< Isaiah 59 >

1 Behold, the hand of YHWH Has not been shortened from saving, Nor His ear heavy from hearing.
Tabbatacce hannun Ubangiji bai kāsa yin ceto ba, kunnensa kuma bai kurmance da zai kāsa ji ba.
2 But your iniquities have been separating Between you and your God, And your sins have hidden The Presence from you—from hearing.
Amma laifofinku sun raba ku da Allahnku; zunubanku sun ɓoye fuskarsa daga gare ku, saboda kada yă ji.
3 For your hands have been defiled with blood, And your fingers with iniquity, Your lips have spoken falsehood, Your tongue mutters perverseness.
Gama hannuwanku sun ƙazantu da jini, yatsotsinku kuma da alhaki. Leɓunanku suna faɗin ƙarairayi, harshenku kuma yana raɗar mugayen abubuwa.
4 There is none calling in righteousness, And there is none pleading in faithfulness, Trusting on emptiness, and speaking falsehood, Conceiving perverseness, and bearing iniquity.
Babu wani mai ce a yi adalci; babu wani mai nema a dubi al’amarinsa da mutunci. Sun dogara a gardandamin banza suna ƙarairayi; suna ɗaukar cikin ɓarna, su haifi mugunta.
5 They have hatched eggs of a viper, And weave webs of a spider, Whoever is eating their eggs dies, and the crushed hatches a viper.
Suna ƙyanƙyashe ƙwan kāsā su kuma saƙa yanar gizo-gizo. Duk wanda ya ci ƙwansu zai mutu, kuma sa’ad da ƙwan ya fashe, zai ƙyanƙyashe kububuwa.
6 Their webs do not become a garment, Nor do they cover themselves with their works, Their works [are] works of iniquity, And a deed of violence [is] in their hands.
Yanar gizo-gizonsu ba amfani don tufa; ba za su iya rufuwa da abin da suka yi ba. Ayyukansu mugaye ne, ayyukan tā da hargitsi kuma suna a hannuwansu.
7 Their feet run to evil, And they hurry to shed innocent blood, Their thoughts [are] thoughts of iniquity, Spoiling and destruction [are] in their highways.
Ƙafafunsu sukan gaggauta zuwa aikata zunubi; suna da saurin zub da jini. Tunaninsu mugaye ne; lalaci da hallaka sun shata hanyoyinsu.
8 They have not known a way of peace, And there is no judgment in their paths, They have made their paths perverse for themselves, None treading in it has known peace.
Ba su san hanyar salama ba; babu adalci a hanyoyinsu. Sun mai da su karkatattun hanyoyi; babu wanda zai yi tafiya a kansu ya sami salama.
9 Therefore judgment has been far from us, And righteousness does not reach us, We wait for light, and behold, darkness, For brightness—in thick darkness we go,
Saboda haka gaskiya ta yi nisa da mu, adalci kuma ba ya kaiwa gare mu. Muna neman haske, sai ga duhu; muna neman haske, sai muka yi ta tafiya cikin baƙin inuwa.
10 We feel [for] the wall like the blind, Indeed, we feel as without eyes, We have stumbled at noon as at twilight, In desolate places as the dead.
Kamar makafi, sai lallubar bango muke yi, muna lallubawar hanyarmu kamar marasa idanu. Da tsakar rana muna tuntuɓe sai ka ce wuri ya fara duhu; cikin ƙarfafa, mun zama kamar matattu.
11 We make a noise as bears—all of us, And we coo severely as doves; We wait for judgment, and there is none, For salvation—it has been far from us.
Muna gurnani kamar beyar; muna ta ƙugi kamar kurciyoyi. Muna ta neman adalci amma ina; mun nemi fansa, amma yana can da nisa.
12 For our transgressions have been multiplied before You, And our sins have testified against us, For our transgressions [are] with us, And our iniquities—we have known them.
Gama laifofinmu suna da yawa a gabanka, zunubanmu kuma suna ba da shaida gāba da mu. Laifofinmu kullum suna a gabanmu, muna kuma sane da laifofinmu,
13 Transgressing, and lying against YHWH, And removing from after our God, Speaking oppression and apostasy, Conceiving and uttering from the heart Words of falsehood.
tawaye da mūsun Ubangiji, mun juye bayanmu ga Allahnmu, zugawa a yi zalunci da tayarwa, faɗin ƙarairayi da zukatanmu suka shirya.
14 And judgment is removed backward, And righteousness stands far off, For truth has been feeble in the street, And straightforwardness is not able to enter,
Saboda haka aka kau da yin gaskiya adalci kuma ya tsaya can da nesa; gaskiya ta yi tuntuɓe a tituna, sahihanci ba zai shiga ba.
15 And the truth is lacking, And whoever is turning aside from evil, Is making himself a spoil. And YHWH sees, and it is evil in His eyes, That there is no judgment.
Gaskiya ta ɓace gaba ɗaya, kuma duk wanda ya guji mugunta zai zama ganima. Ubangiji ya duba bai kuwa ji daɗi cewa babu adalci ba.
16 And He sees that there is no man, And is astonished that there is no intercessor, And His own arm gives salvation to Him, And His righteousness—it sustained Him.
Ya ga cewa babu wani, ya yi mamaki cewa babu wanda zai shiga tsakani; saboda haka hannunsa ya aikata masa ceto, adalcinsa kuma ya raya shi.
17 And He puts on righteousness as a breastplate, And a helmet of salvation on His head, And He puts on garments of vengeance [for] clothing, And is covered, as [with] an upper-robe, [with] zeal.
Ya yafa sulke a matsayin rigar ƙirji, da hulan kwanon ceto a kansa; ya sa rigunan ɗaukar fansa ya kuma nannaɗe kansa da kishi kamar a cikin alkyabba.
18 According to deeds—so He repays. Fury to His adversaries, [their] deed to His enemies, To the islands He repays [their] deed.
Bisa ga abin da suka yi, haka za a sāka fushi a kan abokan gābansa ramuwa kuma a kan maƙiyansa; zai sāka wa tsibirai abin da ya dace da su.
19 And from the west they fear the Name of YHWH, And from the rising of the sun—His glory, When an adversary comes in as a flood, The Spirit of YHWH has raised an ensign against him.
Daga yamma, mutane za su ji tsoron Ubangiji, daga mafitar rana kuma, za su girmama ɗaukakarsa. Gama zai zo kamar rigyawa mai tsananin gudu cewa numfashin Ubangiji zai tafi tare da shi.
20 “And the Redeemer has come to Zion, Even to captives of transgression in Jacob,” A declaration of YHWH.
“Mai fansa zai zo Sihiyona, zuwa waɗanda suke cikin Yaƙub da suka tuba daga zunubansu,” in ji Ubangiji.
21 “And I—this [is] My covenant with them,” said YHWH, “My Spirit that [is] on you, And My words that I have put in your mouth, Do not depart from your mouth, And from the mouth of your seed, And from the mouth of your seed’s seed,” said YHWH, “From now on, even for all time!”
“Game da ni dai, ga alkawarina da su,” in ji Ubangiji. “Ruhuna, wanda yake a kanka, da kuma maganata da na sa a bakinka ba za tă rabu da bakinka ba, ko daga bakunan’ya’yanka ba, ko kuwa daga bakunan zuriyarsu ba daga wannan lokaci zuwa gaba da kuma har abada,” in ji Ubangiji.

< Isaiah 59 >