< Hosea 9 >

1 “Do not rejoice, O Israel, do not be joyful like the peoples, For you have gone whoring from your God, You have loved a wage near all floors of grain.
Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
2 Floor and winepress do not feed them, And new wine fails in her,
Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
3 They do not abide in the land of YHWH, And Ephraim has turned back [to] Egypt, And they eat an unclean thing in Asshur.
Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
4 They do not pour out wine to YHWH, Nor are they sweet to Him, Their sacrifices [are] as bread of mourners to them, All eating it are unclean: For their bread [is] for themselves, It does not come into the house of YHWH.
Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
5 What do you do at the day appointed? And at the day of YHWH’s festival?
Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
6 For behold, they have gone because of destruction, Egypt gathers them, Moph buries them, The desirable things of their silver, Nettles possess them—a thorn [is] in their tents.
Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
7 The days of inspection have come in, The days of repayment have come in, Israel knows! The prophet [is] a fool, Mad [is] the man of the spirit, Because of the abundance of your iniquity, And great [is] the hatred.
Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
8 Ephraim is looking [away] from My God, The prophet! A snare of a fowler [is] over all his ways, Hatred [is] in the house of his God.
Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
9 They have gone deep—have done corruptly, As [in] the days of Gibeah, He remembers their iniquity, He inspects their sins.
Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
10 As grapes in a wilderness I found Israel, As the first-fruit in a fig tree, at its beginning, I have seen your fathers, They have gone in [to] Ba‘al-Peor, And are separated to a shameful thing, And have become abominable like their love.
“Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
11 Ephraim [is] as a bird, their glory flies away, without birth, and without womb, and without conception.
Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
12 For though they nourish their sons, I have made them childless—without man, Surely also, woe to them when I turn aside from them.
Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
13 Ephraim! When I have looked to the rock, Is planted in comeliness, And Ephraim [is] to bring out his sons to a slayer.
Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
14 Give to them, YHWH—what do You give? Give to them miscarrying womb, and dry breasts.
Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
15 All their evil [is] in Gilgal, Surely there I have hated them, Because of the evil of their doings, Out of My house I drive them, I no longer love them, All their heads [are] apostates.
“Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
16 Ephraim has been struck, Their root has dried up, they do not yield fruit, Indeed, though they bring forth, I have put to death the desired of their womb.
An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
17 My God rejects them, Because they have not listened to Him, And they are wanderers among nations!”
Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.

< Hosea 9 >