< Jeremiah 41 >

1 And it comes to pass, in the seventh month, Ishmael son of Nethaniah, son of Elishama, of the royal seed, and of the chiefs of the king, and ten men with him, have come to Gedaliah son of Ahikam, to Mizpah, and there they eat bread together in Mizpah.
A wata na goma sha bakwai sai Ishmayel ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake mai jinin sarauta yake kuma ɗaya daga cikin hafsoshin sarki, ya zo tare da mutum goma wurin Gedaliya ɗan Ahikam a Mizfa. Yayinda suke ci tare a can,
2 And Ishmael son of Nethaniah rises, and the ten men who have been with him, and they strike Gedaliah son of Ahikam, son of Shaphan, with the sword, and he puts him to death whom the king of Babylon has appointed over the land.
sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutum goma waɗanda suke tare da shi suka kashe Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da takobi, suka kashe wannan da sarkin Babilon ya naɗa a matsayin gwamna a kan ƙasar.
3 And all the Jews who have been with him, with Gedaliah, in Mizpah, and the Chaldeans who have been found there—the men of war—Ishmael has struck.
Ishmayel ya kuma kashe dukan Yahudawan da suke tare da Gedaliya a Mizfa, haka ma ya yi da sojojin Babiloniyawan da suke can.
4 And it comes to pass, on the second day of the putting of Gedaliah to death (and no one has known),
Kashegari bayan an kashe Gedaliya, kafin wani ya san abin da ya faru,
5 that men come in from Shechem, from Shiloh, and from Samaria—eighty men—with shaven beards, and torn garments, and cutting themselves, and [with] an offering and frankincense in their hand, to bring [them] to the house of YHWH.
sai ga mutane tamanin daga Shekem, Shilo da Samariya suka zo da gemunsu a aske, da tufafinsu a kece, da jikunansu a tsage, suka kawo hadayun gari da turare tare da su a gidan Ubangiji.
6 And Ishmael son of Nethaniah goes forth to meet them, from Mizpah, going on and weeping, and it comes to pass, at meeting them, that he says to them, “Come to Gedaliah son of Ahikam.”
Ishmayel ɗan Netaniya ya fito daga Mizfa don yă sadu da su. Sa’ad da ya sadu da su, sai ya ce, “Ku zo wurin Gedaliya ɗan Ahikam.”
7 And it comes to pass, at their coming into the midst of the city, that Ishmael son of Nethaniah slaughters them, at the midst of the pit, he and the men who [are] with him.
Da suka shiga cikin birni, sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutanen da suke tare da shi suka karkashe su suka zubar a rijiya.
8 And ten men have been found among them, and they say to Ishmael, “Do not put us to death, for we have things hidden in the field—wheat, and barley, and oil, and honey.” And he refrains, and has not put them to death in the midst of their brothers.
Amma goma daga cikinsu suka ce wa Ishmayel, “Kada ka kashe mu, muna da alkama da sha’ir, mai da kuma zuma, a ɓoye a gona.” Saboda haka ka bar mu kada ka kashe mu tare da sauran.
9 And the pit to where Ishmael has cast all the carcasses of the men whom he has struck along with Gedaliah, is that which King Asa made because of Baasha king of Israel—Ishmael son of Nethaniah has filled it with the pierced.
To, rijiyar da ya zubar da gawawwakin mutanen da ya kashe tare da ta Gedaliya ita ce wadda Sarki Asa ya haƙa a matsayin kāriya saboda Ba’asha sarkin Isra’ila. Ishmayel ɗan Netaniya ya cika ta da gawawwaki.
10 And Ishmael takes captive all the remnant of the people who [are] in Mizpah, the daughters of the king, and all the people who are left in Mizpah, whom Nebuzar-Adan, chief of the executioners, has committed [to] Gedaliah son of Ahikam, and Ishmael son of Nethaniah takes them captive, and goes to pass over to the sons of Ammon.
Ishmayel ya mai da dukan sauran mutanen da suke Mizfa bayi’ya’yan sarki mata tare da dukan sauran da aka bari a can, waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari a hannun Gedaliya ɗan Ahikam. Ishmayel ɗan Netaniya ya kwashe su ganima, ya tashi don yă haye zuwa wurin Ammonawa.
11 And Johanan son of Kareah, and all the heads of the forces that [are] with him, hear of all the evil that Ishmael son of Nethaniah has done,
Sa’ad da Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka ji dukan laifofin da Ishmayel ɗan Netaniya ya aikata,
12 and they take all the men, and go to fight with Ishmael son of Nethaniah, and they find him at the great waters that [are] in Gibeon.
sai suka kwashe dukan mutanensu suka tafi don su yaƙi Ishmayel ɗan Netaniya. Suka iske shi kusa da babban tafki a Gibeyon.
13 And it comes to pass, when all the people who [are] with Ishmael see Johanan son of Kareah, and all the heads of the forces who [are] with him, that they rejoice.
Sa’ad da dukan mutanen da suke tare da Ishmayel suka ga Yohanan ɗan Kareya da shugabannin sojojin da suke tare da shi, sai suka yi farin ciki.
14 And all the people whom Ishmael has taken captive from Mizpah turn around, indeed, they turn back, and go to Johanan son of Kareah.
Dukan mutanen da Ishmayel ya kame a Mizfa suka juya, suka tafi wurin Yohanan ɗan Kareya.
15 And Ishmael son of Nethaniah has escaped, with eight men, from the presence of Johanan, and he goes to the sons of Ammon.
Amma Ishmayel ɗan Netaniya da mutanensa takwas suka tsere daga Yohanan suka gudu zuwa wurin Ammonawa.
16 And Johanan son of Kareah, and all the heads of the forces who [are] with him, take all the remnant of the people whom he has brought back from Ishmael son of Nethaniah, from Mizpah—after he had struck Gedaliah son of Ahikam—mighty ones, men of war, and women, and infants, and eunuchs, whom he had brought back from Gibeon,
Sai Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka bi da dukan waɗanda suka tsira daga Mizfa waɗanda ya karɓe daga Ishmayel ɗan Netaniya bayan ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wato, sojoji, mata, yara da fadawan da ya kawo daga Gibeyon
17 and they go and abide in the habitations of Chimham, that [are] near Beth-Lehem, to go to enter Egypt,
Sai suka ci gaba, suka dakata a Gerut Kimham kusa da Betlehem a kan hanyarsu zuwa Masar
18 from the presence of the Chaldeans, for they have been afraid of them, for Ishmael son of Nethaniah had struck Gedaliah son of Ahikam, whom the king of Babylon had appointed over the land.
don su kuɓuce wa Babiloniyawa. Sun ji tsoronsu domin Ishmayel ɗan Netaniya ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wanda sarkin Babilon ya naɗa gwamna a kan ƙasar.

< Jeremiah 41 >