< Habakkuk 3 >

1 A prayer of Habakkuk the prophet, [set] on shigionoth:
Addu’ar annabi Habakkuk. A kan shigiyont.
2 O YHWH, I heard your report, I have been afraid, O YHWH, Your work! In midst of years revive it, In the midst of years You make known, In anger You remember mercy.
Ya Ubangiji, na ji irin shaharar da ka yi; na yi al’ajabi game da ayyukanka, ya Ubangiji. Ka maimaita su a kwanakinmu, ka sanar da su a lokacinmu; ka yi jinƙai ko a lokacin da kake fushi.
3 God comes from Teman, The Holy One from Mount Paran. (Pause) His splendor has covered the heavens, And His praise has filled the earth.
Allah ya zo daga Teman, Mai Tsarkin nan daga Dutsen Faran. (Sela) Ɗaukakarsa ta rufe sammai yabonsa kuma ya cika duniya.
4 And the brightness is as the light, He has rays out of His hand, And there—the hiding of His strength.
Darajarsa ta yi kamar fitowar rana; ƙyalƙyali ya wulga daga hannunsa, inda ikonsa yake a ɓoye.
5 Before Him goes pestilence, And a burning flame goes forth at His feet.
Annoba ta sha gabansa; cuta kuma tana bin bayansa.
6 He has stood, and He measures earth, He has seen, and He shakes off nations, And mountains of antiquity scatter themselves, The hills of old have bowed, The ways of old [are] His.
Ya tsaya, ya kuwa girgiza duniya; ya duba, sai ya sa al’ummai suka yi rawan jiki. Tsofaffin duwatsu sun wargaje daɗaɗɗun tuddai kuma suka rurrushe. Hanyoyinsa dawwammamu ne.
7 Under sorrow I have seen tents of Cushan, Curtains of the land of Midian tremble.
Na ga tentin Kushan cikin azaba; wuraren zaman Midiyan cikin damuwa.
8 Has YHWH been angry against rivers? Against rivers [is] Your anger? [Is] Your wrath against the sea? For You ride on Your horses—Your chariots of salvation.
Ka ji haushin koguna ne, ya Ubangiji? Ko kuwa ka hasala da rafuffuka ne? Ko ka yi fushi da teku ne sa’ad da ka hau dawakanka da kuma kekunan yaƙinka masu nasara?
9 You make Your bow utterly naked, The tribes have sworn, saying, (Pause) You cleave the earth [with] rivers.
Ka ja bakanka, ka nemi a ba ka kibiyoyi masu yawa. (Sela) Ka raba duniya da koguna;
10 Seen You—pained are mountains, An inundation of waters has passed over, The deep has given forth its voice, It has lifted up its hands high.
duwatsu sun gan ka sai suka ƙame. Ruwaye masu hauka sun yi ta fantsamawa; zurfafa suka yi ruri suka tā da raƙuman ruwansu sama.
11 Sun—moon—has stood—a habitation, Your arrows go on at the light, At the brightness, the glittering of Your spear.
Rana da wata suka tsaya cik a sammai da ganin kibiyoyinka masu wucewa fyu, da ganin hasken māshinka mai walƙiya.
12 In indignation You tread earth, In anger You thresh nations.
Cikin hasala ka ratsa duniya cikin fushi kuma ka tattake ƙasashe.
13 You have gone forth for the salvation of Your people, For salvation with Your Anointed, You have struck the head of the house of the wicked, Laying bare the foundation to the neck. (Pause)
Ka fito don ka fanshi mutanenka, don ceci shafaffenka. Ka ragargaza shugaban ƙasar mugaye, ka tuɓe shi daga kai har ƙafa. (Sela)
14 You have pierced the head of his leaders with his own rods, They are tempestuous to scatter me, Their exultation [is] as to consume the poor in secret.
Da māshinsa ka soki kansa sa’ad da jarumawansa suka fito don su tarwatse mu, suna farin ciki sai ka ce masu shirin cinye matalautan da suke a ɓoye.
15 You have proceeded through the sea with Your horses—the clay of many waters.
Ka tattake teku da dawakanka, kana kaɗa manyan ruwaye.
16 I have heard, and my belly trembles, At the noise have my lips quivered, Rottenness comes into my bones, And in my place I tremble, That I rest for a day of distress, At the coming up of the people, he overcomes it.
Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
17 Though the fig tree does not flourish, And there is no produce among vines, The work of the olive has failed, And fields have not yielded food, The flock has been cut off from the fold, And there is no herd in the stalls,
Ko da yake itace ɓaure bai tohu ba, ba kuma’ya’ya a kuringar inabi, ko da yake zaitun bai ba da amfani ba, gonaki kuma ba su ba da abinci ba, ko da yake babu tumaki a garke, ba kuma shanu a turaku,
18 Yet I, in YHWH I exult, I am joyful in the God of my salvation.
duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, zan yi murna da Allah Mai Cetona.
19 YHWH the Lord [is] my strength, And He makes my feet like does, And causes me to tread on my high-places. To the overseer with my stringed instruments!
Ubangiji Mai Iko Duka shi ne ƙarfina; yakan mai da ƙafafuna kamar na barewa, yakan sa in yi tafiya a wurare masu tsayi. Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata.

< Habakkuk 3 >