< Jeremiah 51 >

1 Thus said YHWH: “Behold, I am stirring up against Babylon, And the inhabitants of Leb, My withstanders, A destroying wind,
Ubangiji ya ce, “Ga shi, zan zuga ruhun mai hallakarwa a kan Babilon da mutanen Leb Kamai.
2 And I have sent fanners to Babylon, And they have fanned her, and they empty her land, For they have been against her, All around—in the day of evil.
Zan aika da baƙi zuwa Babilon su casa ta su kuma yi kaca-kaca da ƙasarta; za su yi hamayya da ita a kowane gefe a ranar masifarta.
3 Do not let the treader tread his bow, Nor lift himself up in his coat of mail, Nor have pity on her young men, Devote all her host to destruction.
Kada ku bar maharbi yă ja bakansa, kada kuma ku bari yă sa kayan yaƙinsa. Kada ku rage samarinta, ku hallaka sojojinta ƙaf.
4 And the wounded have fallen in the land of the Chaldeans, And the pierced-through in her streets.
Za su fāɗi matattu a ƙasar Babilon, da munanan raunuka a titunanta.
5 For Israel and Judah are not forsaken By his God—by YHWH of Hosts, For their land has been full of guilt, Against the Holy One of Israel.
Gama Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila da Yahuda bai yashe su ba, ko da yake ƙasarsu cike da take da laifi a gaban Mai Tsarki na Isra’ila.
6 Flee from the midst of Babylon, And let each deliver his soul, Do not be cut off in her iniquity, For it [is] a time of vengeance for YHWH—His, He is rendering repayment to her.
“Ku gudu daga cikin Babilon! Bari kowa yă ceci ransa! Kada a hallaka saboda zunubanta. Gama lokaci ne don ramuwar Ubangiji, zai sāka mata bisa ga alhakinta.
7 Babylon [is] a golden cup in the hand of YHWH, Making all the earth drunk, Nations have drunk of her wine, Therefore nations boast themselves.
Babilon ta zama ƙoƙon zinariya a hannun Ubangiji, ta sa dukan duniya ta yi maye. Ƙasashe sun sha ruwan inabinta, saboda haka yanzu sun haukace.
8 Babylon has suddenly fallen, Indeed, she is broken, howl for her, Take balm for her pain, perhaps she may be healed.
Farat ɗaya Babilon za tă fāɗi ta farfashe. Ku yi kuka dominta! Ku samo mata magani saboda azabarta; wataƙila za a iya warkar da ita.
9 We healed Babylon, and she was not healed, Forsake her, and we go, each to his land, For her judgment has come to the heavens, And it has been lifted up to the clouds.
“‘Da mun warkar da Babilon, amma ba za tă warke ba; mu ƙyale ta kowane yă koma garinsu, gama hukuncinta ya kai sammai, ya yi tsawo kamar gizagizai.’
10 YHWH has brought forth our righteousnesses, Come, and we recount in Zion the work of our God YHWH.
“‘Ubangiji ya baratar da mu; zo mu tafi mu yi shelarsa a Sihiyona mu faɗa abin da Ubangiji Allahnmu ya yi.’
11 Cleanse the arrows, fill the shields, YHWH has stirred up the spirit of the kings of Media, For His purpose [is] against Babylon to destroy her, For it [is] the vengeance of YHWH, The vengeance of His temple.
“Ku wasa kibiyoyi, ku ɗauko garkuwoyi! Ubangiji ya zuga sarakunan Medes, domin niyyarsa ce yă hallaka Babilon. Ubangiji zai yi ramuwa, zai yi ramuwa saboda haikalinsa.
12 Lift up an ensign to the walls of Babylon, Strengthen the watch, Establish the watchers, prepare the ambush, For YHWH has both devised and done that which He spoke, Concerning the inhabitants of Babylon.
Ku tā da tuta gāba da katangan Babilon! Ku ƙara matsara, ku kafa masu tsaro, ku shirya kwanto! Ga shi, Ubangiji zai aikata abin da ya faɗa umarninsa a kan mutanen Babilon.
13 O dweller on many waters, abundant in treasures, Your end has come—the measure of your dishonest gain.
Ke da kike zama kusa da ruwaye da kike kuma wadatar dukiya, ƙarshenki ya zo, lokaci ya yi da za a kau da ke.
