< Isaiah 38 >
1 In those days has Hezekiah been sick to death, and Isaiah son of Amoz, the prophet, comes to him and says to him, “Thus said YHWH: Give a charge to your house, for you [are] dying, and do not live.”
A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”
2 And Hezekiah turns around his face to the wall, and prays to YHWH,
Hezekiya ya juye fuskarsa wajen bango ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
3 and says, “Ah, now, O YHWH, please remember how I have habitually walked before You in truth, and with a perfect heart, and I have done that which [is] good in your eyes”; and Hezekiah weeps [with] a great weeping.
“Ka tuna, ya Ubangiji, yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukan zuciya na kuma yi abin da yake nagari a idanunka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
4 And a word of YHWH is to Isaiah, saying,
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Ishaya cewa,
5 “Go, and you have said to Hezekiah, Thus said YHWH, God of your father David: I have heard your prayer, I have seen your tear, behold, I am adding fifteen years to your days,
“Ka tafi ka faɗa wa Hezekiya, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda, ya ce na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan ƙara maka shekaru goma sha biyar ga rayuwarka.
6 and out of the hand of the king of Asshur I deliver you and this city, and have covered over this city.
Zan kuwa cece ka da wannan birni daga hannun sarkin Assuriya. Zan kiyaye wannan birni.
7 And this [is] to you the sign from YHWH, that YHWH does this thing that He has spoken.
“‘Ga alamar Ubangiji gare ka cewa Ubangiji zai aikata kamar yadda ya yi alkawari.
8 Behold, I am bringing back the shadow of the degrees that it has gone down on the degrees of Ahaz, by the sun, backward ten degrees”; and the sun turns back ten degrees in the degrees that it had gone down.
Zan sa inuwar da rana ta yi a kan matakalar Ahaz ta koma baya da taki goma.’” Saboda haka inuwar ta koma da baya daga fuskar rana har taki goma.
9 A writing of Hezekiah king of Judah concerning his being sick when he revives from his sickness:
Rubutun Hezekiya sarkin Yahuda bayan ciwonsa da kuma warkarwarsa.
10 “I said in the cutting off of my days, I go to the gates of Sheol, I have numbered the remnant of my years. (Sheol )
Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata dole in bi ta ƙofofin mutuwa a kuma raba ni da sauran shekaruna?” (Sheol )
11 I said, I do not see YAH—YAH! In the land of the living, I do not behold man anymore, With the inhabitants of the world.
Na ce, “Ba zan ƙara ganin Ubangiji ba, Ubangiji a ƙasa ta masu rai; ba zan ƙara ga wani mutum, ko in kasance tare da waɗanda suke zama a wannan duniya ba.
12 My sojourning has departed, And been removed from me as a shepherd’s tent, I have drawn together, as a weaver, my life, By weakness it cuts me off, From day to night You end me.
Kamar tentin makiyayi an rushe gidana aka kuma ƙwace ta daga gare ni. Kamar mai saƙa, na nannaɗe rayuwata, ya kuma yanke ni daga sandar saƙa; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
13 I have set [Him] as a lion until morning, So He breaks all my bones, From day to night You end me.
Na yi jira da haƙuri har safiya, amma kamar zaki ya kakkarya ƙasusuwana duka; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
14 As a crane—a swallow—so I chatter, I mourn as a dove, My eyes have been drawn up on high, O YHWH, oppression [is] on me, be my guarantor.
Na yi kuka kamar mashirare ko zalɓe, na yi kuka kamar kurciya mai makoki. Idanuna suka rasa ƙarfi yayinda na duba sammai. Na damu; Ya Ubangiji, ka taimake ni!”
15 What do I say? Seeing He spoke to me, And He Himself has worked, I go softly all my years for the bitterness of my soul.
Amma me zan ce? Ya riga ya yi mini magana, shi kansa ne kuma ya aikata. Zan yi tafiya da tawali’u dukan kwanakina saboda wahalar raina.
16 Lord, [men] live by these, And by all in them [is] the life of my spirit, And You save me, make me to also live,
Ubangiji, ta waɗannan abubuwa ne mutane suke rayuwa; ruhuna kuma yana samun rai a cikinsu shi ma. Ka maido mini da lafiya ka kuma sa na rayu.
17 Behold, He changed bitterness to peace for me, And You have delighted in my soul without corruption, For You have cast all my sins behind Your back.
Tabbatacce wannan kuwa saboda ribata ne cewa in sha irin wahalan nan. Cikin ƙaunarka ka kiyaye ni daga ramin hallaka; ka sa dukan zunubaina a bayanka.
18 For Sheol does not confess You, Death does not praise You, Those going down to the pit do not hope for Your truth. (Sheol )
Gama kabari ba zai yabe ka ba, matattu ba za su rera yabonka ba; waɗanda suka gangara zuwa rami ba za su sa zuciya ga amincinka ba. (Sheol )
19 The living, the living, he confesses You,
Masu rai, masu rai, su suke yabonka, kamar yadda nake yi a yau; iyaye za su faɗa wa’ya’yansu game da amincinka.
20 Like myself today; A father makes known to [his] sons of Your faithfulness, O YHWH—to save me: And we sing my songs all [the] days of our lives In the house of YHWH.”
Ubangiji zai cece ni, za mu kuma rera da kayan kiɗi masu tsirkiya dukan kwanakinmu a cikin haikalin Ubangiji.
21 And Isaiah says, “Let them take a bunch of figs, and plaster over the ulcer, and he lives.”
Ishaya ya riga ya ce, “Ku shirya curin da aka yi da’ya’yan ɓaure ku kuma shafa a marurun, zai kuwa warke.”
22 And Hezekiah says, “What [is] the sign that I go up to the house of YHWH?”
Hezekiya ya riga ya yi tambaya ya ce, “Me zai zama alama ta cewa zan haura zuwa haikalin Ubangiji?”