< Genesis 31 >

1 And he hears the words of Laban’s sons, saying, “Jacob has taken all that our father has; indeed, from that which our father has, he has made all this glory”;
Yaƙub ya ji cewa’ya’ya Laban mazan suna cewa, “Yaƙub ya kwashe dukan abin da mahaifinmu yake da shi, ya kuma sami dukan wannan arziki daga abin da yake na mahaifinmu.”
2 and Jacob sees the face of Laban, and behold, it is not with him as before.
Yaƙub kuma ya lura cewa halin Laban gare shi ya canja ba kamar yadda yake a dā ba.
3 And YHWH says to Jacob, “Return to the land of your fathers, and to your family, and I am with you.”
Sai Ubangiji ya ce wa Yaƙub, “Koma ƙasar kakanninka da kuma danginka, zan kuwa kasance tare da kai.”
4 And Jacob sends and calls for Rachel and for Leah to the field to his flock;
Saboda haka Yaƙub ya aika a ce wa Rahila da Liyatu su zo jeji inda garkunan suke.
5 and says to them, “I am beholding your father’s face—that it is not toward me as before, and the God of my father has been with me,
Sai ya ce musu, “Na ga cewa halin mahaifinku gare ni ba kamar yadda dā yake ba, amma Allah na mahaifina yana tare da ni.
6 and you have known that with all my power I have served your father,
Kun san cewa na yi aiki wa mahaifinku da dukan ƙarfina,
7 and your father has played on me, and has changed my hire ten times; and God has not permitted him to do evil with me.
duk da haka mahaifinku ya cuce ni ta wurin sauya albashina sau goma. Amma dai, Allah bai yardar masa yă yi mini lahani ba.
8 If he says thus: The speckled are your hire, then all the flock bore speckled ones; and if he says thus: The striped are your hire, then all the flock bore striped;
In ya ce, ‘Dabbare-dabbare ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi dabbare-dabbare, in kuma ya ce, ‘Masu zāne-zāne ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi ƙananan masu zāne-zāne.
9 and God takes away the substance of your father, and gives to me.
Ta haka Allah ya kwashe dabbobin mahaifinku ya ba ni.
10 And it comes to pass at the time of the flock conceiving, that I lift up my eyes and see in a dream, and behold, the male goats, which are going up on the flock, [are] striped, speckled, and spotted;
“A lokacin ɗaukar cikin garken, na taɓa yin mafarki inda na ga bunsuran da suke barbara da garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne.
11 and the Messenger of God says to me in the dream, Jacob, and I say, Here I [am].
Sai mala’ikan Allah ya ce mini a mafarkin, ‘Yaƙub.’ Sai na amsa na ce, ‘Ga ni.’
12 And He says, Now lift up your eyes and see [that] all the male goats which are going up on the flock [are] striped, speckled, and spotted, for I have seen all that Laban is doing to you;
Ya ce, ‘Ɗaga idanunka ka gani, dukan bunsuran da suke hawan garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne, gama na ga dukan abin da Laban yake yin maka.
13 I [am] the God of Bethel where you have anointed a standing pillar, where you have vowed a vow to me; now, arise, go out from this land, and return to the land of your birth.”
Ni ne Allah na Betel, inda ka zuba wa al’amudi mai, da kuma inda ka yi mini alkawari. Yanzu ka bar wannan ƙasa nan take, ka koma ƙasarka ta ainihi.’”
14 And Rachel answers—Leah also—and says to him, “Have we yet a portion and inheritance in the house of our father?
Sai Rahila da Liyatu suka amsa suka ce, “Muna da wani rabo a gādon kayan mahaifinmu ne?
15 Have we not been reckoned strangers to him? For he has sold us, and he also utterly consumes our money;
Ba kamar baƙi ne yake ɗaukarmu ba? Ba sayar da mu kaɗai ya yi ba, har ma ya yi amfani da abin da aka biya saboda mu.
16 for all the wealth which God has taken away from our father, it [is] ours, and our children’s; and now, all that God has said to you—do.”