14 YHWH of Hosts has sworn by Himself, That, Surely I have filled you [with] men as the cankerworm, And they have cried against you—shouting.
Ubangiji Maɗaukaki ya rantse da zatinsa, ya ce Tabbatacce zan cika ka da mutane kamar fāra, za su kuwa yi sowa don nasara a kanka.
15 Making [the] earth by His power, Establishing [the] world by His wisdom, Who by His understanding stretched out the heavens,
“Ya halicci ƙasa ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa, ya kuma shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
16 At the voice He gives forth, A multitude of waters [are] in the heavens, And He causes vapors to come up from the end of the earth, He has made lightnings for rain, And He brings out wind from His treasures.
Sa’ad da ya yi tsawa ruwan da suke sammai sukan yi ruri; yakan sa gizagizai su tashi daga ƙarshen duniya. Yakan tura walƙiya tare da ruwan sama yakan kuma saki iska daga cikin taskokinsa.
17 Every man has been brutish by knowledge, Everyone has been put to shame—from refining a carved image, For his molten image [is] falsehood, And there is no breath in them.
“Kowane mutum marar azanci ne kuma ba shi da sani; kowane maƙerin zinariya yakan sha kunya daga wurin gumakansa. Siffofinsa na ƙarya ne; babu numfashi a cikinsu.
18 They [are] vanity—a work of errors, They perish in the time of their inspection.
Su marasa amfani ne, abubuwan ba’a ne kawai; sa’ad da lokacin hukuncinsu ya kai, za su hallaka.
19 The Portion of Jacob [is] not like these, For He is forming the whole, And [Israel is] the tribe of His inheritance, YHWH of Hosts [is] His Name.
Wanda yake na wajen Yaƙub ba kamar waɗannan ba ne, gama shi ne Mahalicci dukan abu, har da kabilar abin gādonsa, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
20 You [are] My shatterer—weapons of war, And I have broken in pieces nations by you, And I have destroyed kingdoms by you,
“Kai ne kulkin yaƙina, kayan yaƙina, da kai ne na ragargaza ƙasashe, da kai ne na hallaka mulkoki,
21 And I have broken in pieces horse and its rider by you, And I have broken in pieces chariot and its charioteer by you,
da kai ne na ragargaza doki da mahayi, da kai ne na ragargaza keken yaƙin da matuƙi,
22 And I have broken in pieces man and woman by you, And I have broken in pieces old and young by you, And I have broken in pieces young man and virgin by you,
da kai ne na ragargaza miji da mata, da kai ne na ragargaza tsoho da saurayi, da kai ne na ragargaza saurayi da budurwa,
23 And I have broken in pieces shepherd and his drove by you, And I have broken in pieces farmer and his team by you, And I have broken in pieces governors and prefects by you.
da kai ne na ragargaza makiyayi da garke, da kai ne na ragargaza manoma da dawakan noma, da kai ne na ragargaza masu mulki da shugabanni.
24 And I have repaid to Babylon, And to all inhabitants of Chaldea, All the evil that they have done in Zion, Before your eyes,” a declaration of YHWH.
“Zan sāka wa Babilon da dukan mazaunan Babilon a idanunku saboda dukan muguntar da suka aikata a Sihiyona,” in ji Ubangiji.
25 “Behold, I [am] against you, O destroying mountain,” A declaration of YHWH, “That is destroying all the earth, And I have stretched out My hand against you, And I have rolled you from the rocks, And given you for a burnt mountain.
“Ga shi, ina gāba da kai, ya ke dutse mai hallakarwa, wadda ta hallaka duniya duka,” in ji Ubangiji. “Zan miƙa hannuna gāba da ke, zan mirgina ƙasa daga ƙwanƙolin dutse, zan maishe ki ƙonannen dutse.
26 And they do not take out of you a stone for a corner, And a stone for foundations, For you are continuous desolations,” A declaration of YHWH.
Ba za a ɗauki dutsen yin kusurwa daga gare ki ba ko na kafa harsashen gini, gama za ki zama marar amfani har abada,” in ji Ubangiji.
