< Jeremiah 5 >

1 “Go to and fro in streets of Jerusalem, And see now and know, And seek in her broad places, If you find a man, If there is one doing judgment, Seeking steadfastness—Then I am propitious to her.
“Ku yi ta kai da kawowa a titunan Urushalima, ku dudduba ko’ina ku kuma lura, ku bincika cikin dandalinta. Ko za ku sami mutum guda wanda yake aikata adalci wanda yake kuma son bin gaskiya, sai in gafarta wa wannan birni.
2 And if they say, YHWH lives, Surely they swear to a falsehood.”
Ko da yake suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ duk da haka suna rantsuwar ƙarya.”
3 YHWH, Your eyes, are they not on steadfastness? You have struck them, and they have not grieved, You have consumed them, They have refused to receive instruction, They made their faces harder than a rock, They have refused to turn back.
Ya Ubangiji, idanunka ba sa ganin gaskiya? Ka buge su, amma ba su ji zafi ba; ka ragargaza su, amma suka ƙi su gyara. Fuskarsu ta ƙeƙashe fiye da dutse suka ƙi su tuba.
4 And I said, “Surely these [are] poor, They have been foolish, For they have not known the way of YHWH, The judgment of their God.
Na yi tunani, “Waɗannan ne kawai matalauta; su wawaye ne, gama ba su san hanyar Ubangiji ba, ko abubuwan da Allahnsu yake bukata ba.
5 I go to the great, and I speak with them, For they have known the way of YHWH, The judgment of their God.” Surely they have broken the yoke together, They have drawn away the bands.
Saboda haka zan tafi wurin shugabanni in yi musu magana; tabbatacce sun san hanyar Ubangiji, da abubuwan da Allahnsu yake bukata.” Amma da nufi guda su ma suka karye karkiyar suka tsintsinke sarƙoƙin.
6 Therefore a lion out of the forest has struck them, A wolf of the deserts spoils them, A leopard is watching over their cities, Everyone who is going out of them is torn, For their transgressions have been many, Their backslidings have been mighty.
Saboda haka zaki daga kurmi zai fāɗa musu, kyarkeci kuma daga hamada zai cinye su, damisa za tă yi musu ƙawanya kusa da garuruwansu yă yayyage duk wanda ya kuskura ya fita, gama tawayensu da girma yake jan bayansu kuma yana da yawa.
7 “I am not propitious to you for this, Your sons have forsaken Me, And are satisfied by [those who are] not gods, I satisfy them, and they commit adultery, And at the house of a harlot They gather themselves together.
“Me zai sa in gafarta muku?’Ya’yanku sun yashe ni sun yi rantsuwa da allolin da ba alloli ba ne. Na biya musu dukan bukatunsu, duk da haka suka yi zina suka tattaru a gidajen karuwai.
8 Fed horses—they have been early risers, They each neigh to the wife of his neighbor.
An ciyar da su sosai, kamar ƙosassun ingarmu, masu jaraba, kowanne yana haniniya, yana neman matar maƙwabcinsa.
9 Do I not lay a charge for these?” A declaration of YHWH, “And on a nation such as this, Does My soul not avenge itself?
Ba zan hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’ummar nan ba?
10 Go up on her walls, and destroy, And I do not make a completion, Turn her branches aside, For they [are] not YHWH’s,
“Ku ratsa cikin gonakin inabinta ku cinye su, amma kada ku hallaka su gaba ɗaya. Ku kakkaɓe rassanta, gama waɗannan mutane ba na Ubangiji ba ne.
11 For the house of Israel has dealt treacherously against Me, And the house of Judah,” A declaration of YHWH.
Gidan Isra’ila da gidan Yahuda sun zama marasa aminci gaba ɗaya gare ni” in ji Ubangiji.
12 They have lied against YHWH, And they say, “[It is] not He, Nor does evil come in against us, Indeed, we do not see sword and famine.
Sun yi ƙarya a kan Ubangiji; sun ce, “Ba zai yi kome ba! Ba wata masifar da za tă same mu; ba za mu taɓa ganin takobi ko yunwa ba.
13 And the prophets become wind, And the word is not in them, Thus it is done to them.”
Annabawa holoƙo ne kawai maganar kuwa ba ta cikinsu; saboda haka bari abin da suke faɗi ya koma kansu.”
14 Therefore, thus said YHWH, God of Hosts: “Because of your speaking this word, Behold, I am making My words become fire in your mouth, And this people wood, And it has devoured them.
Saboda haka ga abin Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Domin mutanen sun yi waɗannan maganganu, zan mai da maganata a bakinku wuta waɗannan mutane kuwa su zama itacen da za tă ci.
15 Behold, I am bringing against you a nation from afar, O house of Israel,” A declaration of YHWH, “It [is] a strong nation, It [is] an ancient nation, A nation whose tongue you do not know, Nor understand what it speaks.