Tabbatacce dukan dukiyar da Allah ya kwashe daga mahaifinmu ya zama namu da’ya’yanmu. Saboda haka ka yi duk abin da Allah ya faɗa maka.”
17 And Jacob rises, and lifts up his sons and his wives on the camels,
Sa’an nan Yaƙub ya sa’ya’yansa da matansa a kan raƙuma,
18 and leads all his livestock, and all his substance which he has acquired, the livestock of his getting, which he has acquired in Padan-Aram, to go to his father Isaac, to the land of Canaan.
ya kuma kora dukan dabbobinsa, suka ja gabansa, tare da dukan abubuwan da ya samu a Faddan Aram, don su tafi wurin mahaifinsa Ishaku a ƙasar Kan’ana.
19 And Laban has gone to shear his flock, and Rachel steals the teraphim which her father has;
Sa’ad da Laban ya tafi don askin tumakinsa, sai Rahila ta sace gumakan gidan mahaifinta.
20 and Jacob deceives the heart of Laban the Aramean, because he has not declared to him that he is fleeing;
Yaƙub kuwa ya ruɗe Laban mutumin Aram da bai sanar da shi zai gudu ba.
21 and he flees, he and all that he has, and rises, and passes over the River, and sets his face [toward] the Mount of Gilead.
Saboda haka ya gudu da dukan abin da ya mallaka, ya ƙetare Kogi, ya nufi yankin tuddan Gileyad.
22 And it is told to Laban on the third day that Jacob has fled,
A rana ta uku, sai aka faɗa wa Laban cewa Yaƙub ya gudu.
23 and he takes his brothers with him, and pursues after him a journey of seven days, and overtakes him in the Mount of Gilead.
Sai Laban ya ɗauki danginsa tare da shi, ya bi bayan Yaƙub har kwana bakwai, ya kuma same shi a yankin tuddan Gileyad.
24 And God comes to Laban the Aramean in a dream of the night and says to him, “Take heed to yourself lest you speak with Jacob from good to evil.”
Sai Allah ya bayyana ga Laban mutumin Aram a mafarki da dare, ya ce masa, “Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu, ko mai kyau ko marar kyau.”
25 And Laban overtakes Jacob; and Jacob has fixed his tent in the mountain; and Laban with his brothers have fixed [theirs] in the Mount of Gilead.
Yaƙub ya riga ya kafa tentinsa a yankin tuddan Gileyad sa’ad da Laban ya same shi. Laban da danginsa suka kafa sansani a can su ma.
26 And Laban says to Jacob, “What have you done that you deceive my heart, and lead away my daughters as captives of the sword?
Sai Laban ya ce wa Yaƙub, “Me ke nan ka yi? Ka ruɗe ni, ka kuma ɗauki’ya’yana mata kamar kamammun yaƙi.
27 Why have you hidden yourself to flee, and deceive me, and have not declared to me, and I send you away with joy and with songs, with tambourine and with harp,
Me ya sa ka gudu a ɓoye ka kuma ruɗe ni? Me ya sa ba ka faɗa mini don in sallame ka da farin ciki da waƙoƙi haɗe da kiɗin ganguna da garayu ba?
28 and have not permitted me to kiss my sons and my daughters? Now you have acted foolishly in doing [so];
Ba ka ma bari in sumbaci jikokina da’ya’yana mata in yi musu bankwana ba. Ka yi wauta.
29 my hand is to God to do evil with you, but the God of your father last night has spoken to me, saying, Take heed to yourself from speaking with Jacob from good to evil.
Ina da iko in cuce ka; amma jiya da dare Allahn mahaifinka ya faɗa mini, ‘Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu ko mai kyau ko marar kyau.’
30 And now, you have certainly gone, because you have been very desirous for the house of your father; why have you stolen my gods?”
Yanzu ka gudu domin kana marmari komawa gidan mahaifinka. Amma don me ka sace mini gumakana?”
