< Hebrews 12 >
1 Therefore, we also having so great a cloud of witnesses set around us, having put off every weight, and the closely besetting sin, may we run the contest that is set before us through endurance,
Saboda haka, da yake muna kewaye da irin wannan taron shaidu mai girma, sai mu yar da duk abin da yake hana mu da kuma zunubin da yake saurin daure mu, mu kuma yi tseren da aka sa a gabanmu da nacewa.
2 looking to the Author and Perfecter of the faith—Jesus, who, for the joy set before Him, endured a cross, having despised shame, and sat down at the right hand of the throne of God;
Bari mu kafa idanunmu a kan Yesu, tushe da kuma kammalar bangaskiyarmu, wanda ya jure kunyar gicciye da aka yi masa, domin ya san cewa daga baya zai yi farin ciki ya yi haka. Yanzu kuma yana zaune a hannun dama na kursiyin Allah.
3 for again consider Him who endured such contradiction from the sinners to Himself, that you may not be wearied in your souls—being faint.
Ku lura da wannan wanda ya jure da irin hamayyan nan daga masu zunubi, don kada ku gaji, har ku fid da zuciya.
4 You did not yet resist to blood—striving with sin;
Cikin famanku da zunubi, ba ku yi tsayayya har ga zub da jininku ba tukuna.
5 and you have forgotten the exhortation that speaks fully to you as to sons, “My son, do not despise [the] discipline of [the] LORD, nor be faint, being reproved by Him,
Kun kuma manta da kalmar ƙarfafawan nan da tana ce da ku’ya’ya, “Ɗana kada ka rena horon Ubangiji, kada kuma ka fid da zuciya sa’ad da ya kwaɓe ka,
6 for whom the LORD loves He disciplines, and He scourges every son whom He receives”;
domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, yakan kuma hori duk wanda yakan karɓa a matsayin ɗa.”
7 if you endure discipline, God bears Himself to you as to sons, for who is a son whom a father does not discipline?
Ku jimre shan wahala a matsayin horo; Allah yana yi da ku kamar’ya’ya. Gama wane ɗa ne mahaifinsa ba ya horonsa?
8 And if you are apart from discipline, of which all have become partakers, then you are bastards, and not sons.
In ba a hore ku ba (kowa kuwa yakan sami horo), to, ku shegu ne ba’ya’yan gida ba.
9 Then, indeed, we have had fathers of our flesh, correctors, and we respected [them]; will we not much rather be subject to the Father of the spirits, and live?
Ban da haka ma, dukanmu mun kasance da ubannin jiki waɗanda suka hore mu muka kuma yi musu ladabi. Ashe, bai kamata mu yi wa Uban ruhohinmu biyayya mu kuwa rayu ba!
10 For they, indeed, for a few days, according to what seemed good to them, were disciplining, but He for profit, to be partakers of His separation;
Ubanninmu sun hore mu na ɗan lokaci yadda suka ga ya fi kyau; amma Allah yakan hore mu don amfaninmu, domin mu sami rabo cikin tsarkinsa.
11 and all discipline for the present, indeed, does not seem to be of joy, but of sorrow, yet afterward it yields the peaceable fruit of righteousness to those exercised through it.
Babu horon da yake da daɗi a lokacin da ake yinsa, sai dai zafi. Amma daga baya waɗanda suka horu ta haka sukan sami kwanciyar rai wadda aikin adalci yake bayarwa.
12 For this reason, lift up the hanging-down hands and the loosened knees;
Saboda haka, sai ku ƙarfafa raunanan hannuwanku da gwiwoyinku marasa ƙarfi!
13 and make straight paths for your feet, so that which is lame may not be turned aside, but rather be healed;
“Ku shirya hanyoyi marasa gargaɗa saboda ƙafafunku,” don kada guragu su daɗa gurguntawa, sai dai su warke.
14 pursue peace with all, and the separation, apart from which no one will see the LORD,
Ku yi iyakacin ƙoƙari ku yi zaman lafiya da kowa, ku kuma zama masu tsarki; gama in ban da tsarki ba babu wanda zai ga Ubangiji.
15 observing lest anyone be failing of the grace of God, lest any root of bitterness springing up may give trouble, and through this many may be defiled;
Ku lura fa kada wani yă kāsa samun alherin Allah, kada kuma wani tushen ɗacin rai yă tsira har yă kawo rikici, yă kuma ƙazantar da mutane da yawa.
