< Genesis 7 >

1 And YHWH says to Noah, “Come, you and all your house, into the Ark, for I have seen you [are] righteous before Me in this generation;
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
2 you take seven pairs from all the clean beasts to yourself, a male and its female; and of the beasts which are not clean—two, a male and its female;
Ka ɗauki bakwai na kowace iri tsabtaccen dabba tare da kai, namiji da ta mace, da kuma biyu na kowace dabba marar tsabta, namiji da ta mace,
3 also, seven pairs from [each] bird of the heavens, a male and a female, to keep alive seed on the face of all the earth;
da kuma bakwai na kowane iri tsuntsu, namiji da ta mace, domin a bar kowane irinsu da rai a dukan duniya.
4 for after seven more days I am sending rain on the earth [for] forty days and forty nights, and have wiped away all the substance that I have made from off the face of the ground.”
Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arba’in da dare arba’in, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
5 And Noah does according to all that YHWH has commanded him.
Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
6 And Noah [is] a son of six hundred years, and the flood of waters has been on the earth.
Nuhu yana da shekaru 106 ne sa’ad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
7 And Noah goes—and his sons, and his wife, and his sons’ wives with him—into the Ark, out of the presence of the waters of the flood;
Nuhu da matarsa da’ya’yansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
8 from the clean beast, and from the beast that [is] not clean, and from the bird, and of everything that is creeping on the ground,
Biyu-biyu daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da tsuntsaye da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa,
9 they have come to Noah two by two into the Ark, a male and a female, as God has commanded Noah.
namiji da ta mace, suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi, kamar yadda Allah ya umarce Nuhu.
10 And it comes to pass, after seven days, that waters of the flood have been on the earth.
Bayan kwana bakwai kuwa ambaliya ruwa ta sauko a bisa duniya.
11 In the six hundredth year of the life of Noah, in the second month, on the seventeenth day of the month, on this day all [the] fountains of the great deep have been broken up, and the network of the heavens has been opened,
A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe.
12 and the shower is on the earth [for] forty days and forty nights.
Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arba’in da dare arba’in.
13 On this very same day Noah, and Shem, and Ham, and Japheth, sons of Noah, and Noah’s wife, and the three wives of his sons with them, went into the Ark—
A wannan rana Nuhu tare da matarsa da’ya’yansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
14 they, and every living creature after its kind, and every beast after its kind, and every creeping thing that is creeping on the earth after its kind, and every bird after its kind (every bird, every wing).
Tare da su kuwa, akwai kowane naman jeji bisa ga irinsa, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinta, da kowane tsuntsun gida da na jeji bisa ga irinsa, da dukan abu mai fiffike.
15 And they come to Noah, into the Ark, two by two of all the flesh in which [is] a living spirit;
Biyu-biyu na dukan halittu masu numfashi suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi.
16 and they that are coming in, male and female of all flesh, have come in as God has commanded him, and YHWH closes [it] for him.
Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
17 And the flood is on the earth [for] forty days, and the waters multiply and lift up the Ark, and it is raised up from off the earth;
Kwana arba’in ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, sa’ad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
18 and the waters are mighty and multiply exceedingly on the earth; and the Ark goes on the face of the waters.
Ruwa ya taso, ya ƙaru ƙwarai a duniya, jirgin kuma ya yi ta yawo a bisa ruwa.
19 And the waters have been very, very mighty on the earth, and all the high mountains are covered which [are] under the whole heavens;
Ruwa ya ƙaru ƙwarai a duniya, ya kuma rufe dukan duwatsu masu tsawo a ƙarƙashin sammai.
20 the waters prevailed from above the mountains, and cover [them] fifteen cubits;
Ruwan ya taso ya rufe duwatsu, zurfin ruwa daga duwatsun zuwa inda jirgin yake ya fi ƙafa ashirin.
21 and all flesh expires that is moving on the earth, among bird, and among livestock, and among beast, and among every teeming thing which is teeming on the earth, and all mankind;
Kowane abu mai rai da yake tafiya a duniya ya hallaka, tsuntsaye, dabbobin gida, namun jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe a duniya, da kuma dukan mutane.
22 all in whose nostrils [is] breath of a living spirit—of all that [is] in the dry land—have died.
Kome a busasshiyar ƙasa da yake numfashi a hancinsa ya mutu.
23 And all the substance that is on the face of the ground is wiped away—from man to beast, to creeping thing, and to bird of the heavens; indeed, they are wiped away from the earth, and only Noah is left, and those who [are] with him in the Ark;
Aka kawar da kowane abu mai rai, mutane da dabbobi da halittu masu rarrafe a ƙasa, da tsuntsayen sama a doron ƙasa, duka aka kawar da su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari da waɗanda suke tare da shi a cikin jirgi.
24 and the waters are mighty on the earth [for] one hundred and fifty days.
Ruwa ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.

< Genesis 7 >

The Great Flood
The Great Flood