< Isaiah 43 >
1 And now, thus said YHWH, Your Creator, O Jacob, and your Fashioner, O Israel: Do not be afraid, for I have redeemed you, I have called on your name—you [are] Mine.
To, fa, ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicce ka, ya Yaƙub, shi da ya siffanta ka, ya Isra’ila, “Kada ka ji tsoro, gama na fanshe ka; na kira ka da suna; kai nawa ne.
2 When you pass into waters, I [am] with you, And into floods, they do not overflow you, When you go into fire, you are not burned, And a flame does not burn against you.
Sa’ad da kuka bi ta ruwaye, zan kasance tare da ku; sa’ad da kuka bi ta koguna, ba za su kwashe ku ba. Sa’ad da kuke tafiyata cikin wuta, ba za tă ƙone ku ba; harsunan wutar ba za su ƙone ku ba.
3 For I—your God YHWH, The Holy One of Israel, your Savior, I have appointed Egypt your atonement, Cush and Seba in your stead.
Gama ni ne Ubangiji, Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, Mai Cetonku; na bayar da Masar don fansa, Kush da Seba a maimakonku.
4 Since you were precious in My eyes, You were honored, and I have loved you, And I appoint men in your stead, And peoples instead of your life.
Da yake ku masu daraja da kuma girma ne a idona, saboda kuma ina ƙaunarku, zan ba da mutane a maimakonku, al’umma kuma domin ranku.
5 Do not be afraid, for I [am] with you, I bring in your seed from the east, And I gather you from the west.
Kada ku ji tsoro, gama ina tare da ku; zan kawo yaranku daga gabas in kuma tattara ku daga yamma.
6 I am saying to the north, “Give up,” And to the south, “Do not restrain.” Bring in My sons from afar, And My daughters from the end of the earth.
Zan ce wa arewa, ‘Ku miƙa su!’ Ga kudu kuma, ‘Kada ku riƙe su.’ Kawo’ya’yana maza daga nesa’ya’yana mata kuma daga iyakar duniya,
7 Everyone who is called by My Name, Even for My glory I have created him, I have formed him, indeed, I have made him.
kowa da ake kira da sunana, wanda aka halitta saboda ɗaukakata, wanda na siffanta na kuma yi.”
8 He brought out a blind people who have eyes, And deaf ones who have ears.
Jagoranci waɗanda suke da idanu amma suke makafi, waɗanda suke da kunnuwa amma suke kurame.
9 All the nations have been gathered together, And the peoples are assembled, Who among them declares this, And causes us to hear former things? They give their witnesses, And they are declared righteous, And they hear and say, “Truth.”
Dukan al’ummai su taru mutane kuma su tattaru. Wane ne a cikinsu ya yi faɗar wannan ya kuma yi mana shelar abubuwan da suka riga suka faru? Bari su kawo shaidunsu don su tabbatar cewa sun yi daidai, don waɗansu su ji su kuma ce, “Gaskiya ne.”
10 You [are] My witnesses, a declaration of YHWH, And My servant whom I have chosen, So that you know and give credence to Me, And understand that I [am] He, Before Me there was no God formed, And after Me there is none.
“Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “bawana kuma wanda na zaɓa, saboda ka sani ka kuma gaskata ni ka kuma fahimci cewa ni ne shi. Kafin ni babu allahn da aka siffanta, ba kuwa za a yi wani a bayana ba.
11 I [am] YHWH, And besides Me there is no savior.
Ni kaɗai, ni ne Ubangiji, kuma in ban da ni babu wani mai ceto.
12 I declared, and saved, and proclaimed, And there is no stranger with you, And you [are] My witnesses, a declaration of YHWH, And I [am] God.
Na bayyana na ceci na kuma furta, Ni ne, ba wani baƙon allah a cikinku. Ku ne shaiduna,” in ji Ubangiji, “cewa ni ne Allah.
13 Even from the day I [am] He, And there is no deliverer from My hand, I work, and who turns it back?
I, kuma tun fil azal ni ne shi. Babu wani da zai amshi daga hannuna. Sa’ad da na aikata, wa zai iya sauyawa?”