27 “Lift up an ensign in the land, Blow a horn among nations, Sanctify nations against it, Summon against it the kingdoms of Ararat, Minni, and Ashkenaz, Appoint an infant head against it, Cause the horse to ascend as the rough cankerworm.
“Ku tā da tuta a ƙasa! Ku busa ƙahoni a cikin ƙasashe! Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, ku kira waɗannan mulkokin gāba da ita. Ararat, Minni, da Ashkenaz. A naɗa shugaba gāba da ita; ku shirya dawakai kamar fāra.
28 Sanctify against it the nations with the kings of Media, Its governors and all its prefects, And all the land of its dominion.
Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, sarakunan Medes, gwamnoninsu da dukan masu shugabancinsu da kowace ƙasar da take ƙarƙashin mulkinsu.
29 And the land shakes, and it is pained, For the purposes of YHWH have stood against Babylon, To make the land of Babylon a desolation without inhabitant.
Ƙasa ta girgiza tana makyarkyata saboda nufin Ubangiji na gāba da Babilon ya tabbata, nufinsa na mai da ƙasar Babilon kufai don kada kowa yă zauna a can.
30 The mighty of Babylon have ceased to fight, They have remained in strongholds, Their might has failed, they have become [as] women, They have burned her dwelling places, Her bars have been broken.
Sojojin Babilon sun daina yaƙi, suna zaune a cikin kagaransu. Ƙarfinsu ya ƙare, sun zama mata. An sa wa wuraren zamanta wuta, an karya ƙyamaren ƙofofin garinta.
31 Runner runs to meet runner, And announcer to meet announcer, To announce to the king of Babylon, For his city has been captured—at the extremity.
Maguji yana biye da maguji a guje, jakada yana biye da jakada, don su faɗa wa sarkin Babilon, cewa an ci birninsa a kowane gefe.
32 And the passages have been captured, And they have burned the reeds with fire, And the men of war have been troubled.
An ƙwace mashigai aka ƙone fadamu da wuta, sojoji kuma suka giggice.”
33 For thus said YHWH of Hosts, God of Israel: The daughter of Babylon [is] as a threshing-floor, The time of her threshing—yet a little [while], And the time of her harvest has come.
Ni Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila na ce, “’Yar Babilon kamar daɓen masussuka a lokacin da ake sussuka, ba da daɗewa ba lokacin girbe ta zai zo.”
34 Devoured us, crushed us, has Nebuchadnezzar king of Babylon, He has set us [as] an empty vessel, He has swallowed us as a dragon, He has filled his belly with my delicacies, He has driven us away.
“Nebukadnezzar sarkin Babilon ya cinye mu, ya sa muka rikice, ya maishe mu kamar tulun da babu kome a cikinsa. Ya cinye mu kamar yadda dodon ruwa yakan yi ya kuma cika cikinsa da kayan marmarinmu, sa’an nan kuma ya yi amanmu.
35 My wrong, and [that of] my flesh, [is] on Babylon—The inhabitant of Zion says; And my blood [is] on the inhabitants of Chaldea—Jerusalem says.
Bari abin da aka yi wa jikinmu yă kasance a bisa Babilon,” in ji mazaunan Sihiyona. “Bari jininmu yă kasance a kan waɗanda suke zama a Babilon,” in ji Urushalima.
36 Therefore, thus said YHWH: Behold, I am pleading your cause, And I have avenged your vengeance, And dried up her sea, and made her fountains dry.
Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “Duba, zan tsaya muku, zan ɗaukar muku fansa, zan sa tekunta kafe in kuma sa maɓulɓulanta su ƙafe.
37 And Babylon has been for heaps, A habitation of dragons, An astonishment, and a hissing, without inhabitant.
Babilon za tă zama tarin juji, wurin zaman diloli, abin ƙyama da abar ba’a, inda ba kowa.
38 They roar together as young lions, They have shaken themselves as lions’ whelps.
Mutanenta duk suna ruri kamar zakoki, suna gurnani kamar’ya’yan zaki.
39 In their heat I make their banquets, And I have caused them to drink, so that they exult, And have slept a continuous sleep, And do not awaken,” a declaration of YHWH.
