< Job 28 >
1 “Surely there is a source for silver, And a place for the gold they refine;
Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
2 Iron is taken from the dust, And bronze [from] the firm stone.
Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
3 He has set an end to darkness, And he is searching to all perfection, A stone of darkness and death-shade.
Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
4 A stream has broken out from a sojourner, Those forgotten of the foot, They were low, they wandered from man.
Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
5 The earth! Bread comes forth from it, And its under-part is turned like fire.
Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
6 A place of the sapphire [are] its stones, And it has dust of gold.
akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
7 A path—a ravenous bird has not known it, Nor has an eye of the falcon scorched it,
Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
8 Nor have the sons of pride trodden it, The fierce lion has not passed over it.
Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
9 He sent forth his hand against the flint, He overturned mountains from the root.
Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
10 Among rocks, he has cleaved brooks, And his eye has seen every precious thing.
Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
11 He has bound overflowing rivers, And the hidden thing brings out [to] light.
Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
12 And the wisdom—from where is it found? And where [is] this, the place of understanding?
Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
13 Man has not known its arrangement, Nor is it found in the land of the living.
Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
14 The deep has said, It [is] not in me, And the sea has said, It is not with me.
Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
15 Gold is not given for it, Nor is silver weighed—its price.
Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
16 It is not valued with pure gold of Ophir, With precious onyx and sapphire,
Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
17 Gold and crystal do not equal it, Nor [is] its exchange a vessel of fine gold.
Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
18 Corals and pearl are not remembered, The acquisition of wisdom [is] above rubies.
Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
19 The topaz of Cush does not equal it, It is not valued with pure gold.
Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
20 And the wisdom—from where does it come? And where [is] this, the place of understanding?
“To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
21 It has been hid from the eyes of all living. And from the bird of the heavens It has been hidden.
An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
22 Destruction and death have said: With our ears we have heard its fame.
Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
23 God has understood its way, And He has known its place.
Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
24 For He looks to the ends of the earth, He sees under the whole heavens,
Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
25 To make a weight for the wind, And He meted out the waters in measure.
Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
26 In His making for the rain a limit, And a way for the brightness of the voices,
Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
27 Then He has seen and declares it, He has prepared it, and also searched it out,
sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
28 And He says to man: Behold, fear of the Lord, that [is] wisdom, And to turn from evil [is] understanding.”
Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”