31 And Jacob answers and says to Laban, “Because I was afraid, for I said, Lest you violently take away your daughters from me;
Yaƙub ya amsa wa Laban, “Na ji tsoro ne, domin na yi tsammani za ka ƙwace’ya’yanka mata daga gare ni ƙarfi da yaji.
32 with whomsoever you find your gods—he must not live; before our brothers discern for yourself what [is] with me, and take to yourself”: and Jacob has not known that Rachel has stolen them.
Amma in ka sami wani wanda yake da gumakanka, ba zai rayu ba. Kai da kanka ka duba a gaban danginmu, ko akwai wani abin da yake naka a nan tare da ni; in ka gani, ka ɗauka.” Yaƙub dai bai san cewa Rahila ta sace gumakan ba.
33 And Laban goes into the tent of Jacob, and into the tent of Leah, and into the tent of the two handmaidens, and has not found; and he goes out from the tent of Leah, and goes into the tent of Rachel.
Saboda haka Laban ya shiga tentin Yaƙub, ya shiga tentin Liyatu da kuma tentuna matan nan biyu bayi, amma bai sami kome ba. Bayan ya fita daga tentin Liyatu, sai ya shiga tentin Rahila.
34 And Rachel has taken the teraphim, and puts them in the furniture of the camel, and sits on them; and Laban feels all the tent, and has not found;
Rahila fa ta kwashe gumakan gidan ta sa su cikin sirdin raƙumi, ta kuma zauna a kansu. Laban ya bincika cikin kowane abu a tentin amma bai sami kome ba.
35 and she says to her father, “Let it not be displeasing in the eyes of my lord that I am not able to rise at your presence, for the way of women [is] on me”; and he searches, and has not found the teraphim.
Sai Rahila ta ce wa mahaifinta, “Kada ka yi fushi, ranka yă daɗe da ban tashi tsaye a gabanka ba; gama ina al’adar mata ne.” Saboda haka ya bincika amma bai sami gumakan gidan ba.
36 And it is displeasing to Jacob, and he strives with Laban; and Jacob answers and says to Laban, “What [is] my transgression? What my sin, that you have burned after me?
Yaƙub ya fusata, ya kuma yi wa Laban faɗa. Ya tambayi Laban, “Mene ne laifina? Wanda zunubi na yi da kake farautata?
37 For you have felt all my vessels: what have you found of all the vessels of your house? Set here before my brothers, and your brothers, and they decide between us both.
Yanzu da ka bincika dukan kayayyakina, me ka samu da yake na gidanka? Kawo shi nan a gaban danginka da kuma dangina, bari su zama alƙali tsakaninmu biyu.
38 These twenty years I [am] with you: your ewes and your female goats have not miscarried, and the rams of your flock I have not eaten;
“Na kasance tare da kai shekaru ashirin. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuwa ci raguna daga garkunanka ba.
39 the torn I have not brought to you—I repay it—from my hand you seek it; I have been deceived by day, and I have been deceived by night;
Ban kawo dabbobinka da namun jeji suka yayyaga; na kuma ɗauki hasarar ba? Ka nemi in biya dukan abin da aka sace da rana ko da dare.
40 I have been [thus]: drought has consumed me in the day, and frost by night, and my sleep wanders from my eyes.
Yanayin da na kasance ke nan, da rana na sha zafin rana da dare kuma na sha sanyi, ga rashin barci.
41 This [is] to me twenty years in your house: I have served you fourteen years for your two daughters, and six years for your flock; and you change my hire ten times;
Haka ya kasance shekaru ashirin da na yi a gidanka. Na yi maka aiki shekaru goma sha huɗu domin’ya’yanka mata biyu, na kuma yi shekaru shida domin garkunanka, ka kuma canja albashina sau goma.
42 unless the God of my father, the God of Abraham, and the Fear of Isaac, had been for me, surely now you had sent me away empty; God has seen my affliction and the labor of my hands, and reproves last night.”
Da ba don Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim da kuma Tsoron Ishaku ya kasance tare da ni ba, tabbatacce da ka sallame ni hannu wofi. Amma Allah ya ga wahalata da famar hannuwana, ya kuwa tsawata maka da dare jiya.”