Amma sa’ad da aka farkar da su, zan yi musu biki in sa su sha su bugu, domin yi sowa da dariya, sa’an nan su shiga barcin da ba za su farka ba,” in ji Ubangiji.
40 “I cause them to go down as lambs to slaughter, As rams with male goats.
“Zan sauko da su kamar tumaki zuwa mayanka, kamar raguna da bunsurai.
41 How Sheshach has been captured, Indeed, the praise of the whole earth is caught, How Babylon has been for an astonishment among nations.
“Yadda za a ci Sheshak, taƙamar duniya duka za tă daina! Babilon za tă zama abar ƙyama a cikin al’ummai!
42 The sea has come up over Babylon, She has been covered with a multitude of its billows.
Teku zai malalo a kan Babilon, raƙumansa masu hauka za su rufe ta.
43 Her cities have been for a desolation, A dry land, and a wilderness, A land—none dwell in them, Nor does a son of man pass over into them.
Garuruwanta sun zama abin kufai, za tă zama hamada inda ba ruwa, ƙasar da ba mazauna, ba kuma mutumin da zai ratsa ta cikinta.
44 And I have seen after Bel in Babylon, And I have brought forth that which he swallowed—from his mouth, And nations no longer flow to him, Also the wall of Babylon has fallen.
Zan hukunta Bel a Babilon, in sa ya yi aman abin da ya haɗiye. Ƙasashe ba za su ƙara bumbuntowa wurinsa ba. Katangan Babilon kuwa za tă rushe!
45 Go forth from her midst, O My people, And let each deliver his soul, Because of the fierceness of the anger of YHWH,
“Ku fito daga cikinta, jama’ata! Ku tsere da ranku! Ku tsere daga zafin fushin Ubangiji.
46 And lest your heart be tender, And you are afraid of the report that is heard in the land, And the report has come in [one] year, And after it [another] report in [another] year, And violence [is] in the land, ruler against ruler;
Kada zuciyarku tă yi suwu ko ku ji tsoro sa’ad da aka ji labarin a ƙasar, labari guda a wannan shekara, wani kuma a ta biye, labarin hargitsi a ƙasar mai mulki ya tasar wa mai mulki.
47 Therefore, behold, days are coming, And I have seen after the carved images of Babylon. And all its land is ashamed, And all its pierced ones fall in its midst.
Gama kwanaki tabbatacce suna zuwa, sa’ad da zan hukunta gumakan Babilon, zan kunyatar da dukan ƙasar kuma matattunta duk za su kwanta a cikinta.
48 And heavens and earth and all that [is] in them Have cried aloud against Babylon, For the spoilers come to her from the north,” A declaration of YHWH.
Sa’an nan sama da ƙasa da dukan abin da yake cikinsu, za su yi sowa ta murna a kan Babilon, gama daga arewa masu hallakarwa su auko mata,” in ji Ubangiji.
49 “As Babylon [has caused the] pierced of Israel to fall, So they of Babylon have fallen, You pierced of all the earth.
“Babilon za tă fāɗi saboda kisassun mutanen Isra’ila, kamar dai yadda kisassu dukan duniya suka fāɗi saboda Babilon.
50 You escaped of the sword, go on, do not stand, Remember YHWH from afar, And let Jerusalem come up on your heart.
Ku waɗanda kuka tsere wa takobi, ku gudu kada ku tsaya! Ku tuna da Ubangiji a ƙasa mai nesa, ku kuma yi ta tunani a kan Urushalima.”
51 We have been ashamed, for we heard reproach, Shame has covered our faces, For strangers have come in against the sanctuaries of the house of YHWH.
“Mun sha kunya saboda zargin da ake yi mana kunya ta rufe mu, domin baƙi sun shiga tsarkakan wurare na gidan Ubangiji.”
52 Therefore, behold, days are coming,” A declaration of YHWH, “And I have seen after her carved images, And the wounded groan in all her land.
“Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta gumakanta, da kuma a dukan ƙasarta waɗanda aka yi wa rauni, za su yi nishi.
53 Because Babylon goes up to the heavens, And because she fortifies the high place of her strength, Spoilers come into her from Me,” A declaration of YHWH.
