< Jeremiah 38 >

1 And Shephatiah son of Mattan, and Gedaliah son of Pashhur, and Jucal son of Shelemiah, and Pashhur son of Malchiah, hear the words that Jeremiah is speaking to all the people, saying,
Shefatiya ɗan Mattan, Gedaliya ɗan Fashhur, Yukal ɗan Shelemiya da Fashhur ɗan Malkiya ya ji abin da Irmiya yana faɗa wa dukan mutane sa’ad da ya ce,
2 “Thus said YHWH: He who is remaining in this city dies, by sword, by famine, and by pestilence, and he who is going forth to the Chaldeans lives, and his soul has been to him for a prey, and he lives.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba, amma duk wanda ya je wurin Babiloniyawa zai rayu. Zai tsira da ransa, ya rayu.’
3 Thus said YHWH: This city is certainly given into the hand of the force of the king of Babylon, and he has captured it.”
Kuma ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Tabbatacce za a ba da wannan birni ga sojojin sarkin Babilon, wanda zai ci shi.’”
4 And the heads say to the king, “Now let this man be put to death, because that he is making feeble the hands of the men of war who are left in this city, and the hands of all the people, by speaking to them according to these words, for this man is not seeking for the peace of this people, but for its calamity.”
Sai fadawa suka ce wa sarki, “Ya kamata a kashe wannan mutum. Yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran mutane, ta wurin abubuwan da yake faɗa musu. Wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan sai dai wahala.”
5 And King Zedekiah says, “Behold, he [is] in your hand: for the king is not able [to do] anything against you.”
“Yana a hannuwanku” Sarki Zedekiya ya amsa. “Sarki ba zai iya yin kome ya hana ku ba.”
6 And they take Jeremiah, and cast him into the pit of Malchiah son of the king, that [is] in the court of the prison, and they send Jeremiah down with cords; and there is no water in the pit, but mire, and Jeremiah sinks in the mire.
Saboda haka suka kama Irmiya suka sa a rijiyar da ba ruwa a ciki ta Malkiya, ɗan sarki, wadda take a sansanin matsara. Suka saukar da Irmiya cikin rijiyar da ba ruwa da igiya; babu ruwa a cikinta, sai laka, Irmiya ya nutse cikin laka.
7 And Ebed-Melech the Cushite, a eunuch who [is] in the king’s house, hears that they have put Jeremiah into the pit; and the king is sitting at the Gate of Benjamin,
Amma Ebed-Melek mutumin Kush, wani hafsa a fada, ya ji cewa sun sa Irmiya a rijiyar da ba ruwa. Yayinda sarki yana zama a Ƙofar Benyamin,
8 and Ebed-Melech goes forth from the king’s house, and speaks to the king, saying,
Ebed-Melek ya fita daga fadar ya ce masa,
9 “My lord, O king, these men have done evil [in] all that they have done to Jeremiah the prophet, whom they have cast into the pit, and he dies in his place because of the famine, for there is no more bread in the city.”
“Ranka yă daɗe sarki, waɗannan mutane sun yi mugun abu a duk abin da suka yi wa Irmiya annabi. Sun jefa shi cikin rijiyar da ba ruwa, inda zai mutu da yunwa gama ba sauran wani burodi a birnin.”
10 And the king commands Ebed-Melech the Cushite, saying, “Take with you thirty men from here, and you have brought up Jeremiah the prophet from the pit, before he dies.”
Sai sarki ya umarce Ebed-Melek mutumin Kush, “Ka ɗauko mutane talatin daga nan ku fid da Irmiya annabi daga rijiyar kafin ya mutu.”
11 And Ebed-Melech takes the men with him, and enters the house of the king, to the place of the treasury, and takes there worn-out shreds of cloth, and worn-out rags, and sends them by cords into the pit to Jeremiah.
Saboda haka Ebed-Melek ya ɗauki mutane tare da shi suka shiga ɗaki a ƙarƙashin baitulmali a cikin fada. Ya ɗauko waɗansu tsofaffin tsummoki da tsofaffi riguna daga can ya kuma zurara su da igiya wa Irmiya a cikin rijiyar.
12 And Ebed-Melech the Cushite says to Jeremiah, “Now put the worn-out pieces of cloth and rags under your arms, at the place of the cords,” and Jeremiah does so,
Ebed-Melek mutumin Kush ya ce wa Irmiya, “Ka sa waɗannan tsummoki da tsofaffin rigunan a hammatarka, ya zarga igiya.” Irmiya ya yi haka,
13 and they draw Jeremiah out with cords, and bring him up out of the pit, and Jeremiah dwells in the court of the prison.
suka kuma ja shi sama da igiya suka fid da shi daga rijiyar. Irmiya kuwa ya zauna a sansanin matsara.
14 And King Zedekiah sends, and takes Jeremiah the prophet to him, to the third entrance that [is] in the house of YHWH, and the king says to Jeremiah, “I am asking you something, do not hide anything from me.”
