< Jeremiah 30 >
1 The word that has been to Jeremiah from YHWH, saying,
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
2 “Thus spoke YHWH, God of Israel, saying, Write for yourself all the words that I have spoken to you on a scroll.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ka rubuta a cikin littafi dukan maganganun da na yi maka.
3 For behold, days are coming—a declaration of YHWH—and I have turned back [to] the captivity of My people Israel and Judah, said YHWH, and I have caused them to return to the land that I gave to their fathers, and they possess it.”
Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan komo da mutanena Isra’ila da Yahuda daga bauta in kuma maido da su ga ƙasar da na ba wa kakanninsu mallaka,’ in ji Ubangiji.”
4 And these [are] the words that YHWH has spoken concerning Israel and concerning Judah:
Ga kalmomin Ubangiji da ya yi game da Isra’ila da Yahuda,
5 Surely thus said YHWH: “We have heard a voice of trembling, Fear—and there is no peace.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ana jin kukan tsoro, razana, ba salama ba.
6 Now ask and see, is a male bringing forth? Why have I seen every man [With] his hands on his loins, as a travailing woman, And all faces have been turned to paleness?
Ku tambaya ku ji. Namiji zai iya haifi’ya’ya? To, me ya sa kuke ganin kowane mai ƙarfi da hannuwansa a kwankwaso kamar mace mai naƙuda, kowace fuska ta koma fari?
7 Woe! For that day [is] great, without any like it, Indeed, it [is] the time of Jacob’s tribulation, Yet he is saved out of it.
Kaito, gama wannan rana za tă zama mai girma! Babu kamar ta. Zai zama lokacin wahala wa Yaƙub, amma za a cece shi daga cikinta.
8 And it has come to pass in that day, A declaration of YHWH of Hosts, I break his yoke from off your neck, And I draw away your bands, And strangers lay no more service on him.
“‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan karya karkiya daga wuyansu zan kuma cire musu kangi; baƙi ba za su ƙara bautar da su ba.
9 And they have served their God YHWH, And David their king whom I raise up to them.
A maimakon haka, za su bauta wa Ubangiji Allahnsu Dawuda sarkinsu kuwa, wanda na tayar musu.
10 And you, do not be afraid, My servant Jacob, A declaration of YHWH, Nor be frightened, O Israel, For behold, I am saving you from afar, And your seed from the land of their captivity, And Jacob has turned back and rested, And is quiet, and there is none troubling.
“‘Saboda haka kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila,’ in ji Ubangiji. ‘Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nesa, zuriyarka daga ƙasar zaman bautansu. Yaƙub zai sami salama da zaman lafiya, kuma ba wanda zai sa ya ji tsoro.
11 For I [am] with you,” A declaration of YHWH, “To save you, For I make an end of all the nations To where I have scattered you, Only, I do not make an end of you, And I have disciplined you in judgment, And do not entirely acquit you.”
Ina tare da kai zan kuma cece ka,’ in ji Ubangiji. ‘Ko da yake na hallakar da dukan al’umma gaba ɗaya a inda na warwatsa ku, ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba. Zan hore ku amma da adalci kaɗai; ba zan ƙyale ku ku tafi gaba ɗaya ba hukunci ba.’
12 For thus said YHWH: “Your breach is incurable, your stroke grievous,
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Mikinku marar warkewa ne, raunin da kuka ji ya sha ƙarfin warkarwa.
13 There is none judging your cause to bind up, There are no healing medicines for you.
Babu wanda zai yi roƙo saboda damuwarku, ba magani domin mikinku babu warkarwa dominku.
14 All loving you have forgotten you, They do not seek you, For I struck you with the stroke of an enemy, The discipline of a fierce one, Because of the abundance of your iniquity, your sins have been mighty!
Dukan abokanku sun manta da ku; ba su ƙara kulawa da ku. Na buge ku kamar yadda abokin gāba zai yi na kuma hukunta ku yadda mai mugunta zai yi, domin laifinku da girma yake zunubanku kuma da yawa suke.
15 Why do you cry concerning your breach? Your pain [is] incurable, Because of the abundance of your iniquity, Your sins have been mighty! I have done these to you.
Me ya sa kuke kuka a kan mikinku, wahalarku da ba ta da magani? Domin laifinku da girma yake da kuma zunubanku masu yawa na yi muku waɗannan abubuwa.
16 Therefore all consuming you are consumed, And all your adversaries—all of them—Go into captivity, And your spoilers have been for a spoil, And I give up all your plunderers to plunder.
“‘Amma duk wanda ya cinye ku za a cinye shi; dukan abokan gābanku za su tafi zaman bauta. Waɗanda suka washe ku su ma za a washe su; dukan waɗanda suka mai da ku ganima su ma zan mai da su ganima.
17 For I increase health to you, And I heal you from your strokes,” A declaration of YHWH, “For they have called you an outcast, [saying], It [is] Zion, There is none seeking for her.”
Amma zan mayar muku da lafiya in kuma warkar da mikinku,’ in ji Ubangiji, ‘domin ana ce da ku yasassu, Sihiyona wadda ba wanda ya kula da ita.’
18 Thus said YHWH: “Behold, I turn back [to] the captivity of the tents of Jacob, And I pity his dwelling places, And the city has been built on its heap, And the palace remains according to its ordinance.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Zan mayar da wadatar tentin Yaƙub in kuma ji tausayin wuraren zamansa; za a sāke gina birnin a kufansa, fadar kuwa za tă tsaya a wurin da ya dace da ita.
19 And thanksgiving has gone forth from them, And the voice of playful ones, And I have multiplied them and they are not few, And made them honorable, and they are not small.
Daga gare su waƙoƙi za su fito na godiya da kuma sowa ta farin ciki. Zan riɓaɓɓanya su, ba za su kuwa ragu ba; zan kawo musu ɗaukaka, ba kuwa za a ƙasƙanta su ba.
20 And his sons have been as before, And his congregation is established before Me, And I have seen after all his oppressors.
’Ya’yansu za su kasance kamar a kwanakin dā jama’arsu kuma za su kahu a gabana; zan hukunta duk wanda ya zalunce su.
21 And his majestic one has been of himself, And his ruler goes forth from his midst, And I have caused him to draw near, And he has drawn near to Me, For who [is] he who has pledged his heart To draw near to Me?” A declaration of YHWH.
Shugabansu zai zama ɗaya daga cikinsu; mai mulkinsu zai taso daga cikinsu. Zan kawo shi kusa zai kuma zo kusa da ni, gama wane ne zai miƙa kansa don yă yi kusa da ni?’ In ji Ubangiji.
22 “And you have been to Me for a people, And I am to you for God.”
‘Saboda haka za ku zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnku.’”
23 Behold, a whirlwind of YHWH—Fury has gone forth—a cutting whirlwind, It stays on the head of the wicked.
Ga shi, hadarin Ubangiji zai fasu cikin hasala, iskar guguwa mai hurawa a kan kawunan mugaye.
24 The fierceness of the anger of YHWH Does not turn back until He has done [it], Indeed, until His establishing the purposes of His heart. In the latter end of the days you consider it!
Fushi mai zafi na Ubangiji ba zai kawu ba sai ya cika manufofin zuciyarsa gaba ɗaya. A kwanaki masu zuwa za ku gane wannan.