< Genesis 39 >
1 And Joseph has been brought down to Egypt, and Potiphar, a eunuch of Pharaoh, head of the executioners, an Egyptian man, buys him out of the hands of the Ishmaelites who have brought him there.
To, aka kai Yusuf Masar, Fotifar wani mutumin Masar wanda yake ɗaya daga cikin hafsoshin Fir’auna, shugaban masu tsaro, ya saye shi daga mutanen Ishmayel waɗanda suka kai shi can.
2 And YHWH is with Joseph, and he is a prosperous man, and he is in the house of his lord the Egyptian,
Ubangiji kuwa yana tare da Yusuf, Yusuf kuwa yi nasara, ya zauna a gidan mutumin Masar maigidansa.
3 and his lord sees that YHWH is with him, and all that he is doing YHWH is causing to prosper in his hand,
Sa’ad da maigidansa ya ga cewa Ubangiji yana tare da Yusuf, kuma cewa Ubangiji ya ba shi nasara a kome da ya yi,
4 and Joseph finds grace in his eyes and serves him, and he appoints him over his house, and all that he has he has given into his hand.
sai Yusuf ya sami tagomashi a idanunsa, ya kuma zama mai hidimarsa. Fotifar ya sa shi yă zama shugaba a gidansa, ya kuma danƙa masa kome da yake da shi.
5 And it comes to pass from the time that he has appointed him over his house, and over all that he has, that YHWH blesses the house of the Egyptian for Joseph’s sake, and the blessing of YHWH is on all that he has, in the house, and in the field;
Daga lokacin da ya sa shi shugaban gidansa da kuma a kan dukan abin da yake da shi, sai Ubangiji ya albarkaci gidan mutumin Masar saboda Yusuf. Albarkar Ubangiji tana a kan kome da Fotifar yake da shi a gida da kuma a jeji.
6 and he leaves all that he has in the hand of Joseph, and he has not known anything that he has, except the bread which he is eating. And Joseph is of a handsome form, and of a handsome appearance.
Saboda haka sai ya bar kome a ƙarƙashin kulawar Yusuf, bai dame kansa a wani abu ba sai dai abincin da yake ci. To, fa, Yusuf ƙaƙƙarfa ne, kyakkyawa kuma,
7 And it comes to pass after these things, that his lord’s wife lifts up her eyes to Joseph and says, “Lie with me”;
bayan an ɗan jima sai matar maigidansa ta fara sha’awar Yusuf, sai ta ce, “Zo ka kwana da ni!”
8 and he refuses and says to his lord’s wife, “Behold, my lord has not known what [is] with me in the house, and all that he has he has given into my hand;
Amma ya ƙi. Ya ce mata, “Ga shi kome yana a ƙarƙashina, don haka ne ma maigidana bai dami kansa da wani abu a cikin gidan nan ba; kome da ya mallaka, ya danƙa ga kulawata.
9 none is greater in this house than I, and he has not withheld from me anything, except you, because you [are] his wife; and how will I do this great evil? Then I have sinned against God.”
Babu wani da ya fi ni a wannan gida. Maigidana bai hana ni kome ba sai ke, saboda ke matarsa ce. Yaya fa, zan yi irin wannan mugun abu, in yi zunubi wa Allah?”
10 And it comes to pass at her speaking to Joseph day [by] day, that he has not listened to her, to lie near her, to be with her;
Ko da yake ta yi ta yin wa Yusuf maganar kowace rana, amma ya ƙi yă kwana da ita, ko ma yă zauna da ita.
11 and it comes to pass about this day, that he goes into the house to do his work, and there is none of the men of the house there in the house,
Wata rana, ya shiga cikin gida don yă yi ayyukansa, ba wani daga cikin bayin gidan da yake ciki.
12 and she catches him by his garment, saying, “Lie with me”; and he leaves his garment in her hand, and flees, and goes outside.
Sai ta cafke shi a riga, ta ce, “Zo ka kwana da ni!” Amma ya bar rigarsa a hannunta, ya gudu ya fita daga gidan.
13 And it comes to pass, when she sees that he has left his garment in her hand, and flees outside,
Sa’ad da ta ga ya bar rigarsa a hannunta ya gudu ya fita daga gidan,
14 that she calls for the men of her house, and speaks to them, saying, “See, he has brought a man to us, a Hebrew, to play with us; he has come in to me, to lie with me, and I call with a loud voice,
sai ta kira bayin gidan ta ce musu, “Duba, an kawo mana wannan mutumin Ibraniyawa don yă ci mutuncinmu! Ya zo nan don yă kwana da ni, amma na yi ihu.
15 and it comes to pass, when he hears that I have lifted up my voice and call, that he leaves his garment near me, and flees, and goes outside.”
Sa’ad da ya ji na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
16 And she places his garment near her, until the coming in of his lord to his house.
Ta ajiye rigar kusa da ita sai da maigidansa ya dawo gida.
17 And she speaks to him according to these words, saying, “The Hebrew servant whom you have brought to us, has come in to me to play with me;
Sa’an nan ta faɗa masa wannan labari, “Mutumin Ibraniyawan, bawan da ka kawo mana, ya zo wurina don yă ci mutuncina.
18 and it comes to pass, when I lift my voice and call, that he leaves his garment near me, and flees outside.”
Amma da zarar na yi ihu neman taimako, sai ya bar rigarsa kusa da ni, ya gudu ya fita daga gida.”
19 And it comes to pass, when his lord hears the words of his wife, which she has spoken to him, saying, “According to these things has your servant done to me,” that his anger burns;
Sa’ad da maigidansa ya ji labarin da matarsa ta faɗa masa cewa, “Ga yadda bawanka ya yi da ni,” sai ya husata.
20 and Joseph’s lord takes him, and puts him to the round-house, a place where the king’s prisoners [are] bound; and he is there in the round-house.
Maigidan Yusuf ya ɗauke shi ya sa a kurkuku, wurin da ake tsare’yan kurkukun sarki. Amma yayinda Yusuf yake can a cikin kurkuku,
21 And YHWH is with Joseph, and stretches out kindness to him, and puts his grace in the eyes of the chief of the round-house;
Ubangiji ya kasance tare da shi; ya nuna masa alheri, ya kuma sa ya sami tagomashi a idanun mai gadin kurkukun.
22 and the chief of the round-house gives into the hand of Joseph all the prisoners who [are] in the round-house, and of all that they are doing there, he has been doer;
Saboda haka mai gadin ya sa Yusuf ya zama shugaban dukan waɗanda aka tsare a kurkukun, Yusuf ne kuma yake lura da dukan abin da ake yi a can.
23 the chief of the round-house does not see anything under his hand, because YHWH [is] with him, and that which he is doing YHWH is causing to prosper.
Mai gadin ba ya sa kansa game da kome da yake ƙarƙashin kulawar Yusuf, gama Ubangiji yana tare da Yusuf, ya kuma ba shi nasara a cikin dukan abin da ya yi.