< Jeremiah 6 >
1 “Strengthen yourselves, sons of Benjamin, From the midst of Jerusalem, And blow a horn in Tekoa, And lift up a flame over Beth-Haccerem, For evil has been seen from the north, And great destruction.
“Ku gudu neman mafaka, mutanen Benyamin! Ku gudu daga Urushalima! Ku busa ƙaho a Tekowa! Ku ba da alama a Bet-Hakkerem! Gama masifa tana zuwa daga arewa, mummunar hallaka ce kuwa.
2 I have cut off the lovely and delicate one, The daughter of Zion.
Zan hallaka Diyar Sihiyona, kyakkyawa da kuma mai laulayi.
3 Shepherds and their droves come to her, They have struck tents by her all around, They have each fed [in] his own station.”
Makiyaya da garkunansu za su taso mata; za su kafa tentunansu kewaye da ita, kowanne yana lura da sashensa.”
4 “Sanctify the battle against her, Rise, and we go up at noon. Woe to us, for the day has turned, For the shades of evening are stretched out,
“Mu shirya don yaƙi da ita! Ku tashi, bari mu fāɗa mata da tsakar rana! Amma, kaito, rana tana fāɗuwa, inuwar yamma kuwa sai ƙaran tsawo take.
5 Rise, and we go up by night, And we destroy her palaces.”
Saboda haka ku tashi, bari mu fāɗa mata da dare mu rurrushe kagaranta!”
6 For thus said YHWH of Hosts: “Cut down her wood, And pour out a mound against Jerusalem, She [is] the city to be inspected, She [is] full of oppression in her midst.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ku sassare itatuwan ku tula ƙasa kewaye da Urushalima. Dole a hukunta wannan birni; saboda ya cika da zalunci.
7 As the digging of a well, is [for] its waters, So she has dug [for] her wickedness, Violence and spoil is heard in her, Sickness and striking [are] continually before My face.
Kamar yadda rijiya takan ba da ruwarta, haka birnin yake da muguntarsa. Ana jin labarin rikici da hallaka a cikinsa; ciwonsa da mikinsa kullum suna a gabana.
8 Be instructed, O Jerusalem, Lest My soul be alienated from you, Lest I make you a desolation, A land [that is] not inhabited.”
Ki ji gargaɗi, ya Urushalima, ko kuwa in juya daga gare ki in mai da ƙasarki kufai don kada wani ya zauna a cikinta.”
9 Thus said YHWH of Hosts: “They surely glean, as a vine, the remnant of Israel, Put your hand back, as a gatherer to the baskets.”
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Bari su yi kalan raguwar Isra’ila a yi kalan sarai yadda ake yi wa inabi; ka sāke miƙa hannunka a kan rassan, kamar mai tattara inabi.”
10 To whom do I speak, and testify, and they hear? Behold, their ear [is] uncircumcised, And they are not able to attend. Behold, a word of YHWH has been to them for a reproach, They do not delight in it.
Ga wa zan yi magana in kuma gargaɗar? Wa zai saurare ni? Kunnuwansu sun toshe don kada su ji. Maganar Ubangiji ta zama abin zargi a gare su; ba sa jin daɗinta.
11 And I have been filled with the fury of YHWH (I have been weary of containing), “To pour [it] on the suckling in the street, And on the assembly of youths together, For even husband with wife are captured, [The] elderly with one full of days,
Amma ina cike da fushin Ubangiji, kuma ba na iya kannewa. “Ka kwararo shi a kan yara a titi da kuma a kan samarin da suka tattaru; za a kama miji da mata a cikinsa, tsofaffi da suka tsufa tukub.
12 And their houses have been turned to others, Fields and wives together, For I stretch out My hand against the inhabitants of the land,” A declaration of YHWH.
Za a ba da gidajensu ga waɗansu, tare da gonakinsu da matansu, sa’ad da na miƙa hannuna gāba da waɗanda suke zama a ƙasar,” in ji Ubangiji.
13 “For from their least to their greatest, Everyone is gaining dishonest gain, And from prophet even to priest, Everyone is dealing falsely,
“Daga ƙarami zuwa babba, dukansu masu haɗama ne don riba; har da annabawa da firistoci, dukansu suna aikata rashin gaskiya.
14 And they heal the breach of the daughter of My people slightly, Saying, Peace, peace! And there is no peace.
Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, ‘Lafiya, Lafiya,’ alhali kuwa ba lafiya.
15 They were ashamed when they did abomination! Indeed, they are not at all ashamed, Indeed, they have not known blushing, Therefore they fall among those falling, In the time I have inspected them, They stumble,” said YHWH.
