< Genesis 6 >

1 And it comes to pass that mankind has begun to multiply on the face of the ground, and daughters have been born to them,
Sa’ad da mutane suka fara ƙaruwa a duniya, aka kuma hahhaifi musu’ya’ya mata,
2 and the sons of God see that they, the daughters of men, [are] beautiful, and they take women for themselves of all whom they have chosen.
sai’ya’yan Allah maza suka ga cewa’ya’yan mutane mata suna da bansha’awa, sai suka zaɓi waɗanda suke so, suka aura.
3 And YHWH says, “My Spirit does not strive in man for all time, for indeed, he [is] flesh, but his days have been one hundred and twenty years.”
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ruhuna ba zai zauna a cikin mutum har abada ba, saboda shi mai mutuwa ne, kwanakinsa za su zama shekaru ɗari da arba’in ne.”
4 The giants were in the earth in those days, and even afterward, when sons of God come in to the daughters of men, and they have borne to them those who [were] the mighty from of old, the men of renown.
Nefilimawa suna nan a duniya a waɗancan kwanaki, da kuma kwanakin da suka bi baya, a sa’ad da’ya’yan Allah suka kwana da’ya’yan mutane mata, suka kuma hahhaifi musu’ya’ya. Ai, su ne jarumawan dā, mutanen da suka shahara.
5 And YHWH sees that the wickedness of man [is] abundant in the earth, and every imagination of the thoughts of his heart [is] only evil every day;
Ubangiji kuwa ya lura cewa muguntar mutum ta yi yawa a duniya, kuma kowane abin da yake tunani a zuciyarsa mugu ne kawai a kowanne lokaci.
6 and YHWH regrets that He has made man in the earth, and He grieves Himself—to His heart.
Ubangiji ya damu da ya yi mutum a duniya, abin ya zafe shi ƙwarai.
7 And YHWH says, “I wipe away man whom I have created from off the face of the ground, from man to beast, to creeping thing, and to bird of the heavens, for I have regretted that I have made them.”
Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan kawar da mutum, da dabbobi, da halittu masu rarrafe a ƙasa da kuma tsuntsayen sama waɗanda na halitta, daga doron ƙasa, saboda na damu da na yi su.”
8 And Noah found grace in the eyes of YHWH.
Amma Nuhu ya sami tagomashi a gaban Ubangiji.
9 These [are] the generations of Noah: Noah [is] a righteous man; he has been perfect among his generations; Noah has habitually walked with God.
Ga tarihin Nuhu. Nuhu mutum ne mai adalci, marar abin zargi a cikin mutanen zamaninsa, ya kuma yi tafiya tare da Allah.
10 And Noah begets three sons: Shem, Ham, and Japheth.
Nuhu yana da’ya’ya maza uku, Shem, Ham da Yafet.
11 And the earth is corrupt before God, and the earth is filled [with] violence.
Duniya dai ta lalace sosai a gaban Allah, ta kuma cika da tashin hankali.
12 And God sees the earth, and behold, it has been corrupted, for all flesh has corrupted its way on the earth.
Allah ya ga yadda duniya ta lalace, gama dukan mutane a duniya sun lalatar da rayuwarsu.
13 And God said to Noah, “An end of all flesh has come before Me, for the earth has been full of violence from their presence; and behold, I am destroying them with the earth.
Saboda haka, Allah ya ce wa Nuhu, “Zan kawo ƙarshen dukan mutane, gama saboda su duniya ta cika da tashin hankali. Lalle zan hallaka su da kuma duniya.
14 Make an ark of gopher-wood for yourself; you make rooms within the Ark, and you have covered it from inside and from outside with pitch;
Saboda haka ka yi wa kanka jirgi da katakon Saifires, ka yi ɗakuna a cikinsa, ka shafe shi da ƙaro ciki da waje.
15 and this [is] how you do it: three hundred cubits [is] the length of the Ark, fifty cubits its breadth, and thirty cubits its height;
Ga yadda za ka gina shi; jirgin zai kasance mai tsawon ƙafa 45, fāɗinsa ƙafa 75, tsayinsa kuma ƙafa 45.
16 you make a window for the Ark, and you finish it to a cubit from above; and you put the opening of the Ark in its side; you make it [with] lower, second, and third [stories].
Ka yi masa rufi, ka kuma ba da fili inci 18 tsakanin rufin a kowane gefen jirgin. Ka sa ƙofa a gefen jirgin. Ka yi shi hawa uku, ka yi ƙofa a gefe.
17 And I, behold, I am bringing in the flood of waters on the earth, to destroy from under the heavens all flesh in which [is] a living spirit; all that [is] in the earth expires.
Ga shi zan aiko da ambaliya ruwa a duniya, in hallaka dukan mai rai da yake a ƙarƙashin sama, kowace halittar da take numfashi a cikinta. Dukan abin da yake a duniya zai hallaka.
18 And I have established My covenant with you, and you have come into the Ark—you, and your sons, and your wife, and your son’s wives with you;
Amma zan kafa alkawarina da kai, kai kuma za ka shiga jirgin, kai da’ya’yanka maza da matarka da matan’ya’yanka tare da kai.
19 and of all that lives, of all flesh, you bring two from every [kind] into the Ark, to keep alive with you; they are male and female.
Za ka shigar da biyu na dukan halittu masu rai, namiji da ta mace a cikin jirgin, domin su rayu tare da kai.
20 From the bird after its kind, and from the livestock after its kind, [and] from every creeping thing of the ground after its kind, two of every [kind] they come to you, to keep alive.
Biyu na kowane irin tsuntsu, kowace irin dabba da kuma kowace irin halitta mai rarrafe a ƙasa, za su zo wurinka domin a bar su da rai.
21 And you, take for yourself from all food that is eaten; and you have gathered [it] to yourself, and it has been for you and for them for food.”
Za ka ɗauki kowane irin abinci wanda za a ci, ka adana don yă zama abincinka da nasu.”
22 And Noah does according to all that God has commanded him; so he has done.
Nuhu ya yi kome kamar yadda Allah ya umarce shi.

< Genesis 6 >

The World is Destroyed by Water
The World is Destroyed by Water