< Genesis 49 >

1 And Jacob calls to his sons and says, “Be gathered together, and I declare to you that which happens with you in the latter end of the days.
Sai Yaƙub ya kira’ya’yansa maza ya ce, “Ku tattaru don in faɗa muku abin da zai faru gare ku, a kwanaki masu zuwa.
2 Be assembled, and hear, sons of Jacob, And listen to your father Israel.
“Ku tattaru, ku saurara,’ya’yan Yaƙub maza; ku saurari mahaifinku, Isra’ila.
3 Reuben! You [are] my firstborn, My power, and beginning of my strength, The abundance of exaltation, And the abundance of strength;
“Ruben, kai ne ɗan farina, ƙarfina, alamar farko ta ƙarfina, mafi matsayi, kuma mafi iko.
4 Unstable as water, you are not abundant; For you have gone up your father’s bed; Then you have defiled [it]: He went up my couch!
Mai tumbatsa kamar ruwa, amma ba za ka ƙara zama mai daraja ba, gama ka hau gadon mahaifinka ka hau kujerata, ka kuma ƙazantar da shi.
5 Simeon and Levi [are] brothers! Instruments of violence—their espousals!
“Simeyon da Lawi’yan’uwa ne, takubansu makamai ne na tā da hankali.
6 Into their secret, do not come, O my soul! Do not be united to their assembly, O my glory; For in their anger they slew a man, And in their self-will eradicated a prince.
Ba zan shiga shawararsu ba, ba zan shiga taronsu ba, gama sun kashe maza cikin fushinsu cikin ganin dama suka kashe bijimai.
7 Cursed [is] their anger, for [it is] fierce, And their wrath, for [it is] sharp; I divide them in Jacob, And I scatter them in Israel.
La’ananne ne fushinsu, mai tsanani ne ƙwarai, hasalarsu kuwa, muguwa ce ƙwarai! Zan warwatsa su cikin Yaƙub in kuma daidaita su cikin Isra’ila.
8 Judah! Your brothers praise you! Your hand [is] on the neck of your enemies, Sons of your father bow themselves to you.
“Yahuda,’yan’uwanka za su yabe ka; hannuwanka za su kasance a wuyan abokan gābanka,’ya’yan mahaifinka maza za su rusuna maka.
9 A lion’s whelp [is] Judah, For prey, my son, you have gone up; He has bent, he has crouched as a lion, And as a lioness; who causes him to arise?
Kai ɗan zaki ne, ya Yahuda, ka dawo daga farauta, ɗana. Kamar zaki, yakan kwanta a miƙe, kamar zakanya, wa yake da ƙarfin halin tashe shi?
10 The scepter does not turn aside from Judah, And a lawgiver from between his feet, Until his Seed comes; And His [is] the obedience of peoples.
Kursiyi ba zai tashi daga Yahuda ba, ba kuwa sandan mulki daga tsakani ƙafafunsa ba, sai ya zo ga wanda yake mai shi. Biyayyar al’umma kuwa tasa ce.
11 Binding to the vine his donkey, And to the choice vine the colt of his donkey, He has washed in wine his clothing, And in the blood of grapes his covering;
Zai daure jakinsa a kuringa, aholakinsa a rassa mafi kyau; zai wanke tufafinsa cikin ruwan inabi rigunansa cikin inabi ja wur kamar jini.
12 Red [are] eyes with wine, And white [are] teeth with milk!
Idanunsa za su duhunce fiye da ruwan inabi, haƙorarsa farare kamar madara.
13 Zebulun dwells at a haven of the seas, And he [is] for a haven of ships; And his side [is] to Sidon.
“Zebulun zai zauna a bakin teku, yă zama tasar jiragen ruwa; iyakarsa za tă nausa zuwa Sidon.
14 Issachar [is] a strong donkey, Crouching between the two folds;
“Issakar doki mai ƙarfi, kwance tsakanin buhunan sirdi.
15 And he sees rest, that [it is] good, And the land, that [it is] pleasant, And he inclines his shoulder to bear, And is a servant for tribute.
Sa’ad da ya ga yadda wurin hutunsa yana da kyau da kuma daɗin da ƙasarsa take, zan tanƙware kafaɗarsa ga nauyi yă miƙa kai ga aikin dole.
16 Dan judges his people, As one of the tribes of Israel;
“Dan zai tanada adalci wa mutanensa kamar ɗaya cikin kabilan Isra’ila.