Ya gidan Isra’ila,” in ji Ubangiji, “Ina kawo al’umma daga nesa a kanku al’umma ce ta tun dā mai ƙarfin hali, mutane ne da ba ku san harshensu ba, waɗanda ba za ku fahimci abin da suke faɗa ba.
16 Its quiver [is] as an open tomb, All of them—mighty ones.
Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabari ne; dukansu jarumawa ne.
17 And it has consumed your harvest and your bread, They consume your sons, and your daughters, It consumes your flock, and your herd, It consumes your vine and your fig tree, It makes your fortified cities poor, In which you are trusting—by the sword.
Za su cinye amfanin gonakinku da abincinku, za su cinye’ya’yanku maza da mata; za su cinye garkunan tumakinku da na awakinku, za su cinye’ya’yan inabinku da na ɓaurenku. Da takobi za su hallaka biranenku masu katanga.
18 And even in those days,” A declaration of YHWH, “I do not make you a completion.
“Amma ko a cikin waɗancan kwanaki,” in ji Ubangiji, “ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba.
19 And it has come to pass, when you say, Why has our God YHWH done all these [things] to us? That you have said to them, As you have forsaken Me, And serve the gods of a foreigner in your land, So you serve strangers in a land [that is] not yours.
Sa’ad da kuma mutanen suka yi tambaya, ‘Me ya sa Ubangiji Allahnmu ya yi dukan wannan gare mu?’ Sai ka amsa musu, ‘Yadda kuka yashe ni kuka kuma bauta wa baƙin alloli a ƙasarku, haka yanzu za ku bauta wa baƙi a ƙasar da ba taku ba.’
20 Declare this in the house of Jacob, And sound it in Judah, saying,
“Ka sanar da wannan ga gidan Yaƙub ka yi shelarsa a Yahuda.
21 Now hear this, O people, foolish and without heart, They have eyes, and they do not see, They have ears, and they do not hear.
Ku ji wannan, ku wawaye marasa azanci, waɗanda suke da idanu amma ba sa gani, waɗanda suke da kunnuwa amma ba sa ji.
22 Do you not fear Me?” A declaration of YHWH; “Are you not pained from My presence? Who has made sand the border of the sea, A perpetual limit, and it does not pass over it, They shake themselves, and they are not able, Indeed, its billows have sounded, and they do not pass over.
Bai kamata ku ji tsorona ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata ku yi rawar jiki a gabana ba? Na sa yashi ya zama iyakar teku, madawwamiyar iyakar da ba zai tsallake ba. Raƙuman ruwa za su iya yin hauka, amma ba za su iya haye ta ba; za su iya yin ruri, amma ba za su iya ƙetare ta ba.
23 And this people has an apostatizing and rebelling heart, They have turned aside, and they go on.
Amma mutanen nan suna da tauraren zukata, kuma’yan tawaye ne; sun kauce suka kuma rabu da ni.
24 And they have not said in their heart, Now let us fear our God YHWH, who is giving rain, The autumn rain and the spring rain, in its season, He keeps the appointed weeks of harvest for us.
Ba sa faɗa wa kansu, ‘Bari mu ji tsoron Ubangiji Allahnmu, wanda yake ba mu ruwan sama a kan kari na kaka da na bazara, wanda kullum yake tabbatar mana da girbi.’
25 Your iniquities have turned these away, And your sins have kept the good from you.
Laifofinku sun raba ku da waɗannan abubuwa; zunubanku sun hana ku samun alheri.
26 For the wicked have been found among My people. He watches like one who sets snares, They have set up a trap—they capture men.
“A cikin mutanena an sami mugaye waɗanda suke kwanton ɓauna kamar masu sa tarko wa tsuntsaye kamar waɗanda suke kafa tarko don su kama mutane.
27 As a cage full of birds, So their houses are full of deceit, Therefore they have been great, and are rich.
Kamar keji cike da tsuntsaye, gidajensu sun cika da ruɗu; sun yi arziki suka kuma zama masu iko
28 They have been fat, they have shone, Indeed, they have surpassed the acts of the evil, They have not judged judgment, The judgment of the fatherless—and they prosper, And they have not judged the judgment of the needy.
suka kuma yi ƙiba, suka yi bul-bul. Mugayen ayyukansu ba su da iyaka; ba sa wa marayu shari’ar adalci, ba sa kāre’yancin matalauta.
29 Do I not inspect for these,” A declaration of YHWH, “On a nation such as this, Does My soul not avenge itself?
Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’umma kamar wannan ba?
30 An astonishing and horrible thing has been in the land:
“Abin banmamaki da bantsoro ya faru a ƙasar.
31 The prophets have prophesied falsely, And the priests bear rule by their means, And My people have loved [it] so, And what do they do at its latter end?”
Annabawa suna annabcin ƙarya, firistoci suna mulki da ikon kansu, mutanena kuma suna son haka. Amma me za ku yi a ƙarshe?

< Jeremiah 5 >