness,
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 Then He favors him and says, Ransom him from going down to the pit, I have found an atonement.
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 Fresher [is] his flesh than a child’s, He returns to the days of his youth.
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 He makes supplication to God, And He accepts him. And he sees His face with shouting, And He returns to man His righteousness.
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 [Then] he looks on men and says, I sinned, and I have perverted uprightness, And it has not been profitable to me.
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 He has ransomed my soul From going over into the pit, And my life looks on the light.
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 Behold, God works all these, Twice, [even] three times with man,
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 To bring back his soul from the pit, To be enlightened with the light of the living.
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 Attend, O Job, listen to me, Keep silent, and I speak.
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 If there are words—answer me, Speak, for I have a desire to justify you.
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 If there are not—listen to me, Keep silent, and I teach you wisdom.”
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”