Suna jin kunyar halinsu na banƙyama? A’a, ba sa jin kunya sam; ba su ma san yadda za su soke kai ba. Saboda haka za su fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za a hamɓarar da su sa’ad da na hukunta su,” in ji Ubangiji.
16 Thus said YHWH: “Stand by the ways and see, and ask for paths of old, Where [is] this—the good way? And go in it, And find rest for yourselves. And they say, We do not go.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba; ku nemi hanyoyin dā, ku tambaya inda hanyar mai kyau take, ku yi tafiya a kanta, za ku kuwa sami hutu wa rayukanku. Amma kun ce, ‘Ba za mu bi ta ba.’
17 And I have raised up watchmen for you, Attend to the voice of the horn. And they say, We do not attend.
Na naɗa muku masu tsaro a kanku na kuma ce, ‘Ku saurari karan ƙaho!’ Amma kuka ce, ‘Ba za mu saurara ba.’
18 Therefore hear, O nations, and know, O congregation, That which [is] on them.
Saboda haka ku, ya al’ummai; ku lura Ya shaidu, abin da zai faru da su.
19 Hear, O earth, behold, I am bringing evil on this people, The fruit of their plans, For they gave no attention to My words, And My law—they kick against it.
Ki ji, ya duniya. Zan kawo masifa a kan waɗannan mutane, sakayyar ƙulle-ƙullensu, domin ba su saurari maganata ba suka kuma ƙi dokata.
20 Why [is] this to Me? Frankincense comes from Sheba, And the sweet cane from a far-off land, Your burnt-offerings [are] not for acceptance, And your sacrifices have not been sweet to Me.”
Babu riba a kawo mini turare daga Sheba ko rake mai zaƙi daga ƙasa mai nisa? Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawa ba; ba na jin daɗin sadakokinku.”
21 Therefore, thus said YHWH: “Behold, I give stumbling blocks to this people, And fathers and sons have stumbled against them together, The neighbor and his friend perish.”
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Zan sa abin tuntuɓe gaban mutanena. Mahaifi da’ya’yansa maza za su yi tuntuɓe a kan juna; maƙwabci da abokansa za su hallaka.”
22 Thus said YHWH: “Behold, a people has come from a north country, And a great nation is stirred up from the sides of the earth.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Duba, sojoji suna zuwa daga ƙasar arewa; babbar al’umma ce ta yunƙuro daga iyakokin duniya.
23 They take hold of bow and javelin, It [is] fierce, and they have no mercy, Their voice sounds as a sea, And they ride on horses, Set in array as a man of war, Against you, O daughter of Zion.”
Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne kuma marasa tausayi. Motsinsu kamar ƙugin teku ne yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa a jere kamar wanda ya yi shirin yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Sihiyona.”
24 We have heard its sound, our hands have been feeble, Distress has seized us, pain as of a travailing woman.
Mun ji labari a kansu, hannuwanmu kuwa suka yi laƙwas. Azaba ta kama mu, zafi kamar na mace mai naƙuda.
25 Do not go forth to the field, And do not walk in the way, For the enemy has a sword, Fear [is] all around.
Kada ku fita zuwa gonaki ko ku yi tafiya a hanyoyi, gama abokin gāba yana da takobi, kuma akwai razana ko’ina.
26 O daughter of my people, Gird on sackcloth, And roll yourself in ashes, Make mourning [as for] an only one, A most bitter lamentation, For the spoiler suddenly comes against us.
Ya mutanena, ku sanya tufafin makoki ku yi birgima a toka; ku yi kuka mai zafi irin wanda akan yi wa ɗa tilo, gama nan da nan mai hallakarwa zai auko mana.
27 “I have given you a watchtower, A fortress among My people, And you know, and have tried their way.
“Na maishe ka mai jarrabawar ƙarfe mutanena ne kuwa ƙarfen, don ka lura ka kuma gwada hanyoyinsu.
28 All of them are turned aside by apostates, Walking slanderously—bronze and iron, All of them are corrupters.
Su duka masu taurinkai ne,’yan tawaye, suna yawo suna baza jita-jita. Su tagulla ne da ƙarfe; dukansu lalatattu ne.
29 The bellows have been burned, The lead has been consumed by fire, A refiner has refined in vain, And the wicked have not been drawn away.
Mazuga yana zuga da ƙarfi don yă ƙone dalma da wuta, amma tacewa yana tafiya a banza; ba a fitar da mugaye.
30 They have called them rejected silver, For YHWH has kicked against them!”
Ana ce da su azurfar da aka ƙi, gama Ubangiji ya ƙi su.”