14 Thus said YHWH, your Redeemer, The Holy One of Israel: “I have sent to Babylon for your sake, And caused bars to descend—all of them, And the Chaldeans, whose song [is] in the ships.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, “Saboda ku zan aika Babilon in kawo dukan Babiloniyawa kamar masu gudun hijira, a cikin jiragen ruwa waɗanda suke taƙama da su.
15 I [am] YHWH, your Holy One, Creator of Israel, your King.”
Ni ne Ubangiji, Mai Tsarkin nan, Mahaliccin Isra’ila, Sarkinku.”
16 Thus said YHWH, Who is giving a way in the sea, And a path in the strong waters.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya yi hanya ta cikin teku, hanya ta cikin manyan ruwaye,
17 Who is bringing forth chariot and horse, A force, even a strong one: “They lie down together—they do not rise, They have been extinguished, They have been quenched as flax.”
wanda ya ja kekunan yaƙi da dawakai, mayaƙa da kuma ƙarin mayaƙa tare ya kwantar da su a can, ba kuwa za su ƙara tashi ba, ya kashe hayaƙi daga lagwani,
18 Do not remember former things, And do not consider ancient things.
“Ku manta da abubuwan da suka riga suka faru; kada ku yi tunanin abin da ya riga ya wuce.
19 Behold, I am doing a new thing, now it springs up, Do you not know it? Indeed, I put a way in a wilderness, In a desolate place—floods.
Duba, ina yi abu sabo! Yanzu yana faruwa; ba ku gan shi ba? Ina yin hanya a cikin hamada rafuffuka kuma a cikin ƙeƙasasshiyar ƙasa.
20 The beast of the field honors Me, Dragons and daughters of an ostrich, For I have given waters in a wilderness, Floods in a desolate place, To give drink to My people—My chosen.
Namun jeji suna girmama ni, diloli da mujiyoyi ma haka, domin na tanada musu ruwa a hamada da rafuffuka a ƙeƙasasshiyar ƙasa, don a ba da abin sha ga mutanena, zaɓaɓɓuna,
21 I have formed this people for Myself, They recount My praise.
mutanen da na yi saboda kaina don su furta yabona.
22 And you have not called Me, O Jacob, For you have been wearied of Me, O Israel,
“Duk da haka ba ku kira bisa sunana ba, ya Yaƙub, ba ku gajiyar da kanku saboda ni ba, ya Isra’ila.
23 You have not brought to Me, The lamb of your burnt-offerings, And [with] your sacrifices you have not honored Me, I have not caused you to serve with a present, Nor wearied you with frankincense.
Ba ku kawo mini tumaki don hadaya ta ƙonewa ba, balle ku girmama ni da hadayunku. Ban nawaita muku da hadaya ta gari ba balle in gajiyar da ku da bukatar turare.
24 You have not bought Me sweet cane with money, And have not filled Me [with] the fat of your sacrifices, Only—you have caused Me to serve with your sins, You have wearied Me with your iniquities.
Ba ku saya wani turaren kalamus domina ba ko ku gamshe ni da kitsen hadayunku. Amma kun nawaita ni da zunubanku kuka kuma gajiyar da ni da laifofinku.
25 I [am] He who is blotting out Your transgressions for My own sake, And I do not remember your sins.
“Ni kaɗai ne na shafe laifofinku, saboda sunana, ban kuma ƙara tunawa da zunubanku ba.
26 Cause Me to remember—we are judged together, Declare that you may be justified.
Ku tunashe ni abin da ya riga ya wuce, bari mu yi muhawwara wannan batu tare; ku kawo hujjarku na nuna rashin laifinku.
27 Your first father sinned, And your interpreters transgressed against Me,
Mahaifinku na farko ya yi zunubi; masu magana a madadinku suka yi mini tayarwa.
28 And I defile princes of the sanctuary, And I give Jacob to destruction, and Israel to revilings!
Saboda haka zan kunyata manyan baƙi na haikalinku, zan tura Yaƙub ga hallaka Isra’ila kuwa yă zama abin dariya.