< Job 26 >
1 And Job answers and says:
Sai Ayuba ya amsa,
2 “How you have helped the powerless, Saved an arm not strong!
“Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
3 How you have given counsel to the unwise, And made known wise plans in abundance.
Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
4 With whom have you declared words? And whose breath came forth from you?
Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
5 The Rephaim are formed, Also their inhabitants beneath the waters.
“Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
6 Sheol [is] naked before Him, And there is no covering to destruction. (Sheol )
Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol )
7 Stretching out the north over desolation, Hanging the earth on nothing,
Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
8 Binding up the waters in His thick clouds, And the cloud is not burst under them.
Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
9 Taking hold of the face of the throne, Spreading His cloud over it.
Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
10 He has placed a limit on the waters, To the boundary of light with darkness.
ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
11 Pillars of the heavens tremble, And they wonder because of His rebuke.
Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
12 By His power He has quieted the sea, And by His understanding struck the proud.
Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
13 He beautified the heavens by His Spirit, His hand has formed the fleeing serpent.
Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
14 Behold, these [are] the borders of His way, and how little a matter is heard of Him, and who understands the thunder of His might?”
Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”