43 And Laban answers and says to Jacob, “The daughters [are] my daughters, and the sons my sons, and the flock my flock, and all that you are seeing [is] mine; and to my daughters—what do I to these today, or to their sons whom they have born?
Laban ya amsa wa Yaƙub, “Matan,’ya’yana ne,’ya’yansu,’ya’yana ne, garkunan kuma garkunana ne. Dukan abin da kake gani, nawa ne. Duk da haka me zan yi a rana ta yau ga waɗannan’ya’yana mata, ko kuma ga’ya’yan da suka haifa?
44 And now, come, let us make a covenant, I and you, and it has been for a witness between me and you.”
Zo, bari mu ƙulla yarjejjeniya, da kai da ni, bari kuma ta kasance shaida a tsakaninmu.”
45 And Jacob takes a stone, and lifts it up [for] a standing pillar;
Saboda haka Yaƙub ya ɗauki dutse ya kafa yă zama al’amudi.
46 and Jacob says to his brothers, “Gather stones,” and they take stones, and make a heap; and they eat there on the heap;
Ya ce wa danginsa. “Ku tattara waɗansu duwatsu.” Sai suka kwashe duwatsu suka tsiba, suka kuwa ci abinci a can kusa da tsibin.
47 and Laban calls it Jegar-Sahadutha; and Jacob has called it Galeed.
Laban ya sa masa suna Yegar Sahaduta, Yaƙub kuwa ya kira shi Galeyed.
48 And Laban says, “This heap [is] witness between me and you today”; therefore has he called its name Galeed;
Laban ya ce, “Wannan tsibi, shi ne shaida tsakaninka da ni a yau.” Shi ya sa aka kira shi Galeyed.
49 Mizpah also, for he said, “YHWH watches between me and you, for we are hidden from one another;
Aka kuma kira shi Mizfa, domin ya ce, “Ubangiji yă sa ido tsakanin ni da kai sa’ad da muka rabu da juna.
50 if you afflict my daughters, or take wives beside my daughters—there is no man with us—see, God [is] witness between me and you.”
Laban ya ce in ka wulaƙanta’ya’yana mata, ko ka auri waɗansu mata ban da’ya’yana mata, ko da yake babu wani da yake tare da mu, ka tuna cewa Allah shi ne shaida tsakaninka da ni.”
51 And Laban says to Jacob, “Behold, this heap, and behold, the standing pillar which I have cast between me and you;
Laban ya kuma ce wa Yaƙub, “Ga wannan tsibi, ga kuma wannan al’amudin da na kafa tsakaninka da ni.
52 this heap [is] witness, and the standing pillar [is] witness, that I do not pass over this heap to you, and that you do not pass over this heap and this standing pillar to me—for evil;
Wannan tsibin shi ne shaida, wannan al’amudi kuma shaida ne, cewa ba zan tsallake wannan tsibi zuwa gefenka don in cuce ka ba, kai kuma ba za ka tsallake wannan tsibi da al’amudi zuwa gefena don ka cuce ni ba.
53 the God of Abraham and the God of Nahor, judges between us—the God of their father,” and Jacob swears by the Fear of his father Isaac.
Bari Allah na Ibrahim da Allah na Nahor, Allah na iyayensu, yă zama alƙali tsakaninmu.” Saboda haka Yaƙub ya yi rantsuwa da sunan Tsoron mahaifinsa Ishaku.
54 And Jacob sacrifices a sacrifice on the mountain, and calls to his brothers to eat bread, and they eat bread, and lodge on the mountain;
Ya miƙa hadaya a can a ƙasar tudu, ya kuma gayyaci danginsa zuwa wurin cin abinci. Bayan suka ci, sai suka kwana a can.
55 and Laban rises early in the morning, and kisses his sons and his daughters, and blesses them; and Laban goes on, and turns back to his place.
Da sassafe kashegari sai Laban ya sumbaci jikokinsa da’ya’yansa mata, ya sa musu albarka. Sa’an nan ya yi bankwana da su, ya koma gida.

< Genesis 31 >