17 Dan is a serpent by the way, a viper by the path, Which is biting the horse’s heels, And its rider falls backward.
Dan zai zama maciji a gefen hanya, kububuwa a bakin hanya, da take saran ɗiɗɗigen doki domin mahayinsa yă fāɗi da baya.
18 For Your salvation I have waited, YHWH!
“Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji.
19 Gad! A troop assaults him, But he assaults last.
“Masu fashi za su fāɗa wa Gad, amma zai runtume su.
20 Out of Asher his bread [is] fat; And he gives delicacies of a king.
“Abincin Asher zai zama a wadace, zai yi tanadin abinci iri-iri da suka dace don sarki.
21 Naphtali [is] a doe sent away, Who is giving beautiful young ones.
“Naftali sakakkiyar barewa ce da take haihuwar kyawawan’ya’ya.
22 Joseph [is] a fruitful son; A fruitful son by a fountain, Daughters step over the wall;
“Yusuf kuringa ce mai ba da amfani. Kuringa mai ba da amfani kusa da rafi wadda rassanta na hawan bango.
23 And embitter him indeed, they have striven, Indeed, archers hate him;
Da ɗaci rai mahara suka fāɗa masa; suka harbe shi babu tausayi.
24 And his bow abides in strength, And strengthened are the arms of his hands By the hands of the Mighty One of Jacob, From where is a shepherd, a son of Israel.
Amma bakansa yana nan daram hannuwansa masu ƙarfi ba sa jijjiguwa saboda hannun Maɗaukaki na Yaƙub, saboda Makiyayi, Dutsen Isra’ila,
25 By the God of your father who helps you, And the Mighty One who blesses you, Blessings of the heavens from above, Blessings of the deep lying under, Blessings of breasts and womb—
saboda Allah na mahaifinka, wanda ya taimake ka, saboda Maɗaukaki, wanda yake albarkace ka da albarkar sama da take bisa albarkun zurfafa da suke ƙarƙashin ƙasa albarkun mama da kuma mahaifa.
26 Your father’s blessings have been mighty Above the blessings of my progenitors, To the limit of the perpetual heights They are for the head of Joseph, And for the crown of the one Separate [from] his brothers.
Albarkun mahaifi suna da girma fiye da albarkun daɗaɗɗun duwatsu fiye da yalwar madawwaman tuddai. Bari dukan waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin ɗan sarki a cikin’yan’uwansa.
27 Benjamin! A wolf tears; In the morning he eats prey, And at evening he apportions spoil.”
“Benyamin kyarkeci ne mai kisa; da safe yakan cinye abin da ya farauto da yamma yakan raba ganima.”
28 All these [are] the twelve tribes of Israel, and this [is] that which their father has spoken to them, and he blesses them; each according to his blessing he has blessed them.
Dukan waɗannan su ne kabilu goma sha biyu na Isra’ila, kuma abin da mahaifinsu ya faɗa musu ke nan sa’ad da ya albarkace su, yana ba kowane albarkar da ta dace da shi.
29 And he commands them and says to them, “I am being gathered to my people; bury me by my fathers, at the cave which [is] in the field of Ephron the Hittite;
Sa’an nan ya ba su waɗannan umarnai ya ce, “Ina gab da a tara ni ga mutanena. Ku binne ni tare da kakannina a kogon da yake cikin filin Efron mutumin Hitti,
30 in the cave which [is] in the field of Machpelah, which [is] on the front of Mamre, in the land of Canaan, which Abraham bought with the field from Ephron the Hittite for a possession of a burying-place;
kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre a Kan’ana, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, yă zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
31 (there they buried Abraham and his wife Sarah; there they buried Isaac and his wife Rebekah; and there I buried Leah);
A can aka binne Ibrahim da matarsa Saratu, a can aka binne Ishaku da matarsa Rebeka, a can kuma na binne Liyatu.
32 the purchase of the field and of the cave which [is] in it, [is] from sons of Heth.”
Filin tare da kogon da yake ciki, an saya daga Hittiyawa.”
33 And Jacob finishes commanding his sons, and gathers up his feet to the bed, and expires, and is gathered to his people.
Sa’ad da Yaƙub ya gama ba da umarnan ga’ya’yansa maza, sai ya ɗaga ƙafafunsa zuwa gado, ya ja numfashinsa na ƙarshe, aka kuwa tara shi ga mutanensa.

< Genesis 49 >