16 lest anyone be a fornicator, or a profane person, as Esau, who in exchange for one morsel of food sold his birthright,
Ku lura kada wani yă zama mai fasikanci, ko marar tsoron Allah kamar Isuwa, wanda saboda ƙwaryar abinci ɗaya tak ya sayar da gādonsa na ɗan fari.
17 for you know that also afterward, wishing to inherit the blessing, he was disapproved of, for he did not find a place of conversion, though having sought it with tears.
Daga baya, kamar yadda kuka sani, sa’ad da ya nemi yă gāji wannan albarka, aka ƙi shi. Bai sami zarafin tuba ba, ko da yake ya nemi albarkan nan da hawaye.
18 For you did not come near to the mountain touched and scorched with fire, and to blackness, and darkness, and storm,
Ba ku zo ga Dutsen Sinai wanda ana iya taɓawa ba, ko ga wuta mai ci sosai, ko ga duhu baƙi ƙirin, ko
19 and a sound of a trumpet, and a voice of sayings, which those having heard begged that a word might not be added to them,
ko busar ƙaho, ko ga irin wata murya mai magana da kalmomin da masu jinta suka yi roƙo kada su ƙara ji,
20 for they were not bearing that which is commanded, “And if a beast may touch the mountain, it will be stoned, or shot through with an arrow,”
domin ba su iya jimrewa da abin da aka umarta cewa, “Ko da ma dabba ce ta taɓa dutsen, dole a jajjefe ta da duwatsu.”
21 and (so terrible was the sight), Moses said, “I am exceedingly fearful, and trembling.”
Ganin wannan abu da matuƙar bantsoro yake, har Musa ya ce, “Ina rawar jiki don tsoro.”
22 But you came to Mount Zion, and to [the] city of the living God, to the heavenly Jerusalem, and to myriads of messengers,
Sai dai kun zo ne ga Dutsen Sihiyona, ga Urushalima ta sama, birnin Allah mai rai. Kun zo ga dubu dubban mala’ikun da suke cikin taron farin ciki,
23 to the assembly-place and Assembly of the Firstborn registered in Heaven, and to God the judge of all, and to spirits of righteous men made perfect,
kun zo ga ikkilisiyar ɗan fari, waɗanda sunayensu suna a rubuce a sama. Kun zo ga Allah, alƙalin dukan mutane, kun kuma zo ga ruhohin mutane masu adalci da aka mai da su cikakku.
24 and to a mediator of a new covenant—Jesus, and to blood of sprinkling, speaking better things than that of Abel!
Kun zo ga Yesu, mai yin sulhu na sabon alkawari, da kuma ga jinin da aka yayyafa wanda yake magana mafi kyau fiye da jinin Habila.
25 Watch out lest you refuse Him who is speaking, for if those did not escape who refused him who was divinely speaking on earth—much less we who turn away from Him who [speaks] from Heaven,
Ku lura fa kada ku ƙi wanda yake magana. Gama in su ba su tsira sa’ad da suka ƙi wanda ya gargaɗe su a wannan duniya ba, to, ƙaƙa mu za mu tsira, in mun ƙi jin wannan da yake yi mana gargaɗi daga Sama?
26 whose voice shook the earth then, and now He has promised, saying, “Yet once [more]—I shake not only the earth, but also Heaven”;
A lokacin nan muryarsa ta jijjiga duniya, amma yanzu ya yi alkawari cewa, “Har wa yau sau ɗaya tak zan ƙara jijjiga ba duniya kaɗai ba, amma har ma da sammai.”
27 and this, “Yet once [more],” makes evident the removal of the things shaken, as of things having been made, that the things not shaken may remain;
Wannan magana “sau ɗayan nan” sun nuna, kawar da abin da za a iya jijjigawa, wato, ƙirƙiro abubuwa, saboda abubuwan da ba a iya jijjigawa, su kasance.
28 for this reason, receiving a kingdom that cannot be shaken, may we have grace, through which we may serve God well-pleasingly, with reverence and fear,
Saboda haka, da yake muna karɓar mulkin da ba ya jijjiguwa, sai mu yi godiya, ta haka kuwa mu yi wa Allah sujada yadda ya kamata, tare da bangirma da kuma tsoro,
29 for our God [is] also a consuming fire.
gama “Allahnmu wuta ne mai cinyewa.”