Ko da Babilon za tă kai sararin sama ne, ta gina kagaranta mai ƙarfi, duk da haka zan aiki masu hallakarwa a kanta,” in ji Ubangiji.
54 “A voice of a cry [is] from Babylon, And of great destruction from the land of the Chaldean.
“Ku ji muryar kuka daga Babilon, Da hargowar babbar hallakarwa daga ƙasar Babiloniyawa!
55 For YHWH is spoiling Babylon, And has destroyed her great voice, And her billows have sounded as many waters, Their voice has given forth a noise.
Gama Ubangiji zai rushe Babilon, zai sa ta ƙame bakinta na alfarma. Sojoji za su yi ta kutsawa kamar raƙuman ruwa; suna tā da muryoyinsu.
56 For a spoiler has come in against her—against Babylon, And her mighty ones have been captured, Their bows have been broken, For the God of recompenses—YHWH—certainly repays.
Gama mai hallakarwa ya auka wa Babilon, a kama sojojinta, a kuma kakkarya bakkunansu. Gama Ubangiji shi Allah ne mai sakayya; zai yi sakayya sosai.
57 And I have caused her princes to drink, And her wise men, her governors, And her prefects, and her mighty ones, And they have slept a continuous sleep, And they do not awaken—an affirmation of the King, YHWH of Hosts [is] His Name.
Zan sa mahukuntanta da masu hikimarta, gwamnoninta, shugabanninta da sojojinta su sha su bugu; za su dinga yin barcin da ba za su farka ba,” in ji Sarkin, mai suna Ubangiji Maɗaukaki.
58 Thus said YHWH of Hosts: The wall of Babylon—The broad one—is made utterly bare, And her high gates are burned with fire, And peoples labor in vain, And nations in fire, and have been weary!”
Ni Ubangiji Maɗaukaki, na ce, “Za a baje katangan nan na Babilon mai kauri za a kuma ƙone dogayen ƙyamarenta da wuta; mutane sun wahalar da kansu a banza, al’umma sun yi wahala kawai domin wutar lalata.”
59 The word that Jeremiah the prophet has commanded Seraiah son of Neriah, son of Maaseiah, in his going with Zedekiah king of Judah to Babylon, in the fourth year of his reign—and Seraiah [is] a quiet prince;
Jawabin da annabi Irmiya ya ba Serahiya, ɗan Neriya, wato, jikan Ma’asehiya, lokacin da ya tafi tare da Zedekiya, Sarkin Yahuda, zuwa Babilon a shekara ta huɗu ta mulkinsa. Serahiya shi ne shugaba mai lura da gidajen saukar baƙi.
60 and Jeremiah writes all the calamity that comes to Babylon on one scroll—all these words that are written concerning Babylon.
Irmiya ya rubuta a littafi dukan masifun da za su auko wa Babilon, wato, dukan wannan magana da aka rubuta a kan Babilon.
61 And Jeremiah says to Seraiah, “When you enter Babylon, then you have seen, and have read all these words,
Irmiya kuwa ya ce wa Serahiya, “Lokacin da ka kai Babilon, sai ka karanta dukan maganan nan.
62 and have said: YHWH, You have spoken concerning this place, to cut it off, that there is none dwelling in it, from man even to livestock, for it is a continuous desolation.
Ka kuma ce, ‘Ya Ubangiji, kai ne ka yi magana a kan wannan wuri, cewa za ka lalatar da shi, har ba abin da zai zauna a ciki, mutum ko dabba. Wurin zai zama kufai har abada.’
63 And it has come to pass, when you finish reading this scroll, you bind a stone to it, and have cast it into the midst of the Euphrates,
Sa’ad da ka gama karanta wannan littafi, sai ka ɗaura wa littafin dutse, sa’an nan ka jefar da shi tsakiyar Kogin Yuferites.
64 and said, Thus Babylon sinks, and she does not arise, because of the calamity that I am bringing in against it, and they have been weary.” Until now [are the] words of Jeremiah.
Sa’an nan ka ce, ‘Haka Babilon za tă nutse, ba za tă ƙara tashi ba saboda masifar da zan kawo mata. Mutanenta kuwa za su fāɗi.’” Wannan shi ne ƙarshen kalmomin Irmiya.

< Jeremiah 51 >