< Job 17 >

1 “My spirit has been destroyed, My days extinguished—graves [are] for me.
Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
2 If not—mockeries [are] with me. And my eye lodges in their provocations.
Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
3 Now place my pledge with You; Who is he that strikes hand with me?
“Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
4 For You have hidden their heart from understanding, Therefore You do not exalt them.
Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
5 For a portion he shows friendship, And the eyes of his sons are consumed.
In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
6 And He set me up for a proverb of the peoples, And I am a wonder before them.
“Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
7 And my eye is dim from sorrow, And my members—all of them—as a shadow.
Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
8 The upright are astonished at this, and the innocent stirs himself up against the profane.
Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
9 And the righteous lays hold [on] his way, And the clean of hands adds strength.
Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
10 But please return and come in, all of you, And I do not find a wise man among you.
“Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
11 My days have passed by, My plans have been broken off, The possessions of my heart!
Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
12 They appoint night for day, Light [is] near because of darkness.
Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
13 If I wait—Sheol [is] my house, In darkness I have spread out my bed. (Sheol h7585)
In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol h7585)
14 To corruption I have called: You [are] my father. To the worm: My mother and my sister.
In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
15 And where [is] my hope now? Indeed, my hope, who beholds it?
To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
16 You go down [to] the parts of Sheol, If we may rest together on the dust.” (Sheol h7585)
Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol h7585)

< Job 17 >