Sai Sarki Zedekiya ya aika a kawo Irmiya annabi, ya sa aka kawo shi a ƙofa ta uku ta haikalin Ubangiji. Sai sarki ya ce wa Irmiya, “Zan tambaye ka wani abu, kada ka ɓoye mini wani abu.”
15 And Jeremiah says to Zedekiah, “When I declare [it] to you, do you not surely put me to death? And when I counsel you, you do not listen to me.”
Irmiya ya ce wa Zedekiya, “In na ba ka amsa, ba za ka kashe ni ba? Ko da na ba ka shawara, ba za ka saurare ni ba.”
16 And King Zedekiah swears to Jeremiah in secret, saying, “YHWH lives, He who made this soul for us, I do not put you to death, nor give you into the hand of these men who are seeking your soul.”
Amma Sarki Zedekiya ya yi wannan rantsuwa a kaɗaice ga Irmiya cewa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya ba mu numfashi, ba zan kashe ka ko in ba da kai ga waɗanda suke neman ranka ba.”
17 And Jeremiah says to Zedekiah, “Thus said YHWH, God of Hosts, God of Israel: If you certainly go forth to the heads of the king of Babylon, then your soul has lived, and this city is not burned with fire, indeed, you have lived, you and your house.
Sa’an nan Irmiya ya ce wa Zedekiya, “Ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon, za a bar ka da rai ba za a kuma ƙone wannan birni ba; da kai da iyalinka za ku rayu.
18 And if you do not go forth to the heads of the king of Babylon, then this city has been given into the hand of the Chaldeans, and they have burned it with fire, and you do not escape from their hand.”
Amma in ba ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon ba, za a ba da wannan birni ga Babiloniyawa za su kuma cinna mata wuta; kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba.’”
19 And King Zedekiah says to Jeremiah, “I am fearing the Jews who have fallen to the Chaldeans, lest they give me into their hand, and they have insulted me.”
Sarki Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Ina jin tsoron Yahudawan da suka tafi wurin Babiloniyawa, gama Babiloniyawa mai yiwuwa su ba da ni gare su su kuma wulaƙanta ni.”
20 And Jeremiah says, “They do not give you up; please listen to the voice of YHWH, to that which I am speaking to you, and it is well for you, and your soul lives.
Irmiya ya ce, “Ba za su ba da kai ba, ka yi biyayya ga Ubangiji ta wurin yin abin da na faɗa maka. Ta haka zai zama maka da amfani, za ka kuwa rayu.
21 And if you are refusing to go forth, this [is] the thing that YHWH has shown me:
Amma in ka ƙi miƙa wuya, ga abin da Ubangiji ya bayyana mini.
22 That, behold, all the women who have been left in the house of the king of Judah are brought forth to the heads of the king of Babylon, and behold, they are saying: Persuaded you, and prevailed against you, Have your allies, Your feet have sunk into mire, They have been turned backward.
Za a fitar da dukan matan da suka ragu a fadan sarkin Yahuda wa hafsoshin sarkin Babilon. Waɗannan mata za su ce maka, “‘Sun ruɗe ka suka kuma rinjaye ka, waɗannan abokanka. Ƙafafunka sun nutse a cikin laka; abokanka sun yashe ka.’
23 And all your wives and your sons are brought forth to the Chaldeans, and you do not escape from their hand, for you are caught by the hand of the king of Babylon, and this city is burned with fire.”
“Za a kawo dukan matanka da’ya’yanka wa Babiloniyawa. Kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba amma za su sa sarkin Babilon zai kama ka; za a kuma ƙone wannan birni.”
24 And Zedekiah says to Jeremiah, “Let no man know of these words, and you do not die;
Sai Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Kada ka bar wani ya san wannan zance, in ba haka ba za ka mutu.
25 and when the heads hear that I have spoken with you, and they have come to you, and have said to you, Now declare to us what you spoke to the king, do not hide [it] from us, and we do not put you to death, and what the king spoke to you,
In fadawa suka ji cewa na yi magana da kai, suka kuma zo wurinka suka ce, ‘Faɗa mana abin da ka faɗa wa sarki da kuma abin da sarki ya faɗa maka; kada ka ɓoye mana, in ba haka za mu kashe ka,’
26 then you have said to them, I am causing my supplication to fall before the king, not to cause me to return to the house of Jonathan, to die there.”
sai ka ce musu cewa, ‘Na roƙi sarki kada yă mai da ni gidan Yonatan in mutu a can.’”
27 And all the heads come to Jeremiah, and ask him, and he declares to them according to all these words that the king commanded, and they keep silent from him, for the matter was not heard;
Dukan fadawa kuwa suka zo wurin Irmiya suka tambaye shi, ya kuma faɗa musu dukan abin da sarki ya umarce shi ya faɗa. Saboda haka ba su ƙara ce masa kome ba, gama ba wanda ya ji zance da suka yi da sarki.
28 and Jeremiah dwells in the court of the prison until the day that Jerusalem has been captured, and he was [there] when Jerusalem was captured.
Irmiya kuwa ya zauna a sansanin masu gadi har ranar da aka ci Urushalima da yaƙi. Ga yadda aka ci Urushalima,

< Jeremiah 38 >