< Jeremiah 10 >

1 Hear the word, O house of Israel, That YHWH has spoken for you.
Ku ji abin da Ubangiji yana ce muku, ya gidan Isra’ila.
2 Thus said YHWH: “Do not accustom yourselves to the way of the nations, And do not be frightened by the signs of the heavens, For the nations are frightened by them.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ku koyi hanyoyin al’ummai ko ku razana game da alamun sararin sama, ko da yake al’ummai sun razana saboda su.
3 For the statutes of the peoples are vanity, For one has cut a tree from a forest, Work of the hands of a craftsman, with an axe,
Gama al’adun mutane banza ne; sukan yanke itace daga kurmi, sai mai sassaƙa yă sassaƙa shi da gizago.
4 They beautify it with silver and with gold, They fix it with nails and with hammers, And it does not stumble.
Sukan yi masa ado da azurfa da kuma zinariya; sukan ɗauki guduma su kafa shi da ƙusoshi, don kada yă fāɗi.
5 They [are] stiff as a palm, and they do not speak, They are surely carried, for they do not step, Do not be afraid of them, for they do no evil, Indeed, to do good is also not in them.”
Kamar dodon gona cikin gonar kabewa, haka gumakansu ba sa iya magana; dole a yi ta ɗaukansu domin ba za su iya tafiya ba. Kada ku ji tsoronsu; ba za su iya yi wa wani lahani ba ba sa iya yin wani abin kirki.”
6 Because there is none like You, O YHWH, You [are] great, and Your Name [is] great in might.
Babu wani kamar ka, ya Ubangiji; kai mai girma ne, kuma sunanka yana da girma da kuma iko.
7 Who does not fear You, King of the nations? For it is befitting to You, For among all the wise of the nations, And in all their kingdom, there is none like You.
Wane ne ba zai girmama ka ba, Ya Sarkin al’ummai? Tsoronka wajibi ne. A cikin dukan masu hikima na al’ummai kuma cikin dukan mulkokinsu, babu kamar ka.
8 And as one they are brutish and foolish, An instruction of vanities [is] the tree itself.
Dukansu marasa azanci ne wawaye; gumakan itacen banza ne suke koya musu.
9 Spread-out silver is brought from Tarshish, And gold from Uphaz, Work of an artisan, and of the hands of a refiner, Their clothing [is] blue and purple, Work of the skillful—all of them.
An kawo ƙeraren azurfa daga Tarshish zinariya kuma daga Ufaz. Abin da gwani da maƙerin zinariya suka yi sa’an nan aka yi masa ado da mulufi da shunayya dukan aikin gwanaye.
10 And YHWH [is] a God of truth, He [is] a living God, and a perpetual King, The earth shakes from His wrath, And nations do not endure His indignation.
Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya; shi ne Allah mai rai, madawwamin sarki. Sa’ad da ya yi fushi, ƙasa takan girgiza; al’ummai ba sa iya jure da hasalarsa.
11 Thus you say to them, “The gods who have not made the heavens and earth, They perish from the earth, And from under these heavens.”
“Ka faɗa musu wannan, ‘Waɗannan alloli, waɗanda ba su yi sammai da ƙasa ba, za su hallaka daga duniya da kuma daga ƙarƙashin sammai.’”
12 The Maker of the earth by His power, The Establisher of the world by His wisdom, Who, by His understanding, stretched forth the heavens—
Amma Allah ya yi duniya ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa ya shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
13 When He gives forth His voice, A multitude of waters [is] in the heavens, And He causes vapors to come up from the end of the earth, He has made lightnings for rain, And brings out wind from His treasures.
Sa’ad da ya yi tsawa, ruwaye a cikin sammai sukan yi ƙugi; yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya. Yakan aiki walƙiya da ruwan sama ya fitar da iska daga gidajen ajiyarsa.
14 Every man is brutish by knowledge, Every refiner is put to shame by a carved image, For his molten image [is] false. And there is no breath in them.
Kowa marar azanci ne, marar ilimi; kowane maƙerin zinariya zai sha kunya saboda gumakansa. Siffofinsa ƙarya ne; ba su da numfashi a cikinsu.
15 They [are] vanity, work of erring ones, They perish in the time of their inspection.
Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne; Sa’ad da hukuncinsu ya yi za su lalace.
16 The Portion of Jacob [is] not like these, For He [is] the Framer of all things, And Israel [is] the rod of His inheritance, YHWH of Hosts [is] His Name.
Shi da yake Rabon Yaƙub ba kamar waɗannan yake ba, gama shi ne Mahaliccin abubuwa duka, har da Isra’ila, kabilar gādonsa Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
17 Gather your merchandise from the land, O dweller in the bulwark,
Ku tattara kayayyakinku don ku bar ƙasar, ku da kuke zaune a wurin da aka kewaye da yaƙi.
18 For thus said YHWH: “Behold, I am slinging out the inhabitants of the land at this time, And have been an adversary to them, So that they are found out.”
Gama haka Ubangiji ya faɗa, “A wannan lokaci zan jefar da waɗanda suke zaune a ƙasar; zan kawo damuwa a kansu domin a kama su.”
19 Woe to me for my breaking, My striking has been grievous, And I said, “Surely this [is] my sickness, and I bear it.”
Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini! Raunina ba mai warkewa ba ne! Duk da haka na ce wa kaina, “Wannan ciwona ne, dole kuma in jure da shi.”
20 My tent has been spoiled, And all my cords have been broken, My sons have gone out from me, and they are not, There is none stretching out my tent anymore, And raising up my curtains.
An lalatar da tentina; dukan igiyoyinsa sun tsintsinke.’Ya’yana maza sun bar ni ba sa nan; ba wanda aka bari da zai kafa tentina ko ya kafa mini mafaka.
21 For the shepherds have become brutish, And they have not sought YHWH, Therefore they have not acted wisely, And all their flock is scattered.
Makiyaya marasa azanci ne kuma ba sa neman nufin Ubangiji; saboda haka ba sa nasara dukan garkensu kuwa ya watse.
22 A voice of a report, behold, it has come, Even a great shaking from the north country, To make the cities of Judah a desolation, A habitation of dragons.
Ku saurara! Rahoto yana zuwa babban hargitsi daga ƙasar arewa! Zai mai da garuruwan Yahuda kufai, mazaunin diloli.
23 I have known, O YHWH, that not of man [is] his way, Not of man [is] the going and establishing of his step.
Na sani, ya Ubangiji, cewa ran mutum ba nasa ba ne; ba mutum ne yake kiyaye takawarsa ba.
24 Discipline me, O YHWH, only in judgment, Not in Your anger, lest You make me small.
Ka yi mini gyara, Ubangiji, amma fa da adalci kaɗai ba cikin fushinka ba, don kada ka wofinta ni.
25 Pour out Your fury on the nations that have not known You, And on the families that have not called on Your Name, For they have eaten up Jacob, Indeed, they have eaten him up, indeed, they consume him, And they have made his habitation desolate!
Ka zuba hasalarka a kan al’umman da ba su san ka ba, a kan mutanen da ba sa kira bisa sunanka. Gama sun cinye Yaƙub; sun cinye shi gaba ɗaya suka kuma lalace wurin zamansa.

< Jeremiah 10 >