< Genesis 9 >
1 And God blesses Noah and his sons, and says to them, “Be fruitful, and multiply, and fill the earth;
Sa’an nan Allah ya sa wa Nuhu da’ya’yansa maza albarka, yana ce musu, “Ku haifi’ya’ya, ku ƙaru, ku kuma cika duniya.
2 and your fear and your dread is on every beast of the earth, and on every bird of the heavens, on all that creeps on the ground, and on all fishes of the sea—into your hand they have been given.
Dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa, da dukan kifayen teku, za su riƙa jin tsoronku, suna fargaba. An sa su a cikin hannuwanku.
3 Every creeping thing that is alive, to you it is for food; as the green herb I have given to you the whole;
Kome da yake da rai wanda yake tafiya, zai zama abincinku. Kamar yadda na ba ku kowane irin ganye, haka na ba ku kome da kome.
4 only flesh in its life—its blood—you do not eat.
“Akwai abu ɗaya da ba za ku ci ba, wato, nama wanda jininsa yake cikinsa tukuna.
5 And only your blood for your lives do I require; from the hand of every living thing I require it, and from the hand of man, from the hand of every man’s brother I require the life of man;
Game da jinin ranka kuwa lalle zan bukaci lissafi. Zan bukaci lissafi daga kowane dabba. kuma daga kowane mutum, shi ma zan bukaci lissafi game da ran ɗan’uwansa.
6 whoever sheds man’s blood, by man is his blood shed: for in the image of God has He made man.
“Duk wanda ya zub da jinin mutum, ta hannun mutum za a zub da jininsa; gama a cikin siffar Allah ne, Allah ya yi mutum.
7 And you, be fruitful and multiply, teem in the earth, and multiply in it.”
Amma ku, ku yi ta haihuwa, ku ƙaru; ku yaɗu a duniya, ku yi yawa a bisanta.”
8 And God speaks to Noah, and to his sons with him, saying,
Sai Allah ya ce wa Nuhu da’ya’yansa,
9 “And I, behold, I am establishing My covenant with you, and with your seed after you,
“Yanzu na kafa alkawarina da ku da zuriyarku a bayanku,
10 and with every living creature which [is] with you, among bird, among livestock, and among every beast of the earth with you, from all who are going out of the Ark—to every beast of the earth.
da kowace halitta mai rai wadda ta kasance tare da kai; wato, tsuntsaye da dabbobin gida da kuma dukan namun jeji, duk dai iyakar abin da ya fita daga jirgin; wato, kowane mai rai na duniya.
11 And I have established My covenant with you, and all flesh is not cut off anymore by waters of a flood, and there is not a flood to destroy the earth anymore.”
Na kafa alkawarina da ku, ba za a ƙara hallaka dukan rayuka da ambaliyar ruwa ba; ba za a ƙara yin ambaliya don a hallaka duniya ba.”
12 And God says, “This is a token of the covenant which I am giving between Me and you, and every living creature that [is] with you, to continuous generations;
Allah ya kuma ce, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na yi tsakanina da ku, da kowace halitta tare da ku; alkawari na dukan zamanai masu zuwa.
13 My bow I have given in the cloud, and it has been for a token of a covenant between Me and the earth;
Na sa bakan gizona cikin gizagizai, shi ne kuwa zai zama alamar alkawari tsakanina da duniya.
14 and it has come to pass (in My sending a cloud over the earth) that the bow has been seen in the cloud,
Duk sa’ad da na kawo gizagizai a bisa duniya, bakan gizo kuma ya bayyana a ciki gizagizan,
15 and I have remembered My covenant which is between Me and you, and every living creature among all flesh, and the waters no longer become a flood to destroy all flesh;
zan tuna da alkawari tsakanina da ku da kuma dukan halittu masu rai na kowane iri. Ruwa ba zai sāke yin ambaliyar da za tă hallaka dukan masu rai ba.
16 and the bow has been in the cloud, and I have seen it—to remember the perpetual covenant between God and every living creature among all flesh which [is] on the earth.”
Duk sa’ad da bakan gizo ya bayyana cikin gizagizan, zan gan shi in kuma tuna da madawwamin alkawari tsakanin Allah da dukan halittu masu rai, na kowane iri a duniya.”
17 And God says to Noah, “This [is] a token of the covenant which I have established between Me and all flesh that [is] on the earth.”
Saboda haka Allah ya ce wa Nuhu, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na kafa tsakanina da dukan masu rai a duniya.”
18 And the sons of Noah who are going out of the Ark are Shem, and Ham, and Japheth; and Ham is father of Canaan.
’Ya’yan Nuhu maza, waɗanda suka fito daga cikin jirgi, su ne, Shem, Ham da Yafet. (Ham shi ne mahaifin Kan’ana.)
19 These three [are] sons of Noah, and from these has all the earth been overspread.
Waɗannan su ne’ya’yan Nuhu maza uku, daga gare su ne kuma duniya za tă cika da mutane.
20 And Noah remains a man of the ground, and plants a vineyard,
Nuhu, mutumin ƙasa, shi ne farko da ya fara yin gonar inabi.
21 and drinks of the wine, and is drunken, and uncovers himself in the midst of the tent.
Sa’ad da ya sha ruwan inabin ya kuwa bugu, sai ya kwanta tsirara cikin tentinsa.
22 And Ham, father of Canaan, sees the nakedness of his father, and declares to his two brothers outside.
Ham, mahaifin Kan’ana ya ga tsiraici mahaifinsa, ya kuma faɗa wa’yan’uwansa biyu a waje.
23 And Shem takes—Japheth also—the garment, and they place on the shoulder of them both, and go backward, and cover the nakedness of their father; and their faces [are] backward, and their father’s nakedness they have not seen.
Amma Shem da Yafet suka ɗauki mayafi, suka shimfiɗa a kafaɗarsu, sa’an nan suka shiga suna tafiya da baya har zuwa inda mahaifinsu yake kwance, suka rufe tsiraicinsa. Suka kau da fuskokinsu domin kada su ga tsiraicin mahaifinsu.
24 And Noah awakens from his wine, and knows that which his young son has done to him,
Sa’ad da Nuhu ya farka daga buguwarsa ya kuma gane abin da ƙarami ɗansa ya yi,
25 and says: “Cursed [is] Canaan, Servant of servants he is to his brothers.”
sai ya ce, “Kan’ana la’ananne ne, zai zama bawa mafi ƙanƙanta ga’yan’uwansa.”
26 And he says: “Blessed of my God YHWH [is] Shem, And Canaan is servant to him.
Ya kuma ce, “Albarka ta tabbata ga Ubangiji Allah na Shem! Bari Kan’ana yă zama bawan Shem.
27 God gives beauty to Japheth, And he dwells in tents of Shem, And Canaan is servant to him.”
Allah yă ƙara fāɗin ƙasar Yafet; bari Yafet yă zauna a tentunan Shem, bari kuma Kan’ana yă zama bawansa.”
28 And Noah lives after the flood three hundred and fifty years;
Bayan ambaliyar, Nuhu ya yi shekaru 350.
29 and all the days of Noah are nine hundred and fifty years, and he dies.
Gaba ɗaya dai, Nuhu ya yi shekara 950, sa’an nan ya mutu.